episode 2

649 27 0
                                    

AURE UKU

         BY

     CHUCHUJAY✍🏽

EPISODE 2⃣.

    Idan kana bibiyar labarin Rayuwar Umaimah zakace Shin dama masu kuɗi ma suna samun kalubale a rayuwarsu duk da kuɗinsu?

Zaka na tunanin tayaya Umaimah zata jure dukkan wannan Abun bayan mahaifinta sharararen Mai kuɗi ne!

Abun ba Haka yake ba,sau da dama kana da kuɗin da komai amma muddin Allah bai so ba baza ka ji daɗi ba tawani bangaren ,Ya 'dan ganta da kaddarar ka,

    Auren dake tsakanin umaimah da bilal bai wani lasting ba saboda irin sharrin da suka haɗu suka haɗa mata,

Tana kwance kan Gadonta tana bacci ta tsinkayi hayaniyar mutane akanta,koda ta farka mijinta da mahaifiyarsa da matarsa ta gani a gefenta sai gefe guda wani ƙato da bata taba gani ba a rayuwarta kwance kan gadanta!

A ranar suka mata wulakancin da ta kasa mantawa a rayuwarta wato kazafun zina wanda ya Kai har bilal Ya ke tantamar kasancewar Nadiya yarsa ,duka bilal yayi mata sosai da belt wanda sai da Ya farfasa mata jiki kana ya sake ta saki biyu,

Abu na farko kenan da yaje kunnen Alhaji Bulama wanda yayi mutukar harzuƙashi,

Kuka sosai umaimah Take masa tana Mai masa rantsuwa akan bata taba Aikata zina ba hasalima ita bata san mutumin da ta farka ta gani a gefenta ba,

    Mahaifin bilal Ya kira wanda baida masaniyar Mai ke faruwa saboda Ya rabu da mahaifiyar bilal,

Kwata kwata Alhaji bulama bai tsaya yi masa da sauƙi ba saboda yarda ranshi Ya baci,hakuri Alhaji muntari Ya bawa Daddy saboda shi bai masan wainar da ake toya wa ba,

Gudun kar zumuncinsu ya lalace yasa Alhaji Bulama yace masa zai bincike sannan yana so Ya fitar da hannunsa akan duk abinda zai biyo baya dan muddin Ya gane bilal ne baida gaskiya sai Ya ɗauresa.

DNA Ya fara sawa akayi conducting akan Nadiya da bilal wanda Ya fito 99% positive,

Da bincike yayi bincke aka gano haɗine na matar bilal da mahaifiyarsa ,baki ɗayansu Alhaji Bulama Ya daure a yayinda yasa a bawa bilal mugun kashi ladan dukan da yayi wa yarsa sannan yamasa haramiyya da NADIYA.

Haka nan ta cigaba da zama a kano 'dan karasa karatunta wanda a lokacin tafi yinsa cikin kwanciyar hankali ,

A shekarar da ta gama karatunta ta haɗu da Hafiz matashin Mai arziki wanda haduwar farko Ya nuna mata soyayya ,ita macece da bata taba soyayyar ɗa namiji ba sai akan Hafiz ,

A hankali soyayya Ya kullo tsakaninsu inda baki daya bata ganin aibunsa musamman da yasan tana da yara biyu Ya amince da daukan su idan sukayi Aure ,

Da kalamai masu daɗi Hafiz yasa umaimah ta saki jiki dashi sosai,

Bayan ta gama karatunta ta samu licence na fara Aiki takai Hafiz gidansu a matsayin mijin da Take san Aure,

    Kiranta Daddynta yayi Ya zaunar da ita Ya tambayeta akan gamsuwarta da Hafiz sannan Ya jaddada mata shi bazai sake ce mata ta Auri kowa ba idan tana so ma zata iya cewa bata so baki ɗaya bazai ce mata dan me ba,

Nuna masa tayi ta gamsu da hafiz wanda shima a hankali bayan binciken da yayi akansa Ya bada yardar sa akan Aurensu,

    Da shagalin Aurenta da shagalin murnar samun aikinta Alhaji Bulama Ya haɗa mata gagarumun biki .

Kamar yarda Hafiz yayi mata Alƙawari kuwa Haka Ya ɗauki Nameer da Nadiya matsayin nashi,

Lagos suka wuce tare duba da yarda kasuwancin sa Ya tarkata chan,inda ita kuma ta fara aikinta cikin kwanciyar hankali.

AURE UKU(completed)Where stories live. Discover now