KAMA DA WANE....(Completed)

By Seemahwrites

13.2K 1.8K 210

even though they look alike that doesn't mean they should have same goals, their life is filled with regret... More

chapter 1
chapter 2
chapter 3
chapter 4
chapter 5
chapter 6
chapter 7
chapter 8
chapter 9
chapter 10
chapter 12
chapter 13
chapter 14
chapter 15
chapter 16
chapter 17
chapter 18
chapter 19
chapter 20
chapter 21
chapter 22
chapter 23
Apology
chapter 24
chapter 25
chapter 26
chapter 27
chapter 28
chapter 29
chapter 30
chapter 31
chapter 32
chapter 33
chapter 34
chapter 35
chapter 36
chapter 37
chapter 38
chapter 39
chapter 40
chapter 41
chapter 42
chapter 43
chapter 44
chapter 45
chapter 46
chapter 47
chapter 48
chapter 49
FINAL
Trailer

chapter 11

236 34 0
By Seemahwrites

(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)
🖤💙🖤💙🖤💙🖤💙🖤
👩🏻KAMA DA WANE......
BATA WANE👩🏻‍🦱
💙🖤💙🖤💙🖤💙🖤💙

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/

Follow me on Wattpad @ayeeshatmuhd

*Na*
*UMMU NAJMA*
marubuciyar *HAR ABADA*

*DEDICATED TO*
*AMMYN KHAIRAT(golden girl)*
*AND RUKAYYA IKRA(ummu sultan)*

*Happy confusion clique*🗣️🗣️🗣️

Your attention is needed here🤣🤣🤣

Haleesa=Leesa=eldest=Mai bindiga
Saleeha=Salee=youngest=burin Sa'ood Kuma matar Sa'eed
NO MORE CONFUSION PLEASE 🙏🏼😅

Wannan shafin naku ne
*Sis bahijja*
*Farida magaji*
*Fatima*
*Hauwa baba tunde*
*Maryam milo*
And finally my little sis *khadeejah Muhammad (mmn jawad) love you all😘

11👯
8:02pm

Da motan Nabeela da na Idris akayi Kai amarya irin mutanen da ta gani tare da amaryan ya Bata mamaki, ya Sa'eed a wani irin gida ne ya nemi aure haka? Taso ta fada ma Idris abubuwan da ta gani Amman ba zataso wani Abu ya sake samun Sa'eed ba, tasan mijinta qiris yake jira ya tada rigima.

Tunda aka daura aure Zarah ta qule a cikin daki tana risgan kuka gashi Sa'eed bayi Nan Islam Kuma tana wurin Nabeela, al'amin kawai aka Bari da aikin rarrashi,

Bata taba tsammanin zata tsaya takara da wata mace a zuciyar Sa'eed ba ko lokacin da yake da arziqi Amman saboda wulaqanci shine Sa'eed zai Mata kishiya a cikin talauci, Daman rayuwar Yaya aka qare manage suke yi yanzu tsiya zai qaru a Kan na baya,

har qawayen amarya suka Gama Shan zaman su suka watse babu ango babu abokan shi, tun Salee na baza idanuwa har barci ya dauke ta tana zaune tana faman tsiyayar hawaye, Allah yasa Sa'eed ba wani abu bane ya samu Sa'eed din gashi Bata da waya ballantana taji ko Yana lafiya,

Zarah na labe a jikin window tana jiran taga wucewar Sa'eed dakin amarya Amman shiru har qarfe 1 idonta biyu ta kasa samun nutsuwar barci, tana so ta tabbatar ma kanta yaufa Sa'eed ya zamo ba nata ita kadai ba, yau idan Sa'eed ya shigo gida dakin wata zai kwana ba dakin ta ba,

Ganin shirun yayi yawa yasa ta dauki waya ta Kira shi, kaman jira take bugu daya ya dauka, rasa me zata fada mishi tayi shima sai ya tsinci kanshi da Jin nauyin ta yasan rashin dawowar shi gida ne yasa ta Kira shi,

Tattaro Dan qarfin guiwar ta tayi tana qoqarin yakice kishin sa daga cikin ranta, murya a sanyaye tace
"Ya Sa'eed Yaya har yanzu baka dawo gida ba? Ka San amarya tana jiran ka ko?"

Cikin wani irin murya yace "I'm sorry mi Alma uzuri ne ya taso min ki Bata haquri please sai gobe da safe zan dawo"

" Ina dai lafiya ko?"
"Kada ki damu Lafiya qlau"

Sauqe numfashi tayi tace " to Allah ya kaimu goben, bye"

" bye, love you"

"Uhm_hmm" kawai tace ta katse Kiran, tana Jin tausayin Salee cikin ranta, ta San da ciwo ace ango baizo wurin amarya a Daren auren su ba, ta rufe qofarta ta kwanta, da qyar ta samu barci yayi awon gaba da ita.

**********
Nabeela ce tsaye a jikin mirror sanye da kayan barci tana tace gashin kanta, Idris na zaune ya jingina kanshi da gado Yana kallon bayanta,

"Reina Yaya kike ganin yanzu idan na Kira Sa'ood na fada mishi Sa'eed yayi aure?" Dan murmushi ya sake yace "I can't imagine irin tashi hankalin da gaba dayan su nasan sai ya saka bindiga a Kan amaryan Nan ya harbe ta"

Da sauri Nabeela ta ajiye comb din hannun ta ta qaraso kusa dashi ta tsunguna hawaye na taruwa a idanun ta
"Dan girman Allah kada kayi Haka Amor, Mun samu zaman kwanciyar hankali Bayan lokaci mai tsawo Dan Allah kayi haquri haka Nan Sa'eed ya riga yayi maka alqawarin zai dawo da Sarwa cikin qanqanin lokaci ka daga Masa qafa"

" Amman Baki da wayo beelat tsawon shekaru 17 Kenan Sa'eed na Mana wannan alqawarin har yau Bai cika shi ba, Baki ganin wannan wata dama ce da muka samu da zamu saka shi yayi abinda muke so"

Girgiza Kai tayi hawayen dake idon ta suna samun damar sauqowa Kan cheeks dinta
"No please don't do this ka daga mishi qafa zuwa Nan gaba na yarda zaka iya fada mishi zancen auren Amman ba yanzu ba nasan ko baka fada mishi ba zai sani ,ko badan shi ba ka tausaya ma matar da ya aura 'yar qaramace sosai wallahi"

" Shikkenan Sa'eed yaci darajan ki Amman Nan da wata biyu idan Bai kawo min Sarwa ba hmm babu Wanda ya Isa ya cire shi daga matsalan da zan saka shi"

Da sauri ta gyada Kai hade da fadin "eh na yarda" tana da hope kafin lokacin hala Sa'eed ya samo Sarwa,idanma bai samo ta ba zata sake dakatar dashi a Kan mugun nufin shi tunda bayi iya komai sai ya sanar da ita,

**********

Washe gari asuba Salee ta farka hawayen fuskar ta ya Gama bushewa, tashi tayi ta kunna wutan dakin tana kallin fuskar ta a jikin mirror,

Jan qafarta tayi ta shiga toilet tayi alwala sannan ta fiddo da darduma daga cikin akwatin ta tayi sallah, tana idarwa ta wanko toilet dinta ta gyara dakin ta Tass sannan ta fita waje,

Cikin sa'a akwai ruwa a famfo ta cika komai sannan wanke tsakar gidan ta daura musu ruwan wanka a murhun gawayi, har tayi wanka ta shirya tayi breakfast Zarah na sharar bacci da yaran ta, Basu fito ba sai 9 lokacin Salee ta gama Gama hada breakfast, har yanzu tana cikin damuwar abin da ya Hana Sa'eed dawowa gida tun jiya,

Zarah na farkawa taga gida ba a atmospheren da ta 'yan biki suka barshi jiya ba, fitowa tayi ta bude food plask din da tagani a bakin qofar ta taci Karo da lafiyayyen abinci, bata Gama mamaki ba Salee ta qaraso wurin da take tsaye fuska a sake tace
"Ina kwana aunty Zarah"

Kallon sama da qasa tayi Mata babu laifi tayi kyau cikin sabuwar atamfar ta dinkin ya zauna dass a jikin ta, tabe Baki tayi tace

"Ashe Daman karuwai sun it's gaisuwa?"

Sosai Salee taji zafin kalaman ta Amman sai ta share ta nuna Mata food plask din da ta ajiye Mata abinci tace
"Momyn al'amin ga abincin ki"

Tsungunawa tayi ta dauka tace
"Na gode Amman ba sai kin nuna zaqewa da yawa ba, ki haqura na Baki girkin Mana Amman kinyi caraf kin dauka ke bakisan mace tana da kunya bane? Ko dayake karuwai Basu dashi, nasan kinzo tambayan angon naki ne ko juya baizo ya raya daren ku ba right? Ki qara haquri fa idan ya dawo sai kin gaji dashi, ohh Ashe Bai Kamata na Fadi haka ba tunda already Kun riga Kun Saba"

Duk Yanda Salee tayi qoqarin shanye kukanta kasawa tayi Maganganun Zarah sunyi Mata tsauri da yawa Ashe abun da ke cikin gidan Sa'eed dinta Kenan tun daga day one ta fara cin Karo da bacin rai,

Shaida Tasha kukan ta ta qoshi sannan ta wanke fuskarta ta sake fitowa ta samu Zarah ta shimfida taburma a tsakar gidan ita da yaranta suna kwasan girki,

Haka ta zauna tana kallon su har suka Gama ta dauki Islam tayi Mata wanka ta tura ta wurin Zarah ta shiryata, al'amin ma har toilet takai mishi ruwa ta saka musu wani abincin daban a lunch box, tana Jin zagin kasuwan da Zarah take mata amman ta basar ta dauki mayafinta ta raka yaran qofar gida,

Daidai zasu fita saiga Sa'eed Yana shigowa, tsayawa yayi Yana kallon su yaran suka qaraso suka rungume shi, peck sukayi mishi a cheeks suka Kama hannun juna tare dayi musu sallama suka wace makaranta,

Murmushi tayi tadan duqa kadan tace "Ina kwana ya Sa'eed barka da dawowa" ta miqa hannun ta ta karbi manyan laidojin hannun shi,

Sosai yaji kunyar ta ya dauka zatayi fushi sai Kuma yaga akasin haka, lallai Salee yarinya ce tunda Bata gane girman laifin da yayi Mata ba,

Dan Sosa qeya yayi yace
"I'm sorry babe jiya banzo gareki ba kiyi haquri uzuri ne ya taso min Amman insha Allah....."

Bata Bari ya qarasa magana ba tayi saurin shigewa ciki harda hadawa da Dan gudun ta, Sa'eed Saida ya dara Dan shi babu Wani abu da ya fada na Jin kunya a Nan, bin bayanta yayi fuskar shi dauke da murmushi aikuwa shigan su sai a idon Zarah tana jabe a wurin da Salee ta barta gaban kwanon abincin da sunfi 30 minutes da cinyewa Amman kawar dashi daga wurin ya gagara,

Kallon su gaba Daya tayi taja tsaki ta tashi ta wuce ciki, ganin haka yasa jikin Salee yayi sanyi batason tana ganin bacin ran Zarah batasan dalili ba,

Ratsawa tayi ta gefen Sa'eed zata wuce ya riqo hannun ta Yana Jin laushin sa cikin nashi kaman auduga ga yatsunta sirara kaurin hannun ta Bai wuce na al'amin ba ya ayyana a ranshi,

Dawowa gaban shi tayi tana kallon shi, ya miqo Mata Daya daga cikin laidan hannun shi
"Gashi babe bashin kazar ki da kike bi na, na biyaki ko?"

Girgiza Kai tayi tace "no na yafe babu bashi a tsakanin mu ka kaiwa momyn al'amin ta raba sai a bani kaso na"

" Aa babe wannan naki ne ke kadai suna ga nasu Nan"

Karba tayi tana murna duk da ba wani 'da'data da qasa Naman yayi ba,

"Na gode sosai Allah ya qara arziqi Mai albarka"

Lumshe idanu yayi ranshi na mishi Dadi ya amsa da "ameeen babe, Bari na sallami auntyn ki sai muzo muyi magana, yanzu kije ki huta nasan ki gaji"

Gyada Kai tayi ta juya shiga dakinta shi Kuma ya wuce dakin Zarah, ta fito daga wanka Kenan daure da farin towel a jikinta yace ta zauna suyi magana, batayi musu ba zauna tana sauraron shi,

"Mi Alma please ki bani hadin Kai wurin tabbatar da zaman lafiya a cikin gidan Nan Kinga kece shugaba dan Haka Ina matuqar buqatar taimakon ki, ki zauna da yarinyan Nan lafiya Ina da tabbacin zatayi respecting dinki don nasan irin macen da na aura"

" To angon jaririya, gashi ya Sa'ood baiyi ba Kai kayi, ko kunya fa bakaji Wai da sunan kayi aure kaje ka auro 'yar yarinyan da Bata wuce sa'an Sarwa ba har zakace nayi zauna lafiya da ita, to Ina abun tashin hankali a Nan da 'yar ciki na kake son nayi kishi Allah ya tsare ni"

" Itadin Sarwa ce Zarah" ya Fadi haka Yana so yaga reaction dinta,

Da sauri ta miqe ta dafe qirji tace "miel Sarwa fa kace! To Ina Yar uwar ta? Arziqin mu ya dawo wayyo Dadi alhamdulillah"

" Ke nifa ba haka nake nufi ba, I mean da ace ita sarwan ce Zaki zauna da ita?"

" Mtsww kaji wani abun haushi, wallahi na dauka da gaske kakeyi har na fara ganin kaina cikin mailafiya mansion ga danqara danqaran motoci sai Wanda na zaba, maids ta ko Ina sunamin hidima tufafi kuwa idan yayi qasa da 50k bani sakawa, gaskiya ka jamin Rai Kuma ban yafe ba"

Qaramin murmushi Sa'eed yayi dama yasan Zarah ba matan sirri bace, ko mutuwa zaiyi idan tasan su Salee be Sarwa sai fallasa,

Haka suka qare maganar rabi tsiya da rashin arziqi ya koma wurin Salee itama yayi Mata Bata jawabin wanda nusar da ita tayi biyayya ma Zarah da haqurin zama da ita yafi yawa Dan shima Bai tsallake uqubar ta ba,

Bai hadasu ya musu tare bane saboda yasan zaman shi da Salee ba Mai daure wa bane so no need ayi wani rabon kwana and stuff's,

Yana shiga wankanta gyare dakin shi Tass kafin ya fito ta fesa air freshener ta fita shirya abincin Rana Dan already 12 ta wuce, Sa'eed da kanshi ya fita samo Mata Dan aika ta bashi saqon duk abinda za'a siyo Mata tana jin kaman tayi abincin Rana Kuma kaman ta Bari Dan har yanzu maganar da Zarah ta fada Mata da Rana Yana Dan damun ta............🧚

*Manage,😁*

*Ummu najma ce😘*

Continue Reading

You'll Also Like

444K 16.2K 192
Won Yoo-ha, a trainee unfairly deprived of the opportunity to appear on a survival program scheduled to hit the jackpot, became a failure of an idol...
8.6K 974 10
The heart is a confusing, altering thing no state of bliss lasts forever and no state of pain does either. A nice easy going girl, a temperamental a...
33.6K 2.9K 27
ထချစ်ရူးနှင့်တော်၀င်ပန်း
590K 27.1K 42
Needs editing [ the destiny series #1] 𝑻𝒉𝒆 𝒇𝒂𝒕𝒆 𝒑𝒖𝒔𝒉𝒆𝒅 π’•π’‰π’†π’Ž 𝒂𝒑𝒂𝒓𝒕 𝒃𝒖𝒕 π’…π’†π’”π’•π’Šπ’π’š π’‚π’ˆπ’‚π’Šπ’ 𝒑𝒖𝒍𝒍𝒆𝒅 π’•π’‰π’†π’Ž π’•π’π’ˆ...