Babi na dari da d'aya

18.5K 1.3K 243
                                    

*Bismillahir rahmanir rahim*

*Allah S W T yana cewa cikin qur'aninsa mai girma*

*IDAN ZAKUYI UQUBA KUYI UQUBA DA GWARGWADON MISALIN ABINDA AKA YI MUKU UQUBA DA SHI(ma'ana idan zaku rama wani abu da aka yi muku ku rama gwargwadon abinda mutum yayi muku babu qaari)IDAN KUKAYI HAQURI SHINE MAFI ALKHAIRI GA MASU HAQURI*

Sadaqallahul azim
__________________________________

         Da fari labarin dariya ya dinga bashi,quruciyarta ta dinga burgeshi tana masa dadi,ya dinga leqa fuskarta yana tsokanarta,a hankali sai yanayin ya sauya ya koma na kishi,zallahn kishin mukhtar,yayi shuru yana saurarenta,daga bisani kuma sai mamaki ya bijiro masa,tausayi shi ya zama abu na qarshe,kafin ta gama bada labarin saiga hawaye shabe shabe kan fuskarta,yayin da zuciyar almustapha ta dinga motsawa,ji yake kaman ya dawo da hannun agogo baya,kamar ya dawo da baya ya ciro fa'iza zainab har ma da karima ya hukuntasu,lallai dole ta dauki eesha ba a bakin komai ba,tausayin abdallah da qaunarshi suka kamashi,ashe maraya ne,marayan da tun kafin ya iso duniya ya fara fuskantar qalubale na rayuwa,lallai dole yayi maganin eesha,bazai yarda ta sake fuskantar irin wannan rayuwar ba.

       Dubanta kawai yake bayan ya gama rarrasarta,mamakin irin rayuwar da take kawai yake,saidai zuciyarsa cike take fal kishin dukka mazajenta,ina ma ace shi ya fara samunta tun a wancan shekarun,da lallai ba shakka bazai bari tayi irin wannan rayuwar ba,saidai kuma qaddara data rigayi fata,ko a hannunshin ne tunda yazo cikin KUNDIN QADDARARTA dole hakan ya faru da ita.

        Kwanansa biyu cikin gidan baya fita ko nan da can,wata sabuwar rayuwa mai cike da soyayya da qauna suke shimfidawa cikin gidan,wata kulawa sumayyan kr bashi wadda ada can bai taba hakaito ta iya bawa miji kulawa kwatankwacin haka ba,duk sai ya narke ya koma wani shagwababben qarfi da yaji,jinsa yake tamkar qarakin yaro,irin soyayyar da yake hasashen samu ga matar aurensa ita yaje gani zallarta ba algus,shima baiyi qasa a gwiwa wajen bata kulawa ba,ji yake kaman ya lasheta ita da abinda ke cikinta,sau tari yakan sata ta saka qananun kaya kawai don yaga zaman cikinsa a jikinta,wata qimarta ke dada hauhawa cikin zuciyarshi,ta zama wata ta musamman cikin rayuwarshi,labarinta ya tsaye masa a wuya,yana jinjina mata yadda ta fuskanci duk wani qalubale na rayuwarta,yaci alwashin sai ya shafe duk wani tabo da yayi saura qasan ranta da qarfin qwanji da na zuciyarsa.

        Randa suka cika kwana uku a gidan,bayan sallar magariba ne,yana zaune a falo sanye da gajeran wando da vest duka farare qal,qafafunshi harde yana kallon wrestling,fuskarshi qunshe da murmushi duk da ba abin dariya ake ba a allon t.v,yayi shiru yana sauraren fitowar sumayya daga kitchen,wanda yasan me ya qulla maya shi yasa yake dariya,kukan shagwabarta ya jiyo tana fitowa a kitchen din,sanye take da vest itama da wando iya gwiwa baki dayansu blue da pink,kayan sun fito da cikinta muraran ya zauna das a jikinta,gashinta na daure a ribnom qwaya daya ya sauja bayanta sai qyalli yake,wanda aikin almustaphan ne shi ya gyara maya shi dazu da yamma,waiwayowa yayi yana kallonta hadi da qunshe dariya ya dage gira ya ware mata hannayeshi alamun ta taho
"Babe....me ya faru?" Harararshi take tun kafin ta iso
"Nama na.....ina nama na?" Sake qoqarin boye dariyarshi yake ya soma zagaya idanunshi sannan yace
"I think akwai bera ko mage fa gidan nan,dazun naji motso a kitchen may be su shuka janye" sai ta sake sakin kuka ta fado jikinsa a hankali,da sauri ya tarbeta yana sakin dariya,ya cusa hannunshi bayanshi ya ciro kwanan ya dire mata
"Hala baki kallon mudubi....gaba daya kina cin nama yana komawa kumatunki yana zama" ya qarashe yana dariya,dariya itama ya bata,sai ta harde hannayenta tana kallonshi
"Okey.....yanzu ya kake so ayi,na daina ci kenan?" Hannunsa ya daga sama
"Ni bance ba,ci abinki tunda baby na so...." Magananshi ta katse sanda wayarshi ta dauki ruri,ummi ke kira,sai ga miqa hannu ya dauki wayar yayin da ya maqaleta a kunne,ya soma bude plate din yana motsawa sumayya naman don ya huce yadda zai mata dadin ci.

KUNDIN QADDARATAWhere stories live. Discover now