Zumuncin Zamani

De Nazeefah381

7K 517 25

Labari mai saka rauni a zuciya bisa yarda aka yi watsi da zumunci aka martaba ku'di fiye da zumunci ta yarda... Mais

1
2
3
4
5
6
7
8
9
10
11
11
12
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31
32
33
34
35
36
38
39
40
41
42
43
44
45
46
47
48
49
50
51
52

13

110 8 0
De Nazeefah381

Zumuncin Zamani (New update)

Na

Nazeefah Sabo Nashe.

08033748387.

Typing: fadima Sabi'u Dankaka

(Allah ya baki abinda kike nema duniya da lahira.)

Zuciyar Hisham ta sake k'ullewa da tarin bak'in cikin maganganun Inna falmata. ya ilahi, ayi mutane sam babu Allah a ransu? Dubi dai yanzu duk wadatar da Allah ya bata ammn hangen abun wani take yi, ya kuwa za a yi imani ya ratsa mutum, shi yasa kullum mutane ba sa godewa Allah in dai za ka hango na samanka, yanzu falmata nawa ta fi wadatar amman hangen na wani take.
Ganin Hisham ya yi tsit, hakan ya sa Inna falmata ta gyara zamanta tana kallonsa, tace "Hisham kayi shiru?"
D'ago kai ya yi yace "Bakomai Inna dama wata magana ce ta kawo ni."
Inna falmata tace "to ina  jin ka,ga me da me?"
Hisham ya saki ajiyar zuciya ya ce da man mun yi magana da Abba akan mata biyu nake son na aura.to sam Abba  ya k'i ya amince min, kuma na riga na yi alk'awari  a gidan su yarinayr, ba nason na zama k'aramin mutum."
Inna falmata ta gyara zama kafin ta ce "Gaskiya babu dad'i, tunda da dai har ka yi magana a gidansu, ita kuma yarinyar wane ne babanta?"

Hisham ya d'an zunkud'a kafin ya ce "To kin ga Inna abinda nake gaya wa Abba kenan, sam ya kasa fahimta, bafa wata ba ce yarinayr, Saudat ce y'ar gidan Abba  Mustafa"

Da sauri Inna ta zaro ido ta ce " " 'yar gidan mustapha?  Lallai ubanka ya k'i amince maka, wa  zai so ya had'a jininsa da Jinin tsiya? Kai ma dai ka zama sakarai, bar ganin ana maka murna ka taso da nasibi wallahi idan ka had'a jini da jinin Mustafa tsaf za su tsiyataka, don tsiya a jininsu ta ke. Kuma tilas Babanka ya hanaka ana murna ka rab'i arziki, kana  rab'o wa kanka tsiya?"
Hisham mikewa kawai ya yi ba tare da ya sake cewa kanzil ba illa, "Sai anjima"

Falmata ta watsa masa wani kallo, sannan ta ce mu jima da yawa,banda abin ma yaran zamani ina tsiya ina y'ay'an Mustafa da talauci ya yi wa katutu?
Hisham ko da ya shiga mota sunkuyar da kansa ya yi a kan sitiyarin Yana mamakin mutane masu k'in jinin Y'an uwansu saboda talauci. Direct gidan wani abokinsa ya wuce wanda ake kira nejeeb ya yi sa'a kuwa ya same shi a gidan.
Cikin farin ciki najeeb ya tare shi. Bayan  son gaisa Hisham ya Sanar dashi halin da yake ciki, najeeb tsit ya yi yana son gano wa abokin nasa mafita, duk da shi yana ganin wautar abokin nasa na zab'ar d'iyar talakawa, akan y'ar  sanata, a sanatocin ma babanta shine senate president, tabbas abokin nasa yana shirin tafka babban kuskure, sai  dai hausawaa sun ce daidan wani karkataccen Wani, tunanin hakan yasa ya dubi abokin nasa ya ce "ina ganin fareeda zaka samu ka sanar da ita halin da kake ciki, kasan mata da tausayi musamman idan suna sonka,sai ka ga ta tausaya maka har ta lallaba iyayenka su amince da batun."

A take Hisham ya amince da batun abokin nasa. bayan sunyi sallama ya karkata akalar motarsa, zuwa gidan su Fareeda da yake nassarawa G.R.A Kano
Yana danna lambar wayarta bugu d'aya ta d'auka cikin tattausan kalami ya ce, "Ran gimbiya ya dad'e ga ni a k'ofar gidanku"
Mamaki ya kama fareeda don ta dad'e ba ta ji kalamii irin wannan daga gareshi ba. Sai  dai ta danne mamakin nata ta hanyar sauya mayafi ta fice harabar gidan.


A cikin motar ta same shi bayan sun gaisa ta ce "ya aka yi? Na  ga kana ta doka murmushi?"Hisham ya d'an lumshe ido ya ce, "Ina  kallo tsananin kyan da uwargidata tayine."
Fareeda ta saki murmushi jin dad'i ta ce "Uwargida kuma amarya ba, ka san ina da tsananin kishi, don haka daga ni babu K'ari"
Dam!! Dam!! K'irjin Hisham ya buga, don kuwa bai hango dacewa a wajen ba, cikin k'arfin hali ya daure ya ce "a haba ai yanzu mata kansu ya waye, sun daina wannan tsananin kishi........

"Ban dani Hisham, don kuwa zafin kishina ya wuce duk yadda kake zato." fareeda ta fad'a a hassale "Don kuwa wallahi da mace ta yi kishi dani zata gwammace ta fad'a rijiya ko ta rungumi transformers......

Jin abinda tace yasa Hisham zare ido had'e da cewa, "kin san abin da kike cewa kuwa Fareeda?  amman dai ina so furuncin ki yazama gangan. don kuwa rana d'aya zan aure ku ku biyu."
Fareeda ta yi murmushi, lokaci d'aya kuma ta sha mur had'e da fad'in, "Bari Hisham a rayuwa ta ina son kowanne irin wasa amman ban da na kishiya."
Hisham ma ya gintse fuskarsa, kafin ya ce. "Da gaske nake fareeda, babu batun wasa rana d'aya zan aure ku ke da saudat......
 
"Dakata Hisham!! Wallahi indai har da gaske kake na hak'ura da aurenka ko kai ne autan maza....... Daga haka ta bud'e k'ofar mota ko waiwayonsa ba ta yi ba.
Zuciyarsa ta yi zafi, ya rintse idonsa yana fadin,"Oh God " menene mafita kuma?"

Fareeda tana shiga gida ta sakawa mahaifiyar ta kuka, hakan ya rud'a mamin tata, ta shiga tambayar ta dalilin kukanta.
Fareeda ta rattabo mata bayani.
Zuciyar mahaifiyarta ta  tunzira , ta ce  "share hawayan ki, shi d'in banza. ai wallahi ya yi kad'an ya wulak'anta ki  yanzu zan Yi waya gidansu na ji dalilin wananan tozarcin. naji.shin ,da saninsu ko babu?"
Wayarta ta D'auka ta danna lambar mahaifiyar Hisham, bugu d'aya Hajiya laraba ta d'auka.

Hajiya sa,a cikin kausshiyar murya ta ce "laraba Sak'on da ku ka turo Hisham da shi ya isar mana, sai dai ina so ki sani ban zauna da kishiya ba, d'iyarta baza ta yi kishi ba, don haka idan Hisham autan maza ne fareeda ta bar auren sa.......
Laraba ta zaro ido tace "Hajiya sa'a wallahi saurare ni don Allah, sam ba mu muka turo Hisham ba,kiyi hak'uri zan samu mahaifinsa da maganar."
Sam Hajiya sa'a ba ta saurare ta ba illa D'uf  data yi ta kashe wayar, cikin jin zafin Hajiya laraba
Ita kuwa Hajiya laraba tana ajiye wayar tagumi ta zuba tana tunanin irin asarar da Hisham ya ke Shirin janyo musu, amman kuwa tabbas zai zo ya same ta,ba ta yi kasa a gwiwa ba ta kira mahaifinasa ta sanar dashi abunda yake faruwa
Tsam mahaifinasa ya yi da ransa yace," barni da dan banxan yaro,zan dawo daga kadunan gobe _ gobe kuma sai na yi abinda saii ya gwammace bai ce yana son d'iyar Mustafa mai k'ashin tsiya ba daga haka ya Kashe wayar cikin matuk'ar zafin rai Ita ma hajiya laraban zurfin tunani ta afka tare da hasasho irin hukuncin da za ta yi wa zuriyar Mustafa ma'kurar basu k'yale Hisham ba. Ta zabga tsaki,ta rasa har yaushe ta yi sake da Hisham ya fara zuwa gidan Mustafa.

Ko da ya dawo da daddre sai da ya isa sashen sashen mahaifiyarsa don cin abincin dare, wani banzan kallo ta watso masa tare da shigewa D'akinta . Hakan ya tabbatar masa ta samu labarin abinda ya aikata a gidan su Fareeda, sai dai shi ko a jikinsa Allah yasa ma a fasa auren, sam ba shi da damuwa.

Kashegari Alhaji Hamza ya dawo ko zama bai yi ba ya danna kiran wayar Hisham, cikin sakin fuska ya amsa wayar tawa, Alhaji Hamza yace, "ka zo ina son ganin ka yanzu."
Daman yana cikin gidan,don haka babu bata lokaci yaxo, abban nasa da walwala fal a fuskarsa ya tare shi yana fadin angon mata biyu Hisham ya sunkuyar da kansa don yana zaton abban nasa gatse yake masa, ga mamakinsa sai yaji abban nasa yace,tashi muje gidan mustapha a tare na ji ba a yi wa yarinyar miji ba.

Cikin matuk'ar mamaki Hajiya laraba ta kalle shi had'e da cewa, "Alhaji daure masa gindi zaka yi? Ya d'an  d'aga mata hannu, "Ba ruwanki mustapha jininane, kuma ba zan k'i jinina ba saboda wani, muje Hisham."
Hisham kuwa dadi ne ya lullube shi ya ayyana a ransa Allah kenan,Al_hakimu dubi dai yardda cikin hikimarsa ya shirya mahaifinasa a rana daya lokacin daya wa ke da wannan ikon banda Allah.

A kofar gidan Abba mustapha Hisham yayi parking din motarsa cikin zakwadi da tsananin murna ya fito ya zira kansa cikin zauren gidan Abba mustapha,da fara'a fal a fuskarsa ya shigaa gidan sauda da take gefe tana yanka alaiyahu tayi saurin d'agawa ta haska shi da wadatattun idanunta cikin sakin murmushi.shima murmushi ya sakar mata, sananan ya ce" Abba na nan kuwa sauda?"

Ta d'aga kai cikin karassahin murya, yana nan yau gaba d'aya bai fita ba, saboda baya jin dad'i, Hisham ya ce  Ashsha Allah ya sauwake, ga shi da abbana muke ya xo ne a kan maganar auren mu umman tana ciki? Sauda ta d'aga kai tace "tana ciki bara nayi mata magana"
Kafin ta shigaa cikin d'akin Umma ta fito da fara'arta ta ce "Hisham ashe kai ne a tafe."
Durkusawa yayi ya gaishe ta, sannan ya sake gyran zamansa had'e da cewa "ashe abba bai ji dad'i ba?" Umma ta gyad'a kai tace. "Wallahi jikin nasa yau ya tashi babu dad'i, kasan abinka da mai ciwon hawan jini yau da lafiya gobe babu."
Hisham yace "haka ne daman Abbane yake son ganinsa yazo ne akan maganar mu da Sauda.
Umma ta gyad'a kai tace "To Allah yasa lafiya da fatan dai ba wata matsalar ba ce ta faru?" Hisham ya girgiza kai had'e da cewa "babu komai In sha Allah sai alheri. Ya xo ne su tattauna maganar auren."
Cikin farin ciki umma ta ce kai Masha Allahu bara nayi masa magana.

Daidai lokacin yayyen sauda suka shigo gaba d'ayansu,suka mimmik'a wa Hisham hannu. Abba ko da ba ya jin dad'i haka ya k'ok'arta ya fito, bayan Umma ta isar da sak'on ana son ganinsa
Cikin walwala ya fito yana duban dan Dan uwansa Alhaji Hamza, cikin sakakkiyar fuska yace, Hisham maza kace ya shigo mana, ya zaa bar shi a tsaye?"
Hisham ya juya shima cike da walwala.
Abba mustapha ya saka umma ta Malala tabarma a tsakar gidan, ya zauna ya jingina da bango don kam matuka da gaske ba ya jin dadin jikinsa.
Fuskar alhji hamza a hade ya shiga gidan yana karewa gidan kallo, da alamar raini k'arara a fuskarsa gaba d'aya jikinsu ya yi sanyi,amman hakan bai hana Abba mustapha yi masa tarbar mutunci ba, ya mik'a masa hannu had'e da yi masa iso kan tabarmar.

Alhaji Hamza bai ko dube shi ba, ya sake tamke fuska a karo na biyu, ya saki murmushin da kai tsaye za a iya kiransa na rainin hankali, ya kai dubansa kan Hisham,  "Allah wadaran naka ya lalace, yanzu Hisham duk tarin baiwar nasibin da Allah ya yi maka na katarin samun arxiki a nan kake so ka ce min kana neman aure? to me na sama ya ci balle ya bai wa na k'asa ya juya kan Mustafa yace, Ina so ka ji ni da kyau Mustafa babu Hisham babu y'arka, ban ga yarda had'in zai had'u ba, abin da hausawa suke cewa HAD'iN GAMBIZA kun ga yaro ya taso da arzikinsa kun bi kun makale masa saboda ku kassara shi. Wallahi d'ana yafi k'arfin ku me Hisham zai yi da jinin tsiya.idan ma kwad'ayin abin hannusa kuke bud'e kunnunwanka da kyau Hisham kaji daga yau ficikarka ta k'ara shigowa gidan nan Allah ya isa ban yafe ba,duk wahalar dana yi maka tun kana cikin Uwarka." Hisham dake gefe ya rintse idanunsa sai ga kwalla na tsiyaya.

Shi kuwa Abba mustapha murmushi ya saki, ya ce "duk me ya yi zafi haka? ina ganin idan har an yi abin a hankali, komai zai zo da sauki, Hisham dai d'an kane babu wanda zai yi maka iko dashi kana da ikon saka shi ka kuma hana shi da alfarmar annabi saudat dai ko ta rasa mijin aure ba zata aure shi ba sai dai ina so ka ja masa kunne shi ma babu shi babu ita..... 
Hisham ya girgiza kai yana duban mahaifinasa ya ce "Abba bai dace ba abinda ka yi, sam bai dace ba wallahi."
Wani kallo ya bi shi da shi kafin ya girgiza kai "ko d'aya ban yi mamakin furucinka ba nasan ba haka aka barka ba, sai dai ina so ka sani, ko dame mustapha yake takama wallahi na fi shi, mu zuba ni da shi shege ka fasa. Hisham ya sake bud'e baki ya ce Abba....

Ya Harare shi " mutumin banza nuna min matsayitan mutane sun fi ni a wajen ka. Wallahi idan ba ka yi da gaske ba sai na tsine maka akan wad'annan matsiyatan tashi ka fice mu tafi, kuma ka kaddara ka yi wa gidan nan kallon karshe,don ko da wasa ka tako kafarka zuwa gidan nan wallahi ba zan yafe maka ba."
Cikin tashin hankali Hisham ya mik'e ya fice yana bin bayansa Yana sake jaddada, "Matsiyata kawai"
Suna fita umman sauda ta bi bayansu ta shige d'akin mijinta. Sauda kuwa hawaye kawai take. mahamud ya dube ta yana girgixa kai a zuciyar sa yana ayyana tabbas talauci bai yi ba . A hankali ya ce saudat ki yi shiru, Abu d'aya za kiyi ki cire soyayyar Hisham daga ranki . ki bawa mahaifinsa kunya shi ne ki ka cika 'ya'."

Continue lendo

Você também vai gostar

11.5K 1.5K 61
Kaddara! Mece ce ita? Yaya rayuwar yarinya mai karancin shekaru za ta kasance a lokacin da ta tsinci kanta cikin mummunar kaddara, irin kaddarar da b...
One More Mistake | ✓ De ⭑

Ficção Adolescente

205K 7K 66
When Thea Nightingale enters her senior year she didn't expect to see the boy who had died over a month ago in the same room as her, also the hatred...
82.9K 4.4K 59
labarine da ya kunshi rikitacciyar soyayya da ramuwa,Wanda masoyan suna son juna Amman sun kasa gasganta haka Wanda har suka kusa su rasa juna hmmmm...
3.2K 275 25
bana nada bayani kawai ki bibiyeni