RAYUWAR JIDDAH ✔

By DielaIbrahim

10.3K 856 277

RAYUWAR JIDDAH Labari ne akan rayuwar wata ya' mace mai suna Hauwa'u Jiddah. Let embark on the journey togeth... More

01
02
03
04
05
06
07
08
09
10
11
13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31
32
33
34
35
36
37
38
AL'ADARMU
UMMI KWARAS
AL'ADARMU
AL'ADARMU

12

219 25 3
By DielaIbrahim

RAYUWAR JIDDAH
Part 1/12
Mallakin DielaIbrahim

***********************

Jiddah na isa gida ta bawa Momma sakon turare da yalo, dayake Momma uwa ta gari ce tace Autana badai kudin danace ki dena tabawa kika taba ba,
"Jiddah ta girgiza kai nooo Momma"
To where did you get the money?
"Jiddah ta tura baki sannan tace Momma yaya Faisal ne ya tura min ta acct dina"
Momma ta kalli Jiddah da kallon tuhuma dukda ta yadda da Jiddah tasan kuma bazata aikata wani abu mara kyau ba, kuma tasan Faisal yana bata kudi sosai,
Amma bashi zaisa taki tambayarta ba, ahankali tace Jiddah nasan bakya karya kuma karyar ma ba iyawa kikayi ba and nasan Faisal zai iya tura miki kudi batareda sani na ba,Amma yanzu inaso ki fada min gaskiyar yanda kika samu kudin,stop hiding things on me kinji Autana....Ina sauraron ki.
Sosai Jiddah ta fara zare idanu ganin Momma na son kureta, tabbas bata taba karya wa Momma ba,duk abinda ya faru da ita haka zata zayyana wa Momma ko kuskure babu, to meyasa ma zata biye mashi tai ma maman ta karya da sauri tace Momma am sorry bani na siya miki ba Hafiz ne.
"Momma tace ahab gashi gaskiya ta fara fitowa Ina jinki bani labari toh!
"Jiddah ta fadawa Momma duk yadda sukayi da Hafiz from A-Z babu ko gargada....Momma tace to kinga ai gwanda da kika fadamin yanzu dai bazanyi anfani da turaren ba kije store dina ki ajiye min acikin wardrobe, sai ki dawo ki wanke min yalon kinji Auta.
Toh Momma."Jiddah ta dawo da wankakken yalo a plate da knife + fork ta zauna kusa da Momma ta mika Mata.
Momma tace" yauwa Allah yai miki albarka.
Ameen Momma
"Momma tace JIDDAH nasiha nakeso nai amatsayi na na mahaifiyarki kinji.
"Jiddah ta gyada kai ahankali."Momma tace Jiddah na fada miki tun ba yau ba, kiyi taka tsantsan da maza, ko da kuwa yan uwanki ne, bawai Ina nufin ki dene sake jiki dasu ba kwata kwata Noooooo zaki saki jiki dasu amma bakamar yadda zaki sake da yar uwarki mace ba, kuma banda surutan banza da maza magana idan ba muhimmiya ba toh bance ki zauna kiyi da maza ba"Jiddah rayuwar ya mace tana da rauni ki san yadda zaki rike mutuncin ki damu iyayenki, karki manta kece farin cikin mu, kuma wannan rayuwarki ce ba ta wani ba kina jina Auta.
Jiddah datayi tagumi tana sauraron Momma tace eh Momma inshallah zan kula dakaina kuma zan kula da rayuwata Amma momma sai kina taya ni da addu'ar kariya saboda malamai suna cewa Allah yanasaurin amsar addu'ar uwa ga yayanta dakuma addu'ar 'ya'ya ga mahaifansu... "Momma tace Ina tayaki Jiddah Allah yasa mu dace baki daya
Ameen Jiddah ta amsa sannan tashiga ciki don ta watsa ruwa.
tana shiga ta fara jin karar wayarta, dube dube ta rinkayi ta rasa ina ta aje phone din, cen taji karar phone daga cikin hand bag dinta da sauri ta nufi wajan tana kokarin cirowa Letter ya fado, sai da Jiddah ta amsa wayar ta gama kafin ta dauki letter din ta Sanya shi cikin box dinnan dai mai kyau 😁.

***************
3month later
Hafiz da Jiddah sun fada duniyar da har yanzu basu yadda suna cikin ta ba,kimanin watanni hudu kenan da haduwarsu Amma sun kasa fahimtar abinda ke faruwa dasu dukdama suna jin feelings ajikinsu.
Ayanzu saura 1month Jiddah ta kare SIWES dinta, gashi suna seminar a school to which defense biyu zasuyi shiyasa kanta yayi zafi ita da fatima, wata ranar Friday Fatima bata da lafiya batazo base ba, Jiddah ce kadai taje haka taita faman kadaici ita kadai sai taji babu dadi dukdama akwai sauran course mate dinta amma tafi jin dadi idan Fatima na nan, ganin babu aiki a bench din da take, hakan yasa ta dau excuse ta fita cen waje ta nemi waje ta zauna tana tapping phone dinta chart take da Fatima tana fada mata yadda tayi missing nata.
From no where taji an kira sunanta "Hauwa'u Junaid" tana waigawa ta ga Hafiz tsaye shikadai ayanzu ta sake dashi amma ba sosai ba kuma masifar na nan bata bari ba sai dai idan bata motsa ba,Jiddah ta dan sake fuska kadan tace Good morning!
Morning ya amsa hade da zuwa inda take ya tsugunna in front of her yace I've been looking for you since naje Lab dinku ban ganki ba sai da wata colleague dinki ta nuna min direction din da kikabi shine na samo ki,kina wani abu ne yanzu Jiddah?

"Jiddah ta girgiza kai tana cewa chatting nake da besty na!
Hafiz yadan zare ido besty woooohh gashi yau kaman bata zo ba koh?
Jiddah ta gyada kai tayi da fuska kaman zatayi kuka"
"Hafiz yace nooo don't cry meke damun ta ne meyasa bata zo ba?
" Jiddah tace bata da lafiya ne kuma kuma gashi banje na gaisheta ba tun jiya"
Hafiz ya dan sa hannunshi a cheeks dinshi 🤔kaman me tunani cen kuma yace why not ki tambayi Mom dinki idan kunyi closing sai kije ki gaishe ta.
"Jiddah ta girgiza kai tana cewa Momma bata son yawo daga school zata ce na bari idan na dawo gida sai yaya Faisal ya kaini kuma shi yaya Faisal sai yamma yake dawowa.
"Toh ki kira Yaya Faisal din ki fada mai, sai yayiwa Momma explaining mana"
Jiddah tace okay tayi dialing contact dinshi bugu daya ya daga Yana cewa my little girl how far?
Yaya Faisal!
Na'am Auta"
Yaya Faisal besty bata da lafiya kuma yanzu nake so naje daga hospital ina so ka kira Momma ka fada mata please.
Sai yace "Jiddah ki bari idan na dawo na kaiki mana "
No yaya ka bari naje yanzu idan ka dawo sai ka biya ka dauke ni.
Faisal yace Alright bari na kira Momma koh kidan jirani.
Okay
Ta kashe wayar tasa dan yatsanta karami a baki tana kallon Hafiz,
"Hafiz yace zai kirata koh"
Jiddah tace eh"
Okay
Jim kadan saigashi ya kira tana picking yace tace kije ,so take your time a gidan idan na tashi awajan aiki zan biya na dauke ki kinji.
Tace thanks much yaya ta fada tana murna sannan ta kashe wayar.
Ta kalli Hafiz da murmushi afuskarta tace yaaaayyyyy ta barniiiii😁
Hafiz bai taba ganin dariyarta ba sai yau to which ya ciro wayar shi ya dauke ta hoto batareda saninta ba, ta waigo tace ehhennn you wre just saying something dazu,
Hafiz ya harareta playfully yace sai yanzu ma kika tuna saboda kinyi clearing damuwarki.
Tace am so sorry please
Hafiz yayi murmushi yace playfully am not.
"Jiddah tayi da fuska kaman zatayi kuka tace please am sorry!
Murmushi ya kumayi ganin reaction dinta very serious dinnan so she can pleed ehnnn...Lallai Hauwa'u you can't predict her character!!! Hafiz ya fada cikin tunani, sai yaji "Jiddah" nacewa tohm bazan tafi ba sai ka hakura ta fada tana neman waje kusa dashi ta zauna abinta tana kallon mutanen dake kai da kawo a wajan.
"Hafiz yace "Hauwa'u" ahankali,
Jin ya kirata hakan yasa zuciyarta bugawa ta waiga cike da kulawa tana kallonsa itama ido cikin ido zasu kai akalla 3 to 5min kafin Jiddah tai saurin dauke idanuwanta saboda jin wani sabon abu na shiga cikin jikinta.... ta tashi tana cewa bari na tafi....." But, quite unfortunate Hafiz ya riko hannunta to which gaba dayansu suka ja da baya saboda wani irin shock daya shiga jikinsu lokaci daya.
"Jiddah ta kalle shi kamar yadda shima yake kallon ta yana son tambayarta ko tana jin abinda yake jine amma bazai iyaba.... likewise itama same tunani a ranta tana son taji ko shima yana ji.
" Jiddah ta share maganar tace nawuce batareda ta sake kallon Hafiz ba, ta tafi tabarshi tsaye yana ta kallonta har ta bace ma ganinsa take ya saki ajiyar zuciya sannan ya bar wajan da tunani cike da zuciyarshi.
"Jiddah tana zuwa kai tsaye wajan Oga Abdul taje ta dau excuse wai bata da lafiya zataje gida, hakanan ya barta tana komawa common room ta hada kayanta tanayi tana tunanin Hafiz tabar Lab din ta kama hanya ta tafi.
******
Hafiz yayi sauri ya fito ya shiga mota,M.malunfashi na mashi magana akan kada ya fita shikadai amma yace kada ka damu M.M yanzu zan dawo ba jimawa zanyi ba....(sauri yake yaje wajan Dad saboda ya kirashi yana son ganinshi yanzu.)
m.malunfashi yace okay sir Allah ya tsare.
Ameen ya fada yana tuka motar hade da barin wajan cikin sauri don yai bitting time ya Isa da wuri, Yana Isa bakin gate ya hango mutane sun taru daga gani accident ne akayi har yasa kai zai wuce sai ya hango sojoji awajan hakan yasa yayi parking ya sauka ya nufi wajan.
"Ahankali yake kutsawa yana shiga idanuwansa suka hango masa Jiddah kwance bata numfashi ayanda ya gani kenan....da sauri ya karasa wajan ya tsugunna yana kallonta da mamaki to me ya faru da ita, dama har ta fito ne shi yama manta ya dubata...yana nan taugunne sojojin suka zo wajan sa suna gaishe shi cikin girmamawa, Hafiz yace dasu me ya sameta?
Daya daga cikin sojan yace ta fito kenan daga cikin base tana shirin crossing wani mai bike ya bigeta and suddenly she faint yanzu muna so mu kaita cikin hospital ne.
Hafiz ya shiga damuwa sosai, wanda har fuskarshi ta nuna yace bari na kaita hospital din....ya fada yana kokarin tashi, waigawan da zaiyi sai ganin sojojin yayi zasu dauki Jiddah baisan lokacin daya daka masu tsawa ba.
"What nonsense is this! nace ku dauketa ne? ya karasa wajan ya duka ya dauke ta cak kaman baby😄 sannan yace da dayan sojan daya kwaso mata jakanta da wayarta ya biyoshi dashi
Suna tafiya har suka isa motar yasanya ta abaya ya kulle sannan ya zagaya ya shiga motar, har yayi reverse zai koma cikin base sai ya kuma ganin kiran Daddy
Ya ilahi! Har na manta yana jirana and I have to take her to the hospital...sai kawai ya canja hanya yayi hanyar gwamna road, batareda yayi tunanin mezai faru ba.
Yana isa gida ya kira leemarh yai mata bayanin komai hade da bata key din motar yace idan ta farfado ki kaita dakin granny and tell her that she is your friend.
Leemarh tace okay ta nufi motar ta bude bata gane Jiddah ba kasancewar Hijab din data sanya ya rufe mata fuska hakan yasa tai mata duk taimakon daya kamata amma bata farfado ba,
Tsahon minti ashirin 20min kafin Hafiz ya fito ya gama da Daddy yace Leemarh how far ta farfado kuwa.....No Yaya uptill now na watsa mata ruwa Amma no response.
Hafiz ya zagaya ta dayan side din seat na gaba ya zauna hade da juyowa yana kallonta, ahankali ya kama hannunta ya matsa sannan yace wake up please( just like a whisper).
Leemarh na kallon ikon Allah tace yaya taya zata farfado with this little things lol.
Hafiz ya kalleta da mamaki sai kuma yace a zuciyar shi Leemarh fah is right wannan abunne zaisa ta farka yayi murmushi hade da kallon gefe yana tunanin abinda zaiyi at thesame time hannun Jiddah na makale da hannun Hafiz,yadan kara matse hannun wanda baida kwari ko kadan.
Leemarh datake kokarin tapping wayar ta, ta hango yatsun kafar Jiddah na motsi, da sauri tace Yaya she is responding, tayi saurin bude mata fuskarta anan suka ga Jiddah nata faman yamutsa fuska and idunuwanta akulle still, Hafiz ya sake matsa hannun ahankali, sai alokacin ta bude ido da sauri jin presence dinshi a tare da ita moreover jin shocking din kuma har cikin jin jikinta hakan yasa ta tsorata ko data bude ido kuma sai ta ganta cikin mota tsahon minti biyar tana kallon saman motar batareda ta ga su Hafiz ba, tana recalling abinda ya faru da ita dazu bayan ta fito daga base, ji tayi Leemarh na cewa Yaya ta farfado wlhy idanuwanta abude amma kaman bata motsi what happened.
Sai alokacin Jiddah tagane tana tare da wasu ne ahankali ta soma kokarin tashi tana mutsu mutsu, Leemarh tai saurin taimaka mata ta tashi tana ce mata sannu ko.
"Hafiz ko ya tsare ta da idanu ga hannu ta cikin nashi mamaki yake ya akai ta farka kodai taji shock dinne itama, ko kuma taji maganar dayayi.
"Jiddah tace da Leemarh yauwa thank you hade da kallonta sai alokacin Leemarh ta ganta da kyau tafara tunanin ta santa awani waje ita ko Jiddah ta gane Leemarh da sauri tace, kece muka taba saukewa a gwamna road ko?
Take Leemarh ta gane ta tace yes nice dama Ina ta tunanin nima nasanki somewhere else but,I can't recall sai yanzu....sukayi murmushi Jiddah tace to ya akai nazo nan, nidai nasan bike ya bige ni.
Hafiz yayi gyaran murya sai alokacin Jiddah ta lura dashi ta Kuma ga hannun ta acikin na Hafiz dasauri ta fizge hannun tana cewa ya akai na shiga motar ka kuma?
Hafiz ya fada mata duk yadda akayi ta fahimta sannan yace Leemarh dama kinsanta ne?
Leemarh tace eh sun taba rage min hanya ne suka kawo ni har gida.
Hafiz yace okay sannan ya dubi Jiddah yace Hauwa'u karki damu driver zai kaiki har gidan su besty amma hope babu abinda yake miki ciwo?
Jiddah tace no babu dama tsoro ne yasa nayi fainting.
" Hafiz yace Leemarh Daddy yasani aiki please kiyi wa driver magana ya kaita inda zata, Leemarh tace to yaya nah, ta taimaka ma Jiddah ta fito shi kuma yabar gidan cikin sauri, sai da Leemarh taja Jiddah wajan granny.
Suna shiga kuwa granny tace Hali dubu bakuwa akayi ne,
Ni wallahi granny sai ki rinka cemin Hali dubu ni sunana Leemarh!
Granny tace na fada kuma bazan dena fada ba, kawai an wani lakaba maki Leemarh kaman wata lema (umbrella 😂)
Leemarh tace kingani zamu fara Koh granny Ni yanzu ba fada nazo yi ba, bakuwa nakawo maki
"Granny tace Ja'irah kawai bakuwa zo zauna kinji ki rabu da wannan lemar,..... Leemarh dai ranta ya baci tace bakomai granny yanzu bazan biye mki ba ai amma kibari tommorow.
"Jiddah ta zauna kusa da granny tana murmushi take taji son tsohuwar ya shiga ranta tace Ina wuni
"Lafiya lau ya gida"
Lafiya tabata amsa
Leemarh ta nufi fridge din granny ta dauko mata ruwa da chi-exotic along with glass cup ta kawo mata tana cewa kisha wani abu kafin ki tafi koh.
" Da kyar Jiddah tasha ruwan granny tace miye sunanki?
"Hauwa'u Jiddah"ta bata amsa
Granny tace MashaAllah Allah kice takwara kika kawomin Hali dubu, ahh gaskiya nagode sosai tana murmushi
Leemarh tace to su granny anga namesake sai faman washe baki akeyi....granny ta galla mata harara ta waiga ta cigaba da mata hira,har dai Jiddah taga time na tafiya har 2pm tace granny bari na tafi kada nayi dare,
Granny tace "okay to ba damuwa ki gaida mamaki kinji ta tashi ta shiga ciki Jim kadan sai gata ta fito da jakan kwali mai kyau ta bawa Leemarh tace ungo bama kawarki....Takwara yaushe zaki kara zuwa musha fira don Ni yanzu dake nakeyi ba lema ba.
Jiddah tayi murmushi mai kayatarwa sannan tace zan kara dawowa Inshallah nagode.
To sai anjima Koh
Leemarh sai dariya takewa granny tana tsokanarta har suka bar flat din Leemarh batayu tunanin ta kai Jiddah wajan Mom ba don haka ta kaita wajan driver kawai shi kuma yakaita gida.
***********
Sai kusan karfe hudu Hafiz yagama da aiken Daddy ya dawo gida around 5pm ya tafi wajan Daddy yace Daddy na gama maka booking flights din jirgin zai tashi 10am gobe inshallah ga details din komai da komai.
Daddy yace okay to thank you son.
Mom tace Amma dear ba jimawa zakayi ba ko?
"Daddy yace nooo just 1month inshallah,
"Hafiz yace to Allah yakaimu Daddy, naso mu tafi tare wallahi saboda it's been long da mukayi tafiya tare, Daddy yace nima shiyasa na tambayeka ko kana free amma kaga har yanzu baka gama course din dakakeyi ba.... nevertheless wani lokacin sai muje Koh.
Toh Daddy Allah yakaimu.
Ameen

Da safe gaba dayansu suka raka Daddy airport ya tafi Australia company dayake aiki ne suka nemi suganshi saboda cigaban daya kawo masu a company dinsu sosai yana aiki dasu for over 25years now yasamu kudin da zai iya bude nashi company din Amma sun rikeshi saboda sunsan muhimmancin Engr.Abubakar Yusuf Abubakar
Wanda sukafi kira da Engr. A.Y Abubakar.
Hafiz kuma daganan ya yafi wajan aiki Amma sai da ya tabbatar Mom,Leemarh da granny sun tafi kafin ya wuce shima.

********
Yau tunda ta iso hospital din take Allah Allah ta hadu dashi amma ko motarshi bata hango ba hakan yasa ta tafi Lab to which ba ita ta fito ba sai karfe biyu 2pm lokacin tashi kenan tayi sallah sannan ta kama hanyar gida, tana tunanin zata biya gidansu Fatima don jiya bata samu taje ba.
Tun daga bakin gate na hospital ya hango ta shi Kuma yana cikin mota ta mirrow ya ganta kanta na kasa tana tafiya cikin natsuwa batareda wani rawan kai ba, don dama Jiddah akwai natsuwa masifar tane dakuma in ta fara surutu sai ka dauka kaman tana da rawankai.
Har ta foto tazo daf dashi batareda tasan cewa shine a cikin motor ba ta tsaya tana jiran Napep sai taga an sauke glass din window Hafiz ta gani fuskarshi babu yabo babu fallasa yace cikin turanci tazo ya kaita.
Sai data jah ajinta na tsahon minti biyar tayi tsaye kaman ba da ita yake ba don kanta ta nufi inda yake ta bude ta shiga dukda cewa ta ji dadi aranta ganinsa datayi amma hakan bai nuna afuskartaba sai ma daure fuska datayi don ko gaishe shi ma batayi ba.
"Hafiz dama shima ba gwanin surutu bane sometimes hakan yasa yai banza da ita ya tuka motar har suka kai bakin gate babu wanda yace komai.
Kai tsaye ya dauki hanyar Kinkinau without asking her, tuni Jiddah tace da sauri unguwan rimi zani ba kinkinau ba.
Baiko kalli inda take ba kasancewar ko gaishe shi batayiba data shigo dukdama bawai ya damu da gaisuwan bane Amma at least ka nuna ma mutum respect ai is something...(ni ko nace ku dai sojoji akwai son girma)
Ganin bai kula taba Kuma ya cigaba da tafiyarsa bai juya ba, hakan yasa ta galla masa harara ta daure fuska itama sannan ta jinginar da kanta tazuba masa ido taga Ina zai kaita.
Sosai take mamakin Hafiz ganin Kinkinau ya nufa Kuma har sun kai unguwan, ranta yayi mugun baci but, ta rasa me zata ce mashi har ya kawota daidai inda take cewa "momma ta aiketa cen gidan"
Sai alokacin Hafiz ya ciro paper yayi rubutu sanin bazata karba ba, Kuma baiyi tsammanin bazata karanta ba hakan yasa ya fizgo karamar hand bag dinta ya sanya mata paper din, sannan yayi unlocking motar ya bude ta cike batareda ya kalleta ba ya juya kai fuskar nan tashi tasha mur.
Sosai Jiddah take mamakin karfin hali irin na Hafiz har ma Yana da karfin halin Sanya mata paper acikin jaka bayan ya kawo ta gida after all ita unguwan rimi tace zata, Duk yadda take son yin masifa ranar kasawa tayi saboda wani takaici daya tokare mata zuciya hakan yasa ta fita da sauri acikin motar tayi hanyar gida shi Kuma yana kallonta yadda take tafiya aranshi kuwa dariya yake tayimata ya girgiza Kai yace Hauwa'u kenan yaja motarshi yabar wajan.
Jiddah na shiga gida tana mita tana masifa kawai ta iske sunyi baki saif ne da Ammi da Mama lokaci daya daji bacin ran ya tafi hakan yasa ta zauna tafara hira dasu, inda suke cewa sunzo gaisuwan rasuwa ne kuma ayau yau din zasu koma....Jiddah ta zumbure baki tana cewa Ammi ni zan biku naga Ummi da Abba da Yaya Muhammad.
Mama tace Jiddodooo ai baki gama SIWES dinba taya zaki bi mu.
Jiddah ta buga kafafu like a small child tana cewa uhm uhm Mama zan biku ko kwana daya ne nayi sai driver ya dawo dani.
Momma tace Jiddah saura kwana nawa ku gama IT all in all saura 3weeks to ki bari ku gama sai Yayanki ya kaiki mana.
Jiddah tadan kalli Momma tana nazarin maganarta kafin tace toh Momma shikenan na hakura
Yauwa my little girl cewar Faisal dayake ta faman kallonta tun dazu. Tashi tayi ta nufi daki don ta canja kayan jikinta, wanka ta farayi sannan ta sauya kaya ta koma falo suna ta hira har suka tashi komawa sukai musu sallama suka tafi Jiddah na bawa Said sakon cakes,cookies da dambum nama wai akaiwa Abba da Ummi da Yaya Muhammad.
Saif yace angode Auta Jiddah zaakai masu bye.ta koma parlor suka cigaba da hira ita da Momma inda ta tsefe wa Momma ta wanke mata tai mata stretching tana cewa Momma na dana iya kitso yau dana miki wollah.
Momma tayi dariya tana cewa gobe inshallah zaki tsefe kanki kema idan mai kitson tazo sai ta Mana kinji.....Jiddah ta tura baki don ita aduniya batason kitso saboda cika da tsayin gashin kanta rober hair gareta kuma idan tana tsifa ko ana mata kitso har kuka takeyi saboda zafin da yake mata, da tana karama ma Momma ce kadai ke taba mata kai ahaka Momma ta koyi kitso don dole to which har yanzu ita takewa Jiddah kitso.
"Jiddah tace Momma kinsan bana son ana taba min kai ni ke zakimin kitson kinji.
Momma ta girgiza tana cewa Jiddah rigima to Allah ya kaimu goben.
Ameen.
Jiddah na shiga daki ta tuna paper din Hafiz hakan yasa ta dauko taji kaman ta bude yau sai ta zauna saman gadonta tana shirin budewa ne Momma ta shigo, tashi tayi ta sanya paper din cikin box sannan tayi facing Momma tana cewa Momma kina son wani abu ne?
Momma tace yes aiken ki zanyi kije gidan su sabeer ( Bayan layinsu ne gidan maman sabeer din kawar Momma ce) please kice mata idan ta kawo turaren wuta ta baki masu kamshin ki kawomin, turaren wutan mu ya soma karewa kiyi sauri ki dawo.
Toh Momma ta Sanya hijab dinta ta tafi.
****
Jiddah dai bata samu taje gidan su Fatima ba sai weekend Faisal yakaita ta wuni kafin suka dawo gida....gashi bata kara sanya Hafiz a ido ba tun ranar daya bata mata rai.
2weeks letter, alokacin saura 1week su gama SIWES.
"Jiddah tana Lab ita da Fatima suna aiki Hafiz ya shigo Lab din kowani staff suka tashi suka fara gaishe da commander har IT student, ya amsa gaisuwan cikin fara'a sannan yayi passing information din dayazo passing
"Jiddah ta kura masa ido ganin shi very new yau, ya mata kyau sosai ji takeyi kaman taje tace mishi yayi kyau....amma sai ta basar hade da juya fuskarta tayi kaman bata ganshi ba, shi kuma
ya fita ranshi fal farin ciki saboda yaga Hauwa'u yau kwana nawa yana son ganinta bai samu yaganta ba gashi dukkan abinda yake rubuta mata a paper it seems tana karantawa tunda ga alama yana gani atareda ita....yayi kayataccen murmushi har ya koma office.
Aranar ya yanke hukuncin fitowa ya fada mata abinda ke cikin ranshi, saboda ya yadda ayanzu yana son Hauwa'u kuma ya yadda da halayenta dukda baiyi binciken gidansu ba, amma yasani with time idan suna tare zai samu yasan komai agame da ita, shidai yasan yana mata matsanncin so wanda shi kanshi baisan time din da hakan ya faru dashi ba.....hakan yasa ya aika aka kira mashi Jiddah.
Da sallama ta shiga office din yana zaune a kujeran sofa yana danna laptop ahankali yace come in.
tana shigowa yai switching laptop din ya tashi yana cewa Hauwa'u zo ki zauna, tazo ta zauna tana kallon shi,
Hafiz ya dauko stool ya zauna yana facing dinta,ya tsura mata ido for some minutes har yasa ta tsargu ta saukar da kanta tana wasa yatsun hannunta.
Hafiz ya kura wa yatsun hannun ido, the more yana ganinta the more yake kara ganin kyayunta, dama shi tuntuni yana son traditional henna amma ya lura Jiddah tana son Jan lalli tun ranar daya fara ganinta, ranar daya karya mata hannu ya ganta da jan lalli, har yau bazai manta ba yana tuna henna din wanda yai mashi kyau amma alokacin tsoronta bai barshi ya ga lallin da kyau ba.
Hafiz yayi gyaran murya yace in a nice voice "Hauwa'u"
Ahnakali ta dago tace na'am
Yanda ta kalle shine yasa ya tsargu sai ya kasa fadin abinda ke ranshi sai ya canja da cewa kina da saurayi?

***************
FANs say one word about
Hafiz Abubakar and
Hauwa'u Jiddah

VOTE!VOTE!!VOTE!!!!!!!!!
PLEASE

Continue Reading

You'll Also Like

1.4M 117K 110
Kalmar QADDARA kalma ce dake rataye bisa wuyan kowanne bawa,haka rayuwa ta gada,tafe take da QADDARORI kala kala,masu zaqi da akasin haka...
67.4K 7.4K 58
Murmushi tayi mishi wanda ya tafi da imanin sa yayin da ta juya kallonta ga duɓɓin mutanen wajen. Dogayen yatsunta biyu wanda suka sha jan lalle ta b...
10.7K 549 20
Labari ne dake dauke da darussa kala kala na rayuwa, Mai dauke da tausayi, Al'ajabi ga kuma kauna agefe d'aya.. shin wacece UMMI_A'ISHA?
13.8K 3.2K 21
"හරි නරකයි ඔහෙ මට ඉන්න දෙන්නැ ඉහි..ඉහි ,අනික මන් ඔහෙගෙ නමවත් දන්නෑ" යෙහස් බිම බලාගෙන කිව්වා.. "මගෙ නම විහංඟ , විහංඟ ප්‍රභාෂ්වර රත්නායක ....කවුරැහරි උ...