Babi na casa'in da hudu

16.6K 1.4K 356
                                    

*Bismillahir rahmanir rahim*

*Allah madaukakin sarkin yana cewa*

*CENE DA SU HARAM DA HALAL BAZAI DAIDAI BA,KODA KUWA YAWAN HARAM DIN NAN YA QAYATAR DA KAI(KO YA BAKA MAMAKI),KUJI TSORON ALLAH YA MA'ABOTA HANKULA DON KU RABAUTA*
_______________________________________

        Tamkar wanda aka jefo haka ya shigo dakin,hantar cikin sumayya ta kada,sai ta sake qudundunewa a zaune ta cusa kanta tsakanin cinyarta,muryarsa taji saman kanta cikin wani irin amo
"A ina kika samo wannan cutar,ba dake nake ba" tsananin rudewa ya sanyata daga kai ba tare data shirya ba,abun mamaki fuskarsa wani annuri take fitarwa,kafin ta kai ga yunqurin komai ua sureta baki daya ko nauyinta baiji ya soma juyi da ita,qanqameshi tayi sosai hawaye na zirya saman kumatunta,batasan me take ji ba cikim zuciyarta zuwa yanzu,ciki?,ciki kums ita din?,tayi zatombdaga abdallah ta gama,shin da yaya ma aka samu abdallah?,ciki jin abun take tamkar almara,a hankali ya direta saman kujera ya duqa bisa gwiwoyinshi baki daya,hannunsa ya sanya cikin nata tafin hannun yana matsawa,sai motsa bakinsa yake amma ya rasa kalmar da zai furta,ita din ma shi take kallo,tunda suke zata iya rantsewa bata taba ganin annuri saman fuskanshi kaman haka ba
"I dont know me zan fada,ummu abdallah......pls idan mafarki nake taimakeni ki tada ni,i cant blieve it" sai ya kasa zama ya miqe daga durquson da yayi,ya kama hannunta tsam ya miqar da ita,bai tsaya ko ina da ita ba sai clinic din cikin gidan,ya hau nuna mata gwajin da yayi,itakam ba abinda ta gane tunda ba bangarenta bane,jin tayi shiru sai ya daga ta baki daya ya aza saman gadon scanning,ya kunna na'ura ya daidaitata sannan ya janye rigar dake jikinta ya dora na'uarar bayan ya zuba cream saman cikinta
"Ya salam.....ya salamm....oh my god..." Abinda ya dinga maimaitawa kenan yana ci gaba da yawo da na'urar saman mararta yana kallon allon scanning din,cikin wani irin sanyi ya gyaara mata rigar bayan ta dagata ta zauna sosai,ga mamakinta hawaye ne fal idanunshi,ya Allah wanne irin so yakewa haihuwa haka?,tamkar yaji abinda take rayawa a ranta ya soma girgiza kai
"Bansan ina son haihuwa har haka ba sai a yanzu,da gaske ne nima ashe zan iya zama uba?,zan iya ganin jinina?" Tamkar ita yakewa tambayar da ita kanta bata da amsarta,hannunshi ya dora saman mararta
"Alhamdulillahil lazi bi ni'imatihi tatimmus salihat" ya furta hadi da fitar da nannauyan ajiyar zuciya,har a lokacin juya lamarin take cikin mamaki
"Ki tambayi duk abinda kike so a duniya zan mallaka miki shi matuqar mallakata ne please,ki roqeni ina son ko yaya ne na faranta miki nima..."ya fada yaba matsa yatsun hannunta
"Baki ce komai ba ummu abdallah....ko baki murna....ko ba zaki iya ba kaman yadda kika taba gayan a dubai?" Da hanzqri ta girgiza kai
"Bana son komai,kawai ki riqe amanata,kada ka wukaqanta ni,sannan nima bani ke badawa ba ai Allah ne ya baka"
"Ya bani ko ya bamu?....kada dai kice min har yau babu wani matsayi da na taka cikin zuciyarki?" Murmushi ta saki,sai ya sake matsowa tare da yin dan tsalle ya haye shima gadon,duka hannuwanshi ya sanya ya kamo fuskarta
"Tell me wanne matsayi ke gareni?.....bana son baby na yazo duniya ya fuskanci babanshi is nothing" so take ta qwace fuskarta saboda yadda yake azawa qirjinta nauyi da yawa amma ya qiya,sai ya koma magana da gaske
"Am seriouse madam,am not even hear you kina fadin i love you,baki taba fada ba,why?"
"Ba komai" ta fada a sanyaye
"Bakya sona?" Ya sake tambayarta,shuru ta masa zuciyanta na bugawa,wannan tambayar titsiye ce kawai,ta yaya zaiyi wannan maganar
"Sumayya!" Ya kira sunanta karon farko a rayuwarsu cikin wani irin taushi wanda ya tilastata daga kai ta dubeshi
"Bana soyayya da wasa kowa ya sanni,idan nace ina son abu zan tabbatar da hakan har daukewar numfashina bana canzawa,sonki na tabbatar bai shiga rayuwata don ya tafi ba,na fara sonki a lokacin da ni kaina ban sanshi ba......kin shigo rayuwata da tarin alkhairan da banga kamarsu ba..." Shiru yayi yana maida numfashi sannan ya dora
"Gaya min kina sona indai kina son naci gaba da rayuwa" kunya ta kamata,tana yunqurin kau da kanta ya sake tallafe fuskar
"Nooo,a yau a wannan muhallin bana buqatar kunyarki.....ki gayan abinda nakeso naji"
"I....love...you" ta fada ararrabe cikin muryar rada,idonshi ya lumshe kalmomin na ratsashi tamkar ranar aka soma gaya mishi su
"Basu gamsar da ni ba.....please.....i need more"kafeshi tayi da idanu sanda nashi idon ke lumshe,tana jin yadda wani feeling da so mai zafi ke ratsa jininta,qaunarsa na fusgarta da wani irin qarfi
"ina sonka da dukkan zuciya ruhi da gangar jikina.....ban taba jin so irin wannan ba a duniyata sai wannan karon,na tabbata kai na dabanne shi yasa Allah ya jarrabeni da qaunarka.....ina sonka baki dayanka bawai wani abu da ka mallaka ba....kai din dai zallarka kai nake......." Idanunshi da ya bude tar tsakiyar nata shi yasa ta gaza qarasa furta abinda take son fada,zallar soyayyar da take gani a qwayar idanunsa kadai ta isa sake narkar da masoyi
"Wani irin zazzafan so nake miki ummu abdallah....taba qirjina kiji yadda ya sauya bugu daga jin kalamanki" ya kama hannunta yana mannawa a qirjinsa saitin zuciyarsa,ba shakka bugunta ya sauya,da mamaki take dubanshi,da gaskene mutane masu tsananin miskilanci da rashin lura da sabgar wasu,yawan shiru basu iya fadawa tafkin soyayya ba?,ta tabbatar da cewa irin son da take gani cikin qwayar idonsa da wanda yake furta mata ba irin nata bane,jikinsa ya janyota yana sakin qatuwar ajiyar zuciya
"Na gamsu da kalamanki matata,uwar 'ya'yana da yardar Allah" kusan awa guda suka bata cikin dakin suna jaddada kalaman soyayya tsakaninsu,wanda wani abun almustaphan bai taba tunanin shi kanshi zai iya faruwa ba tsakaninsu,kusan ya samu yadda yake so,irin soyayya da kulawar da yake muradi.

KUNDIN QADDARATAWhere stories live. Discover now