KAMA DA WANE....(Completed)

By Seemahwrites

13.2K 1.8K 210

even though they look alike that doesn't mean they should have same goals, their life is filled with regret... More

chapter 1
chapter 2
chapter 3
chapter 4
chapter 5
chapter 6
chapter 7
chapter 8
chapter 9
chapter 10
chapter 12
chapter 11
chapter 13
chapter 14
chapter 15
chapter 16
chapter 17
chapter 18
chapter 19
chapter 20
chapter 21
chapter 22
chapter 23
Apology
chapter 24
chapter 25
chapter 26
chapter 27
chapter 28
chapter 29
chapter 30
chapter 31
chapter 32
chapter 33
chapter 35
chapter 36
chapter 37
chapter 38
chapter 39
chapter 40
chapter 41
chapter 42
chapter 43
chapter 44
chapter 45
chapter 46
chapter 47
chapter 48
chapter 49
FINAL
Trailer

chapter 34

221 39 10
By Seemahwrites

(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)
🖤💙🖤💙🖤💙🖤💙🖤
👩🏻KAMA DA WANE......
BATA WANE👩🏻‍🦱
💙🖤💙🖤💙🖤💙🖤💙

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/

Blog : prowritersnovels.blogspot.com

Follow me on Wattpad @ayeeshatmuhd

*Na*
*UMMU NAJMA*
marubuciyar *HAR ABADA*

*DEDICATED TO*
*AMMYN KHAIRAT(golden girl)*
*AND RUKAYYA IKRA(ummu sultan)*

*Musmayya, Ummi Zariya, Aisha bello, Hussaina Maijama'a and Fatima Muhammad*
*Wannan shafin naku ne Kuna sharhi Yanda ya Kamata💞 GRACIAS🙏🏼❤️*

34👯
I..I mean a matsayin 'dan uwan ki kaman Yanda kike son Idris Nima kina so na haka?"

Murmushi tayi ta qara jaddada mishi " I don't like you ya Sa'ood"

Wani Abu kaman mashi yaji ya cakke shi a zuciyar sa, a wannan matsayin ma Haleesa ta qishi Ina ace ya bude Mata sirrin zuciyar shi? Bazai iya jure rejection daga wurin ta ba he better hide his feelings kada sabon dake tsakanin su ma ya rasa shi,

"Amman daga jiya zuwa yau na fara canza ra'ayi na a kanka, maybe idan na ci gaba da zama tare dakai zan tantance whether to like you or not, Amman bani da tabbacin hakan gaskiya"

Ya bude Baki zaiyi magana waiter ya qaraso da abincin su ya jere musu shi, ganin kaman Yana bata mishi lokaci Kuma ya lura rabin attention dinshi na wurin Leesa yasa shi saurin bata rai a kausashe yace

"Kai malam kayi sauri ka Gama abinda ke gaban ka ka bamu wuri" kafin ya bar wurin har Leesa ta saka spoon ta fara cin abincin ta,

Wannan lokacin a nitse take ci Dan Bata son abinda zai Bata kwalliyan ta, a tsanake Sa'ood yake qare Mata kallo she is eating like a queen today, dukda kiciniyar tattare hannun rigan ta da takeyi Amman Saida ya samu Daman Shiga cikin bowl din porridge din da take sha,

"Ya Rabb!! Duk iya qoqarina Saida wannan abun ya Bata min Kaya gashi ni bazan ci ba"

Miqa Mata nashi plate din yayi Wanda yake dauke da kalan abinci daban harda plate din da suke side duk ya tura Mata gaban ta yace "ga wa'innan kici" Yana gyara zama hade da tallafe fuskar shi da tafukan hannayen shi biyu, kallo kawai yake bin ta dashi ta zamo mishi kamar TV komai na Haleesa birgeshi yakeyi sai faman daddage Baki takeyi tana saka abincin saman harshen ta kada ya Bata Mata Jan baki,

A haka ta Gama cin abincin ta Sa'ood baici komai ba Bayan kallon ta ya saka ta wanke hannun rigan ta da ya baci a sink sannan suka bar restaurant din suka sake komawa mall din da suka fito lokacin an Gama packaging kayan su ya bada card dinshi suka cire kudin su sannan aka saka musu a mota sukayi gaba,

Nan ma wani hanya daban suka sake daukan ba Wanda zai maida su asibiti ba, cikin NASARAWA GRA suka Isa gate din wani qaton gida ganin haduwan shi yasa shakku ya darsu a zuciyar Leesa sosai 'kode da gaska sayar dani zaiyi?' ta tambayi kanta tana duba reaction din Sa'ood,

Fuskar shi a sake take Yana marmarin haduwa da abokin shi ya tura a sanar ma maigidan zuwan sa, Leesa kuwa a tunanin ta murnar zai Saida ita yakeyi a take cikin ta ya fara kuka ta tsorata sosai ta rasa qoqarin guduwa zatayi ne ko Kuma tambayar sad abinda ya kawo su zatayi? A haka har mutumin ya fito da kansa kafin ya qaraso Sa'ood ya fita daga cikin motar suna dariyan farinciki sukayi buddy's hug,

Mutumin ne ya fara cewa "welcome back SD we miss you so much"

Murmushi yayi yace "na sani barrister it's been long since we've met, I missed your company Yaya labarin future KD governor?"

" Hmm al'amarin Ameer sai a hankali yaje ya daura ma Kashi abunda yafi qarfin sa"

" Ko Kuma mace ta daura Masa abinda yafi qarfin sa ba?" Sa'ood ya fada Yana dariya "ai nasan Yanda take kurari Yana wani na qarya idan ya Shiga hannun mace wallahi sai yayi sanyi"

" Wa yace maka? Matar da washe garin auren ya sake ta!!"

Zaro Ido Sa'ood yayi cike da mamaki yace "subhanallah! A Kan wani dalili? Me tayi Masa da ya dauki wannan danyen hukuncin haka?"

" Haba SD kaman bakasan waye Ameer ba? Babu abinda baiwar Allah tayi mishi akan wannan mummunar aqida da familyn shi suka ginu a Kai yasa ya lalata rayuwar 'yar mutane, yanzu da kada na cika ka da surutu mu Shiga ciki sai mu qarasa tattaunawa"

" Tare da baquwa nake tana mota bari nayi Mata magana ta fito ka Shiga zamu biyo ka a baya"

" Oh! My! God!!! Babban tuzuru yau anyi abun Kai, kace Kuna qwato sunan ku ka santamo baby? gaskiya bana za'ayi ruwan sama da qanqara Bari na qarasa in gaisa da amaryan tamu na kwashi karama" ya fada Yana qarasa jikin windown Leesa ba tare da ya tsaya Jin ta bakin Sa'ood ba,

Dan dafa saman windown yayi Yana kallon Leesa dake ciki ita Kuma hankalin ta Yana Kan Sa'ood dake qarasowa inda suke,

"Amarya Ina wuni"

Kaman an shuka dusa haka Leesa ta zauna bata juyo ba balle yasa ran zata bashi amsa hasali ma Bata San da ita yakeyi ba, juyawa wurin Sa'ood yayi yace "SD ko ba ita bace amaryan?"

"Itace Mana me ka gani?"
" Kurma ce? Naga Ina ta magana Bata kulani ba"

Kyalkyalewa da dariya Sa'ood yayi, yasan wannan kadan ne daga shu'umancin Leesa taji shi Kuma taqi amsawa, dafa shi yayi yace "barrister Sarwa ce fa"

"What!!! Like seriously??? I mean yaushe kuka same su? A Ina? Ta Yaya?"

" Ikon Allah kawai, Amman munsha wahala sosai saidai alhamdulillah buqata ya biya"

Cikin tausayawa yace "Allah sarki! Amman Yaya maman su? Ta samu waraka ko? Gaskiya na tayaku farinciki lokaci Daya komai sun dawo dai_dai Allah ya dada kiyayewa"

" Ameen barrister, yanzu dai qafa kawai ya rage Mata Amman Baki da sauran gabobin jikin ta alhamdulillah tana iya amfani dasu"

" Wacece Daya a cikin motar? Saleeha ce ko?"

" No Sa'eed yayi min snatching din Saleeha wannan Haleesa ce, ka sake Mata magana maybe idan taga dama zata kula ka"

Sake komawa jikin windown ta yayi Yana fadin " kace madam din tamu Yar rigima ce" ya sunkuya daidai Yanda zai ganta da kyau yace "Ina wuni aunty Haleesa"

Saurin Juyowa tayi tana kallon shi, wannan magidancin ne zoqai_zoqai dashi zai Kira ta aunty? Amman ya ma Raina Mata hankali wani ma yaji Haka idan Bai ganta ba zaiyi tunanin wata tsohuwa ce tukuf, a taqaice ta amsa mishi da "wa'alaikumus Salam"

Dan Sosa qeya yayi Yana dariya sai yanzu ya Gane inda kwafsa yace "Assalamu alaikum, sorry for the misconception sunana Adam ni abokin yayanki ne if you don't mind ki fito mu Shiga ciki I will like to introduce you to my wife"

A hankali ta zuro qafarta Bayan ta bude qofar ta fito, suka qarasa inda Sa'ood yake tsaye tare da Adam sannan yayi gaba ya barta ita da Sa'ood sun biyo shi a baya har cikin gidan,

Matar shi da tuntuni ya fada Mata Sa'ood yazo ta zauna a kusa dan tarban shi ne ta miqe ganin sun shigo tana musu barka da zuwa,
"Honey look who's here" Adam ya fada Yana nuna Haleesa,

Kallon rashin sani matar tabi Haleesa dashi tana tambayar Sa'ood "who is she?"

"It's Sarwa, wannan itace babban Haleesa"

Kare bakinta matan tayi da hannun ta with amusement tana kallon Haleesa "innalillahi wa Inna ilaihirraji'un I can't believe it, yaushe aka same su? A Ina?"

" Kinaga Nima dai tambayar da nayi Masa Kenan Amman har yanzu ban samu amsa ba tukunna, yanzu dai ki Kira yara suzo su gaida uncle dinsu, Bari muje parlor na"

Yaja Sa'ood suka tafi yabar Haleesa wurin matar Adam, Babu laifi Leesa ta sake suna 'dan taba Hira Amman duk Yanda ta kada ta rawa taqi taci komai dan already a qoshe take, tayi excusing kanta sannan ta kaima Sa'ood abinci da drinks ta tura yaran ta uku duka maza suka gaida shi sannan suka fito suka Basu wuri,

**********

"Wai nikam kayi min bayani please SD ta Yaya akayi Sa'ood ya kwace Saleeha daga wurinka Bayan kowa yasan takace?"

Matsowa kusa dashi Sa'ood yayi yana kallon cikin idanun shi looking serious yace "ba abinda ya kawo ni ba Kenan Adam, nazo ne Akan maganar hospital kasan cewa a qarqashin Mailafiya hospital akayi registering Mailafiya orphanage Kuma duk wani riba da aka samu a asibitin wurin yake tafiya da kudin ake ciyar da marayun ake Basu ilimi da wajen kwana,

har yanzu Basu bamu asibitin ba saboda ba'a gano ainihin Wanda ya shigo da qwayoyin Nan ba Dan sun bincika sun tabbatar ba Sa'eed bane, dukda an kulle shi a prison na tsawon lokaci idan ba sun gano ainihin Wanda yayi wannan aikin ba bazasu taba dawo Mana da asibitin Nan ba and muna buqatar ceto rayuwar marayun na we really need our orphanage back,

Kai kadai ne nake da yaqinin zaka it taimaka min ta wannan fannin Adam ka taimaka kayi wani abu a wanke sunan asibitin mu idan har ba'a bude shi ba duk Yanda mukayi HAR ABADA ba zasu taba bamu orphanage ba, nayi maka alqawarin daga Kan million 50 har zuwa million 200 zan ita bayarwa Akan case dinnan just help me please na roqe ka"

Furzar da numfashi Adam yayi ya jiqa maqoshin shi da ruwa sannan ya fara kwararo ma Sa'ood bayanai,

" Bani buqatar kudin ka Sa'ood idan na karba zan bawa abokantaka kunya, saidai kasan wannan case din ba qaramin bane Kuma ba Mai sauqi bane, it was a clean crime har gobe zanci gaba da fada maka wani na kusa daku sosai ne yayi wannan abun mutumin da yasan sirrin ku Kuma yasan komai Akan kadarorin ku dukda nasan ba yarda zakayi dani ba Amman in har kana son NASARA cikin wannan case din Dole ka amince da haka saboda Babu wani mistake da akayi Babu wani clue da muka samu ko kadan,

Babu record din shigo da magani Babu CCTV footage din lokacin da aka shigar dashi office din Sa'eed aka chanza Masa da Wanda ya ajiye zaiyi amfani da su so believe me na kusa daku ne yayi wannan aikin and idan har bamu Kama shi ba bazamu samu Mailafiya hospital ya dawo hannun mu ba,

Saidai idan zamu bi hanya ta biyu and it is very dangerous and hard, idan har muka saka gwamnati a ciki zata yaqi kanta da kanta ta gyara sunan ku ammafa zata iya amfani daku wurin biyan nata buqatun and duk lokacin da Abu yaje ya dawo Kuma Zaku fada ciki, idan gwamnati tayi rashin adalci you will also be blamed for it hatsarin San Kuma shine sunan ku zai baci a Karo na biyu Wanda a wannan lokacin bazamu ita gyara Muku ba duk Yanda mukayi kuwa, mutane zasu tsane ku za'ayi Muku kallon mugayen mutane Wanda idan ba'ayi sa'a ba bama zaman Kano kadai ba zaman Nigeria ma said ya gagare ku wallahi,

So kaje kayi shawaran idan zakayi qoqarin ka gano Mai laifin ne ko zakuyi taking risk din aiki da gwamnati? It's left to you idan kayi shawaran ka dawo ka sanar dani sai na fara aiki na".............🧚

#vote
#share
#comment

Continue Reading

You'll Also Like

450K 32.2K 43
α€•α€²α€•α€Όα€―α€α€Ία€žα€Šα€Ία€„α€•α€Όα€°α€Έα€”α€²α€· α€†α€­α€―α€€α€Ία€€α€¬α€Έα€†α€›α€¬α€„α€œα€°α€Έα€α€­α€―α€·α€›α€²α€· story α€œα€±α€Έα€α€…α€Ία€•α€―α€’α€Ί
5K 442 40
love is a strange feeling but also a very strong connection that will either be your strength or your weakness it all depends on who you've to be wit...
Ice Cold By m

General Fiction

2.2M 83.6K 49
[boyxboy] Wren Ridley is always two steps ahead of everyone, or so he thinks. His life seems out of his control when he starts having feelings for so...
226K 16.7K 21
Avantika Aadish Rajawat Aadi, with his fiery nature, adds intensity and excitement to their relationship, igniting a spark in Avni. Avni, like the ca...