RAYUWAR JIDDAH ✔

By DielaIbrahim

10.3K 856 277

RAYUWAR JIDDAH Labari ne akan rayuwar wata ya' mace mai suna Hauwa'u Jiddah. Let embark on the journey togeth... More

01
02
03
04
06
07
08
09
10
11
12
13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31
32
33
34
35
36
37
38
AL'ADARMU
UMMI KWARAS
AL'ADARMU
AL'ADARMU

05

324 20 0
By DielaIbrahim

RAYUWAR JIDDAH
part 1/05
Mallakin DielaIbrahim

*****************

..........Gwamna Road suka nufa tun bayan fitowar su daga NAFbase din suka hau kan titin express ayayinda basu tsaya ko ina ba sai bakin gate na wani katafaren gida, wanda yasha gyara, gate din gidan babba ne mai katuwar rumfa ciki da waje, inside the house kuma malam dauda gateman ne zaune kofar dakinshi kusa da gate,zaune yake saman wani dogon bench na  katako,Yana ta faman goga aswaki a bakin sa gefe daya na hannun daman sa kuma radio ce take ta faman surutu,Horn yaji bashiri ya tashi ya leka don yasan mai gidan dai duk yau bai fita ba in ba masallaci dayake zuwa ba, bude separate door din dake gefen gate din yayi hade da lekawa......take ya zare idanu hade dacewa ahhhhhh karamin mai gida MashaAllahu ya fada yana washe baki, Take ya rufe kofar sannan ya nufi gate yana turawa da sauri har karshe.
At that time motocin suka sako kai cikin harabar gidan sukayi parking awajan da aka ware domin aje motoci.
Bude murfin motar akayi tsahon dakika biyar kafin ya sako kafar sa daya waje ayayinda malam dauda gateman ya karaso yana kai gaisuwa cikin girmamawa....alokacin har ya fito yana kuma gyada ma malam dauda kai alamar yana amsa gaisuwar tashi sannan ya mika masa bandir din yan dari biyu sabbi dal, yana cewa malam dauda ayi hakuri da wannan banyi  maku tsaraba ba, malam dauda na murmushi yana cewa ahhh yallabai karamin mai gida wannan kyauta dayawa haka jiya an bamu yauma haka ai hakan ma mun gode sosai Allah ya saka da alkhairi. Shi dai bai tsaya sauraran malam daudan ba yayi wucewarsa ciki dasauri take kuma idanuwansa suka hango masa kanwar tasa tana nufo inda yake cikin sauri itama... hugging dinshi tayi tana cewa Yaya Hafiz welcome back.
Ya kama karan han cinta yaja ya matsa kadan yana cewa lil sis I missed you
"I missed you more Yaya"tayi saurin fada tana kwantawa ajikin shi lokaci daya kuma suna karasawa cikin main parlor dinsu....Mom ya fara hangowa tsaye a dinning tana jera warmers masu kyau na abinci akan dinning, bangaren parlor dinkuma Daddy ne zaune saman sofa daya daga cikin kujerun parlour masu design din Royal.Ayayinda Hannun Daddy ke dauke da newspaper.
Batareda sanin kowa ba ya daga murya yana cewa  Mom,Daddy am back, home sweet home ya fada with so much excitement a fuskarshi, yanayi yana daga hannayenshi sama kaman wani karamin yaro....Lokaci daya mom ta jiyo tana murmushi, haka zalika Daddy ma da murmushi yake kallon Dan nasu.
Leemarh tai masa kuri da idanuwanta tana dariya ta karasa palour wajan Daddy tana cewa su Yaya Hafiz anzo gida dole ka sake da kowa,yanzu kam da awaje ne dakayi kicin kicin da fuska, ka daure kaman baka taba dariya ba, shikam zuba mata idanu yayi yana hararar ta cikin wasa shima ..Cen kuma bayan ta tsagaita sai tace Nevertheless yaya ni nafi son haka saboda kada watacen ta janye min hankalin Yaya na, ta karashe maganar cike da shagwaba tana langwabar dakai ayayinda take kokarin zama gefen Daddy...Daddy da ya dago yana kallon son din nashi yana murmushi ya kalli Leemarh yace exactly kuma maganar ki gaskiya ce fah Auta, kinsan Officers dinnan akwai jiji da kai ya karasa yana shaking head dinsa....shiyasa up till now bai kawo matar aure ba, sosai leemarh take dariya harda rike ciki....tace oooooh yes Daddy ta kanne ido daya tana kallon yayan nata.
Hafiz daya zuba masu ido kaman wani maraya,hakanan fuskar nan ta koma kaman bai taba dariya ba yace haba Daddy, da tsokana za'a tarbe ni yau Koh?,......Nan take Daddy yace Leemarh look at his face......take suka kuma kwashewa dawani dariyan......cikin wasa.
Mom tsaye a dinning tana kallon su cikin sha'awa wanda tun fara conversation dinsu take murmushi itama tana kallon Dan nata yadda yakoma kaman wani maraya,tsabar tsokanan shi da sukeyi, Sai alokacin ta sauka zuwa palour din tana cewa Wallahi ku kyale min Babana hakanan, haba mutum ma ya dade baya gida,and ya dawo yanzu maimakon kuyi masa tarba mai kyau Amma kun zauna kuna tsokananshi, tohhh nagane nufin ku so kuke kucemishi kuna bukatar In-law tohm baza akawo in-law dinba takarasa alokacin data Isa inda Hafiz ke tsaye ta rike mashi hannu hade damashi murmushi tace rabudasu Babana.... Hafiz ya kalli Mom ya tura baki kaman karamin boy yace mom dama nasan ke kadai kikayi missing dina ya karashe yana rungumeta sannan yace kuma ma ke kadai zan kawo ma in-law sukam bazan kawo musu ba.....ae baima karasa ba Leemarh ta ruga da gudu wajan sa tana cewa Allah Yaya munyi missing dinka koh Daddy ta karashe maganar tana kallon Daddy...Ba Hafiz ba har Mom sai da suka dara saboda yanda leemarh tayi reacting,murmushi Daddy yayi yace ae duk yaron daya dade baya gida toh idan ya dawo dole ayi missing dinsa terribly, muma munyi Missing dinka kuma dai gaskiyar Mom ne, muna so ka kawo mana In-law dinmu ya karashe maganar fuska adaure Kuma yana kallon jaridar hannunsa Kaman bashi yayi maganar ba.
Hafiz yayi long breath kafin ya karasa wajan Daddy ya zauna ya rungumeshi ta baya cike da qauna da kewan juna Daddy yace welcome back son,ya aiki
Hafiz yace aiki Alhamdulillah Daddy, jiya nazo amma ban jima a gidan ba natafi saboda wani important meeting danayi attending a Abuja....Daddy yace  Mom dinku ta fadi min so I wanted to call you and she said you are in your way, dukdama baki suka hada da leemarh wai don ka dawo yanzu,....Hafiz yayi murmushi yana kallon Mom da take kokarin zama kusa dashi tace Amma bana fushi da Babana , Leemarh kuma tace and it's was my plan because we really missed you terribly, wannan karan Hafiz can't stop him self from blushing, take ya kuma jin son family dinshi na kara shiga cikin zuciyarshi, suna ta wasa da dariya Hafiz yace Mom where's my Honey?tunda na shigo gidannan banganta ba, ko batasan dawowana bane, let me go and see my honey" I missed her wollah ya karashe maganar yana kokarin tashi daga saman kujera, Daddy yace dashi batanan fah son.
Hafiz ya dubi Daddy cike da tambaya a fuskar shi yace ina take Daddy?
Mom tace "Babana sun tafi India da Baba Yusuf za'a duba mata idanunta, Hafiz ya dafe kai Lord! sannan yace Daddy har yanzu ciwon idanun na damunta ne?
Daddy ya gyada kai, sannan yace Idanun na damunta sosai shine nace Yusuf yatafi da ita aduba idon sannan abata magani, yanzu dai satin su biyu da tafiya amma sun kusa dawowa.
Hafiz ya gyada kai toh Allah yasa adace.
Ameen suna zaune suna ta hira aka fara kiraye kirayen sallah Daddy da Hafiz suka tafi masallaci, Mom da Leemarh kuma sukayi sallan su agida...sai bayan sallan isha'i Daddy suka dawo, sannan suka nufi dinning zasuyi dinner anan suka tarar da Mom suna jiran dawowansu.
"koda suka gama cin abincin palour suka koma sun jima suna ta hira inda Hafiz ke basu labarin kasar dasukaje yin wani course sun sha wahala, sai gashi kuma suna gamawa aka turo shi Airforce Base kaduna."Daddy yace nayi matukar farin ciki da aka maidoka kasarshi koba komai kanatare da family dinka yanzu, Mom ma tace exactly kuma ka tabbatar ka samo mana In-law kafin a kara cilla ka wani gurin, Hafiz kama baki yayi yana mamakin Mom, Leemarh kam kwance take saman kafar Mom  kuma dariya takeyi abinta, Hafiz yace Mom ki kwantar da hankalinki kiyita min Addu'a Allah ya bani mace ta gari,Mom ta capke tana cewa inshallah Babana Ina yimaka kuma zan cigaba dayi.... Daddy kam gyaran murya yayi, sannan ya cigaba da karanta newspaper dinshi har karfe 10
Hafiz ya tashi yana yi masu Mom da Daddy sai da safe, ya kalli Leemarh da har yanzu tana jikin Mom yace Mom haryanzu baki yaye wannan Autan bane wai?
Ahhh toh kaima kafada ai Babana" gatanan kullun shagwaba sai faman nanike min take kaman wata kuliya(cat)
Leemarh ta dago kai tana tura baki tace to bani bace Auta cikin sigar shagwaba.
Yayi folding 2 hands dinshi sannan ya dubi Leemarh yace oooohhh as big as you are, karki manta kina da kanne fah ya fara counting da hannu Yana cewa, akwai su salim, twins,aisha, and maryam('ya'yan kanne Daddy ne),and the rest kice wani kece auta kina wani kwantawa ajikin Mom sai kin sa kafafunta suyi mata ciwo....Allah Mom ke kike kyaleta ma.
Leemarh ta tsuke fuska ta bubbuga kafa ita ala dole shagwaban ya motsa tace Daddyna kanajin Yaya koh?
Daddy yace ooo ooo nikam bazan shiga tsakaninku ba saboda yanzu zakuba mutum kunya.
Hafiz yayi wa Leemarh gwalo Yana cewa kima dena hawa don aure zan miki kwanan nan.......ae bai karasa fada ba ta tashi tana yima Mom korafi.
Mom tace lah lah lah karki biye mashi kinji Auta sai ya farayi kafin azo kanki tunda he is   older than you,Hafiz dayaji maganar Mom sai ya sanya hannunshi a keya yana sosa kai yanacewa"goodnight"."Leemarh tana dariya tace dawo nan mana ka cigaba da tsokana yaya, bai ko kulata ba yayi gaba abinshi tsabar baya son biye wa maganan Mom, shi ya rasa meyasa yanzu suke son takurashi da maganar aure.har yakai bedroom dinsa yana tunani acikinranshi.sannan kowa ya wuce makwancinsa.
Hafiz na shiga daki wanka ya farayi sannan ya canja kaya izuwa sleeping wears fararen riga da wando, harda socks fara abinshi tsabar sabawan dayayi tun suna school idan zasu kwanta bacci sai sun saka socks.. Idan ko baka sa ba, ranar ka shiga uku, don kuwa tun asubahi za'afara maka ihu ana dariya duk abinda kayi aranar sai ayi ta dariya, wannan dalilin yasa ko baka son saka socks dole ka nemo ka sanya don kwanciyar hankalinta...  Hafiz na daya daga cikin wanda suka fara kawo saran sanya su lokacin bacci daganan kuma yazama dole kowa ya sanya".   Ya kwanta yana facing ceiling maganganun Mom & Dad su suke ta faman yi masa yawo a kwakwalwar sa, shikam nawa yake daza'a farayi masa maganar aure, toh wai ma shi da bai taba ganin macen data burgesa arayuwarsa ba, beside shi mace ma bata gabanshi yanzu saboda bai taba sawa aranshi zaiyi tarayyah da mace ba,"Sai dayayi numfashi mai tsayi kafin ya rufe idanuwansa lokaci daya kuma pictures din yarinyar daya bige a hospital su suka fara tsere acikin idanuwansa, saurin budewa yayi yana fadin Hasbunallahu wani'imal wakil, Allah kaimin tsari da wannan yarinyar nikam nasan nine sanadin karayan ta Amma ko mayyace ae ta sarara min tunda nayi mata dukkan abinda yakamata nayi, ya cigaba dacewa Allah yasa ma taji sauki kafin gobe subar hospital din donni bana bukatar ma na sake ganinta, haka yaita faman masifa shikadai kuma acikin ranshi yana danasanin saka idanunshi afuskarta.....ya juya ya kwanta ahannunsa na dama yana addu'a Allah yasa karya kara ganinta a idonsa ahankali ya ringa rufe idanunshi har bacci ya daukeshi.
*********
Karfe Biyar na asubahi ya farka hade dayin salati yana kokarin tashi daga kan gadon, ya nufi toilet yayi alwala yazo ya sauya kaya izuwa ash color din jallabiya ya feshe jikinshi da Arabian perfume Mai kamshi, ya dauki sallayarsa ya fita ahanyar fita ya hadu da Daddy suka jera har masallaci.
Around 6:20 suka dawo gida don saida suka tsaya yin karatu, suna dawowa ya cire kaya ya nufi bathroom donyin wanka kodaya fito lokacin karfe 6:40 shiri yakamayi cikin uniform irin na jiya Amma bana jiyan ya maimaita ba kasancewar yana dasu kusan guda biyar duk kala Daya,Banda Kuma sauran kakin sojojin don kowani rana da irin uniform din dasuke sawa,
Karfe bakwai 7:00 ya fita zuwa dinning yana kokarin answer call  din M.Malunfashi yanacewa kun karaso ne, okay tohm gani nan fitowa, kai tsaye ya nufi dinning room din nan ya samu Mom tana shirya abincin, ya rungumeta Yana cewa good morning my beautiful Mom,
Murmushi Mom tayi sannan tace Morning Son how was your night?
Hafiz yace it was awesome Mom, me Kika dafa mana ne? Yakarasa Yana kokarin bude wani cooler....tace na hada maka komai a basket ka tafi dashi cuz naga kaman zakayi late....Amma ka tabbatar kaci kaji Babana. Murmushi yayi yace that's my Mom, Thank you so much you are the best mommy in whole world, I love you Mom 😘yai mata peg a kumatu sannan ya ansa basket din Yana cewa good bye mom.......Mom ta tsaya tana kallon shin adoringly tana Jin son Dan nata aranta sosai da sauri tace, Take good care of your self Sweetheart and make sure you eat your breakfast.
Okay Mom consider it done.
Bye tace tana daga mashi hannu.
Tana nan tsaye taji an rungumeta tabaya Leemarh ce, tace Mom na fara kishi fah, yau kin manta da Auta,kinma manta ki tashe ni da asubahi, and baki ko leko kin duba ni ba tun jiya, ta karshe maganar kamar me shirin yin kuka,
Mom ta kama hannunta tace Haba Autana kishi kikeyi da Yayannaki....ooo ooo bansan Auta da wannan halin ba.
Leemarh ta girgiza kai... Toh ae.....
Shihhhiiiiiii 🤫 mom ta katse ta tana cewa kul nasan bazaki school bane and shi kuma nasan zai fita da sassafe shiyasa na tashi na hada masa breakfast da wuri.
Leemarh tace Mom stop it please am just kidding nima tunda na kwanta tun jiya sai yanzu na tashi fah, Kawai I blame my self ne da ban tashi da wuri na tayaki aiki ba,......mom tayi murmushi tace don't worry Auta nasan baccin ne yai maki nauyi shiyasa ban tada ke ba., bari naje na duba Daddynku ko ya gama shiryawa, Please ki karasa fito da sauran warmers din dake kitchen kafin mu fito.
Okay Mom dina ta fada tana yima mom murmushi.

*******
Tunda suka shiga hospital din sukayi parking sannan ya fito, escort na biye dashi abaya, ya nufi assembly ground dinsu inda yaga gabadaya staffs din suna jiran isowarshi, anan akayi introducing dinshi as The new commander of the hospital, and ba wani jimawa zaiyi ba 7month zaiyi anan kawai...... welcoming dinshi suke tayi suna murna don tun kafin yazo labari ya karade hospital din cewa za'a kawo New commander Hafiz Abubakar and kowa Fadi yake ai yana da kirki sun dade suna Jin labarinshi......anan aka rufe taron kowa ya tafi office dinshi, Hafiz Abubakar ya shiga office dinshi Wanda ayau zai fara aiwatar da aikinsa kuma yana so yayi aikin dakyau dukda bawani dadewa zaiyi ba Amma ya dau alkawarin yin aikin dakyau, dukdama yana gamawa za'a kara masa Rank amma shi hakan bai dameshi ba, yana dai so yayi aiki tsakani da Allah, Although he knows that he have to achieve his goal, but sometimes we don't have to work hard for our own good.
Haka ya cigaba da having thoughts at thesame time yana aiwatar da aikinsa.

*******

Bangaren su Jiddah

Momma ce zaune gefen gado, hannunta dauke da bowl na glass da spoon hadin friut salad ne wanda yasha madara, momma ta debo a spoon takai bakin Jiddah wacce ke zaune saman gadon ta jingina da pillow ayayinda take sanye da doguwar riga na material maroon color kanta kuma ta yafa black veil, ta bude baki kadan aka sanya mata fruit salad din abaki, da kyar take taunawa Amma fah fuskar nan tata ayamutse ga wani hade rai datayi  yadda kasan kashi aka sanya mata abaki.
Wayar tace ta fara ringing takai dubanta ga right hand dinta inda phone din ke ajiye.....sannin right hand dinta shine mai ciwon hakan yasa ta tsura wa hannun idanu wanda ayanzu bata iya Koda motsi dashi tsabar tsami dayayi mata, girgiza kai tayi ta sanya Left hand ta dauko phone din ta amsa wayar sannan ta Kara a kunne, hade da cewa Yaya Faisal Ina kwana.
Cikin wayar aka amsa da lafiya lau Jiddah ya karfin jikin naki?
"Da sauki Yaya Faisal"Amma nikam fushi nake dakai baka zo ka dubani ba,
Lord! Ya furta cen kuma yace Jiddah waya ce miki ban zo ba, nazo fah kuma alokacin baki farka ba, kina ta bacci, momma batace miki nazo dubaki ba.
"Ta fadamin ta amsa" Amma meyasa baka jira na farka ba?

Ohhh my little girl kiyi hakuri kinji an kirani a office ne, shine na tafi am sorry kinji......"uhmmmm toh Yaya Faisal ai komai ya wuce".
Dariya Faisal yayi sannan yace
To thank you kinji, Ina ta faman kiran Momma Amma shuru bata picking, and I decided to call you, ina ta shiga ne?
Gatanan fah Yaya and wayar ta I think ta Sanya a silent ne tun jiya.....cikin wayar akace uhmmmm kukam ai haka kuke keda momma kuyita faman sa waya silent and flight mood bansan dalilin ku nayin hakan ba ,kuma ke Kika koya wa momma, ko dayake dama ance zama da madokin kanwa.....ta zumbura baki kaman Yana kusa da ita tace Ya ya , shikuma yace yes ai gaskiya na fada my little girl.....bani momma din nayi mata magana
"Jiddah tace toh" ta mika wa Momma phone din.
"Assalamualaikum momma ta furta bayan ya amsa ne yace "Momma na fito agida yanzu Ina shikenan abinda kuke bukata?"
"Momma tace eh sai ka karaso kawai" okay momma Faisal ya amsa sannan ya kashe wayar.
Momma ta dubi Jiddah tace, Jiddah nikam ki daure ki karasa shan fruit salad din kafin Yayanki ya kawo breakfast kinji......Amma Jiddah ko gizau kaman ba da ita ake magana ba,
Momma tace Jiddah wai nikam ba dake nake magana ba,and kikamin shuru ki daure kici kinji Jiddah na.
Jiddah tadan yi ajiyar zuciya Wanda yasa Momma dauka kaman ta sauko ne daga kan mulkin data hau tun jiya tunda ta farfado ta duba bataga sojan nan ba, toh shine tafara rigima ita ala dole mezaisa su Fatima su barshi ya tafi bayan bata warke ba, Harda cewa Ina shi yaji mata ciwon toh ae bai kamata abarshi ya tafi hakanan ba, after all ai ciwon bai warke ba so babu inda yakamata ya tafi, sai kuma hawaye kuka kaman karamar yarinya wai ita sai an nemoshi kafin zatayi shuru.....ajiyar zuciya momma ta kumayi alokacin data tuna sai da suka kira Ummi kafin Jiddah ta yi shuru, amma dukda haka batayiwa kowa magana har su Fatima da mamanta suka tafi dayake maman tazo daukar ta...Momma ji tayi Jiddah na cewa Momma Abba, Abba zan kira kafin naci wani abu banji muryar shiba tun jiya.
Ya ilahi! Cewar Momma aranta tace another problem,afili Kuma sai tace call him Jiddah nikam rigimar ki ta ishe ni.
Jiddah ta tura baki kaman mai Shirin yin kuka jin ance rigimarta yayi yawa tace Sorry my momma please karki bata rai da Jiddah, ai wannan sojan ne yasa raina ya bace shiyasa amma ni bana so ranki ya baci ta karashe maganar tana kokarin dialing contact din Abba.
Momma tai shuru tana kallon Jiddah so da dama haka Jiddah take tana da shagwaba, amma batada raina na gaba da ita sai dai idan kayi mata ba daidai ba, Amma halayenta masu kyau yawa garesu don saika zauna da ita kake fahimtar ta dakuma kyawawan halayenta..... Momma tai saurin cewa to karki kira Abba yanzu, zaki tada masa hankali ne kibari sai Yayanki yazo kinji.

Jiddah ta zumbure karamin bakinta tace shikenan....sosai Momma tayi ajiyar zuciya wanna karan dan tasan da ta bar Jiddah ta kira Abba da drama da za'ayi sai yafi na jiya ahankali take bata fruit salad din har ta shanye.....kana ta sauka daga kan gadon tace Momma zandan zagaya waje na motsa jiki na dawo...... "Momma ta zare idanu tace Jiddah motsa jiki dai" naga ko agida ke bame son fita ko tsakar gida bace and yau kuma........
"Momma please"
Okay toh kije amma kada ki dade iyakarki area dinnan kada ki wuce wajan kina jina.
"Eh Momma ta amsa tayi waje da sauri abinta,
Momma ta girgiza kai tana cewa Jiddah hmmm tana tuno yanda akayi drama kafin iyayenta suka yadda ta amso Jiddah, dukdama Jiddah na tsananin son Momma hakan yasa ta yadda ta biyo ta kd.....tashi tayi tana gyara ward din.

Jiddah na fita tayi hanyar wani corridor har tayi nisa ta fita waje kaman ance ta waiga hannunta na hagu, tsaye ta hango su, ahankali tace wancen kaman Yaya Faisal.....ta kuma kai dubanta gareshi, Sanye yake da uniform na police black trouser sai shirt din royal blue ayayinda shoulder dinsa ke manne da star har uku, Dogo ne sosai kuma black in completions sai dai kallo daya zakai mashi kasan fulani ne yanayin gashin kanshi mai laushi Kuma ya kwanta hade da saje Mai kyan gaske wanda yasha gyara kuma ya kara fito da asalin kyan nashi dukda force ba'a cika son suna barin gashi any how ba Amma shi babu ruwanshi....  Jiddah tasaki ihu da karfi tace Yaya Faisal cike da murnar ganinsa" shima damamaki ya kalli wajan da aka kira shi nan ya ga Jiddah ce dukda yana mamakin ganinta awaje haka how comes tabar ward din ta fito waje kuma, Amma hakan bai hana shi yin murnar ganinta ba, murmushi ya sakarmata yace Jiddah
Tunda ta karaso wajan tafara zuba kaman an sa mata  battery,tace" Yaya Faisal tun day b4 yesterday ban sake ganin ka ba, yauwa dama akwai aikin danakeso kamin Yaya "Faisal dake sauraronta yayi murmushi yace wani irin aiki Jiddah? Jiddah ta numfasa sannan tace wai daman wannan sojan daya jimin ciwo nake nema, so nake idan na kamashi ka tafi dashi police station  ka kulle minshi har sai na warke sannan ka bude shi, Yaya Faisal ji hannuna fah tun jiya yake min ciwo bana iya motsi dashi sai kuma ta saki kuka wanda idan kaga yanda tayi reacting dole tabaka tausayi tana cewa Allah sarki hannuna, shikenan na koma mai hannu daya....taja majina ta goge hawayen fuskarta sannan ta cigaba dacewa Yaya Faisal zaka tayani neman shi don Allah muje mu kulle shi saboda yaji min ciwo, Ni bazan raga mishi ba kuma sai na koya mai hankali tunda yasan halin danake ciki kuma ya tafi ya barni maimakon ya tsaya awajan har sai na warke.....uhmmm ai ya kara ma kanshi laifi,yanzu laifinshi 2✌️ tayi nuni da dayan hannun tana gwadawa wanda yake tare da Faisal ayayinda takai dubanta ga fuskarshi ita ala dole tana basu labarin abinda wancen guy din yayi Mata, Amma me zai faru......kallon shi tayi at thesame time hannunta na nuna alamar ✌️, zare idanu tayi lokaci daya sannan tace da karfi Yaya Faisal wannan ne, wlhy shine wanda yaji min ciwo ka kamashi kada ya gudu Allah shine yaji min ciwo jiya......kana ta kalli sojan tace kaine Allah, sai kuma ta murguda masa baki hade da harara sannan tace zaka sani yau, bakai ka iya guduwa ba, baka iya tsayawa ka wanke laifin ka ba,yau zaka gane ai....dama nace bakasan wacece Jiddah Junaid ba, Amma still ka tafiyar ka ko ajikinka Koh to sai nasa Yaya na ya kulle mun kai, inga ta inda zaka kara guduwa, ta tura baki gaba tana kallonshi daga sama har kasa, sai kuma tace kana ji koh ni babu ruwana da wai ka sanya kayan soja wama yasani ko aro aka baka kayan, ko kyau ma basuyi maka ba ai gwanda ka cire........ta kalli Yaya Faisal da hankalinshi ya gama tashi tace Yaya Faisal kabashi shawara idan ka kulle shi kace mishi uniform dinnan baya mai kyau ta fada cike da nuna seriousness a fuskarta.
Sosai abin da Jiddah take Fadi wa bawan Allahn nan ya tsorata Faisal duk da yasan halinta Amma hakan bai hanashi kara mamaki ba, don wannan sojan ma ko da police officers ne to ya fishi rank taya ma zai iya kama shi har ya kulle shi, ita Jiddah bata ganin rank dinshi ne shine fah commander na hospital din, dayan zuciyanshi tace dashi to ai bata sani ba shiyasa, karkayi blaming dinta.....lokaci daya yaji ba laifin Jiddah bane Amma yasan yaddah zai yi handling dinta.
Ya kalli Jiddah wacce sai faman hararar sojan take yi tana murguda masa baki, ya dafe kanshi yace ya Ilahi! Sannan ya kalli Hafiz da tun da Jiddah ke magana yake ta kallan ta yana mamkinta....hannayensa sanye cikin aljihun wandonsa Faisal shikanshi sai da ya yaba da irin kyan da uniform din sukai ma Hafiz donshi tunda yake bai taba ganin wanda kakin soja ya amshi jikin shi sosai ba sama da Hafiz.....Amma lokaci Daya Jiddah ta kushe shi.....Ajiyar zuciya yayi hade da dafa shouldern Hafiz yace am sorry sir she is my sister and on behalf of her Ina bada hakuri batasan ko kai waye bane shiyasa take fadan haka,Am so sorry sir.

Hafiz ya girgiza kai Yana murmushi lokaci daya Kuma kyan fuskarshi ta bayyana karan hancinshi ya fito sosai ya dubi Faisal yace don't worry i understand.... anyway ni zan koma office yanzu idan kana bukatar wani abu ka sameni a office dina....abinda yace kenan kawai ya wuce yana kallon Jiddah wacce take kallon shi cike da tsana a fuskarta....har sai da ya bacewa ganinta ta dubi Faisal tace Yaya Faisal why?

******************
Vote
Comment

Continue Reading

You'll Also Like

126K 7.2K 45
Complicated🤐🤐🤐 Find out👇👇👇
1.4M 117K 110
Kalmar QADDARA kalma ce dake rataye bisa wuyan kowanne bawa,haka rayuwa ta gada,tafe take da QADDARORI kala kala,masu zaqi da akasin haka...
10.8K 504 16
***Tsokaci Duk tsananin zurfin ciki akwai inda za'a tadda qashi... Aka ce Shure Shure Bata Hana mutuwa... A juri zuwa rafi lallai watarana dole a fas...
17K 882 32
DR UMAIMAH USMAN BULAMA,Mace yar kimanin shekara ishirin da tara , Babbar surgeon A asibitin CITY TEACHING HOSPITAL , Aure Uku, ƴaƴanta uku . Mace m...