RAYUWAR JIDDAH ✔

נכתב על ידי DielaIbrahim

10.3K 856 277

RAYUWAR JIDDAH Labari ne akan rayuwar wata ya' mace mai suna Hauwa'u Jiddah. Let embark on the journey togeth... עוד

01
02
03
04
05
06
07
08
09
10
11
12
13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31
32
33
35
36
37
38
AL'ADARMU
UMMI KWARAS
AL'ADARMU
AL'ADARMU

34

178 14 6
נכתב על ידי DielaIbrahim

RAYUWAR JIDDAH
Part 2/14
ALKALAMIN DIELAIBRAHIM ✍️

____________________________________
❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️

***********

Ranar da kyar aka iya fitar dani daga dakin" sai da nayi kwana biyu Ina kuka" babu yadda Ummi da Momma basuyi dani ba akan nayi shuru amma na kiyin shuru" shin da wanne zanji da rashin kafata guda ko kuma da rashin lafiyar mijinah"Wanda bakomai ke damunsa ba sai neuronal disorder, cuta ce wanda yake taba kwakwalwa sannan ya sanya kokwanto acikin brain din mutum, sai dai kuma shi Hafiz cutar ta kamashi da yawa wanda ko farfad'owa baiyi ba tun bayan da aka kawo shi asibitin ya farka so daya daga nan kuma ya sake komawa bacci wanda har yau bai tashi ba" kuma likitoci sun tabbatar da yana numfashi" am helpless and no one will understand how am feeling awannan lokacin aka soma shirye shiryen fitar da Yayanah waje domin ai masa aiki a brain dinshi ya dawo daidai kwatsam sai aka wayi gari da wata cuta wai ita Covid-19" aka sanya lock down mai tsanani sannan jiragen dake zuwa kasashe daban daban suma an hana su wannan aikin sakamakon kulle ko wacce kasa da akayi saboda wannan disease din"

Tunda naga haka nace da granny da Daddy da su barni naje asibiti na rinka kwana da Yayanah" Kuma suka amince" dukdama dokar da aka sanya a KADUNA STATE  yayi tsanani amma da taimakon Yaya Faisal da Abba na muka samu aka kaini hospital din " granny ta tafi gida don dama ita ke kwana dashi"

Sabuwar RAYUWA  na fara nida Yayanah wanda har lokacin bai farfad'o ba, kullin zan tashi tsakar dare nai ta sallar nafila Ina rokon Allah daya bashi lafiya, abinci ko wani abu ba damuwa bane saboda komai akwai a hospital din kitchen na kusa damu don haka time din abinci nayi zasu kawo min abinda na zaba, dukdama ba wani ci nakeyi sosai ba, ban kuma damu da rashin ganin family ba saboda nasan ansanya lockdown" akwana atashi yau har munyi wata d'ai d'ai d'ai har wata biyar a hospital" kullin bani da aiki sai dai na tsura masa idanu Ina imagining ranar da zai bude idanuwansa"

3rd September, 2020

Abbana ya tashi da wani ciwo wanda yake numfashi sama sama, Ina hospital aka kirani aka sanar dani sosai na tsorata naji Ina son ganin Abbana, NAFHospital aka kawo shi, likitoci suna ta faman gwaje gwaje atunaninsu corona ce amma da aka duba sai aka ga ba ita bace,  amma sun kasa gane takamai mai abinda ke damun Abbana ga numfashin sa yaki dawo wa daidai"
Kwanan biyu kacal a hospital akwana na uku ne Ina ward din mijina, Abbana yasa aka kira masa ni" naje na ganshi Ina kuka yana kuka Ina tayi masa addu'a" Abba yace Alhamdulillah Allah na gode maka dayasa na aurar da 'ya'ya na biyu da raina" ya dube ni ya rike hannayena da karfinsa yace Mamana ki kula da mijinki" kuma ki kula da Ummin ki" Ya kara cewa Mamana ki bautawa Allah mahallincinki kamar kina ganinsa kuma ki kiyaye fushin Ubangijin ki" kibi mijin ki sau da kafa" insha Allah zai samu lafiya kinji mamana"

Kuka ya kufce min nace Abba inshaAllah zan yi abinda kace Amma kaima zaka samu sauki da yardar Allah kaji Abba"
Abba cikin Jin ciwo ya girgiza kai ya kalli Ummi wacce take gefensa idanuwanta sunyi jazir yace a'a Ummi addu'a zakiyi min awannan lokacin ita nafi bukata akan komai" ya kara cewa Ummi ki kula da kanki kuma ki kula da amanar yaran mu" Ummi tace haba Abba kayi shuru mana kana ta wasu irin maganganu haka" kowa awajan ya tausaya wa halin da Abba yake ciki, lokaci  daya ya rame, yai fari" Saifullah shi yake tayi masa Addu'o'i a ruwa yana bashi yana sha" Muhammad kuma yana gefensa yana karanto masa Addu'o'i shi kuma Abba yana kamawa tsahon minti arba'in mukayi a haka mun kasa yin nisa dashi" gashi ciwon sai karuwa yakeyi nikam ma kuka kawai nake ta famanyi toh naga fah an sanya masa drip tun safe amma ruwan baya tafiya, baya shiga jikinshi ko kadan" ga jikin yayi sanyi kararau sai zufa daya keto masa a goshi" muna zazzaune misalin karfe hudu 4 Abba yace Ummi kiyimin alwala zanyi sallah"
Ummi tai masa alwala su Yaya muhammad suka fita don zuwa masallaci, ni da Momma muka fita muma waje zamuyi sallah bamu jima ba muka dawo dakin sai muka iske Ummi na kuka ta rirrike Abba wanda ya sassadare yana ta mimmikewa idanuwansa kuma suna kara kallon sama" Ummi nata yimasa kalmatusshahada shi kuma yana amsawa irin a zabure" Momma ce tai saurin rufe min idanu sannan muka juya muka bar dakin Ina cewa momma barni naje wajan Abba mana bakiga baya da lafiya ba, zan mishi addu'a ne" amma Momma tai kaman bata ji ni ba a waje muka zauna gashi kafa daya gareni dana shiga ciki da gudu"

Muna nan zaune su Yaya muhammad suka dawo, Momma bata hana su shiga ciki ba" haka kawai naji kaman wani abu ya faru da Abba don haka sai nayi kokarin tashi na rike stick dina Ina kokarin shiga ward din"

Momma kaman ta rike ni Amma sai ta kyaleni don itama ta shiga cikin wani hali" Ina shiga dakin naga an rufe fuskar Abba da farin bedsheets , Yaya Muhammad ya rungume Ummi yana comforting dinta Yaya  Faisal ya rungume Ya Saifullah yana bashi hakuri"

Na karasa wajan Ina cewa what's going on Ummi Abba ya kwanta bacci ne, Jikin yayi sauki koh Alhamdulillah dama nayi masa Addu'a yanzunnan Abba Allah ya kara maka lafiya" ganin kowa yai min shuru babu mai cewa uffan hakan yasa na samu waje kusa da Abba na zauna, daga bisani naga suna fita daya bayan daya" ban damu ba kawai na kwanta akan kirjin Abba Ina maida numfashi har kusan rabin awa kafin naga an shigo da wani gadon karfe wanda ake daura mattatu (gawa)
Ina kallo aka yi kama kama aka daura Abba, sai alokacin na fara wani kalan tunani amma nai saurin korar tunanin acikin rai na" kafin mubar asibitin Daddy, Mom da granny suka zo, nidai Momma tace min zan bisu gida Mom da Granny zasu kwana a hospital.

A hanya nake ta faman tambayar me yasa zamu maida Abba gida, shin ya samu sauki ne? Amma shuru babu mai tanka min har muka iso gida.

Toh fah alokacin ne na gane Allah yayi wa Abba rasuwa, kullu nafsin za'ikatul maut"
washegari da za'akaishi makwancinsa abokanan shi suna ta zuwa yan maradi da yan katsina da na kaduna sun cika a gidan shi na marafa estate, Ina ji Ina gani aka kai Abba gidanshi na gaskiya" hakika nayi  kuka fiye da tunanin mai karatu" na rasa mahaifi na mai so na" duk kokarin danake na inyi hakuri Amma na kasa har ciwo na ya tashi ranar sadakar uku, Yaya Faisal ne ya siyamin maganin da likita yace na rinka sha da zaran ciwo na ya tashi kuma cikin ikon Allah a kwana biyu na samu sauki, kuma aranar granny ta kira Momma a waya take shaida mata cewa Hafiz ya farfad'o"

Wayyooo Allah dadi kaman ya kashe ni na takurawa Momma da ta kaini hospital naga Yayanah" Momma ta sanya Yaya Saifullah ya kaini" Ina shiga ward din  na hadu dasu Mom, Mom ta rungume ni tana cewa d'iyata ya kk? Kafin na amsa Granny ma tace takwara kina lafiya ?

Gyada masu kai nayi Ina mai leken inda Yayanah yake kwance"  to my own surprised sai naga yana kallon mu fuskarshi kuwa a d'aure ya fito a asalin sojan shi" al my thoughts was he will say something to me amma ko dana mishi magana idanu kawai yake bina dashi baya cewa komai" I even touched him so that he can feel my sense of touch amma duk abanza na kalli su Mom nace" Mom me ya samu yaya nah na dauka yasamu lafiya tunda ya farka?

Granny tace haka yake fah Jiddah tun jiya daya farka likitoci sukai mashi yan gwaje gwajen su, baya cewa komai har yanzu" Mom ta d'aura da cewa Jiddah doctor yace best treatment din da za'ai Masa shine a fitar dashi waje idan aka mashi aiki a brain dinshi to inshallahu ana sa ran duk abinda ya manta zai dawo brain dinshi.

Cikin kuka nace then what are we waiting for Mom, Granng please we should do something kafin abun yayi yawa" Mom tace Jiddah munyi iya kokarin muga mun fitar dashi a jiya Daddy kwana yayi yana booking flights online amma bai samu ba, yau yaje tun safe amma sun tabbatar mashi da cewa babu jirgin dazaije wani country saboda Covid-19 dinnan"

Ohhhh gosh na daki karfen gadon, Ina kallon Yaya nah wanda shima ido ya kura min kaman mai shirin yin magana" na share hawayen daya zubo min Ina cewa Yaya Hafiz inshaAllah zaka samu sauki da yardar Allah"
Mom suka amsa da amiin ya rabbi"

**********************
Akwana atashi ba wuya kwanaki na ta tafiya kamar kyaftawar ido, Ummi basu koma katsina ba sai sukayi zaman su gidan Abba na marafa ita da Saifullah wanda kullin shi yake rarrashinta, saboda condition dinta ya nemi transfer awajan aiki aka dawo dashi kaduna" shi kuma Muhammad dama Abba ya siya mishi dankareren gida a malali, so suna cen shi da Leemarh wacce take da ciki tama kusan haihuwa alokacin" ita ma Fatima ciki gareta da alama ma tare zasu haihu.

December,2020
**************

Aka fara shirye shiryen fitar da yayanah waje saboda ai mashi aiki" alokacin ciwon zuciya na ya tashi saboda damuwar danake sanya kaina aciki,
Lafiya lau nake kula da Yaya Hafiz a hospital kawai watarana na yanki jiki na fad'i shine kawai aka kawo ni Barau Dikko teaching hospital wani likita Wanda ya karanci komai akan zuciya shi yake dubani ayanzu haka labarin danake baki Diela
" Daddy ya auri Ummi kuma tana zaune a gidan ta na marafa, Yaya Hafiz kuma yana NAFhospital kuma gobe ne tafiyansu,

Nace to meyasa ba'a kaishi ba tun farkon december sai yanzu January,2021
Jiddah tace Daddy ne yace abari na samu sauki sai atafi dani Kuma alhamdulillah saukiya samu don yanzu garau nakejin zuciyata kuma Ina da hope inshaAllah Yaya Hafiz zai warke"

*****************

The next day aka sallami Jiddah kuma direct airport suka wuce suka hau jirgin dazai kai su Abuja wanda daga cen zasu tafi"
Tafiyar daga ita Jiddah, Granny, Daddy, sai Ammi su kenan"

❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️

Littafi dai yana kan gangara Insha Allahu😁

Taku DIELAIBRAHIM ✍️
VOTE
COMMENT PLEASE

המשך קריאה

You'll Also Like

132K 8.6K 55
Kallon kitse ba litaffina bane na marubuciyar nan ne Halima Abdullahi k/mashi
38.7K 2.7K 49
labarin soyyaya ne tsakanin mai kudin da mulki dakuma yar talakawa Inda mahaifiyarsa tace bazaya auretaba saidai mai matsayi dakuma mulki yar manya...
764K 28.2K 26
"𝘩𝘰𝘸 𝘤𝘰𝘶𝘭𝘥 𝘺𝘰𝘶... 𝘩𝘰𝘸 𝘤𝘰𝘶𝘭𝘥 𝘺𝘰𝘶 𝘭𝘪𝘦 𝘵𝘰 𝘮𝘦 𝘧𝘰𝘳 𝘴𝘰 𝘭𝘰𝘯𝘨?" "𝙞'𝙢 𝙨𝙤... 𝙨𝙤, 𝙨𝙤𝙧𝙧𝙮... 𝙮/𝙣." ✧・゚: *✧・゚:*...
Daisy נכתב על ידי Sin

ספרות חובבים

2.8K 128 9
TokyoRevengersXQinShiHaung!Fem!Reader PAUSED