BABI NA HAMSIN DA SHIDA

337 110 25
                                    

BABI NA HAMSIN DA SHIDA
Cikin wani irin azababben zafin nama yake yakar su, kamar ba bako ba. Irin yakin nan da ake yi dan kare kai wato (self defense) haka yakar su, tsabar tsoro ko bude idanu bata yi ba, sauran mayakan gani yana kokarin kar su, yasa suka juya a guje, taka dutse yayi ya murza tare da cillata da kafa, ai kuwa ta samu keyar dayan su, faduwa yayi yana rike kan shi. A hankali ya sake takobin ya kunce ta daga jikin shi fincikota yayi har zuwa lokacin bata bude ido ba, ai kuwa ya damke rigar ta gaba sannan ta cillata, kamar wata bushashen ganye haka ta gibgu da kasa ji kake timmm.

"Wayyo Allah na katarya ta!" Ta rike kugun ta, tana me bude idanun ta. Ganin shi tsaye yana nad'e fuskar shi , kallon yadda yayi mugun barna yasa yasa ta ce.
"Amma kai daga duniya makasa kazo ko? Da yanzun na mutu waye zai biya Ni mutuwa ta? Kawai ayi mutum bai da burbushi imani, salon na mutu a saka shanuna kuka."

Rike baki tayi tana kallon yadda wurin ya b'aci da jini, bata san lokacin da ta fara kwara amai ba, sabida karnin jinin da ya kaure a wurin.

Aikuwa shanun suma munafukai suka ce "muaaaaah!"
A wahale ta ce musu
"Ai na sani bayan ku babu me min kuka ko na mutu"
Bai damu da zanttukar ta ba da kuma halin da take ciki ba, dan yasan dole haka ta faru, kawai abinda yayi shine zuwa wurin mutumin ya riko wuyar shi, ya D'aga shi cak. Rike bakin ta tayi tana kallon rashin imani irin nashi.
"Waye ya aiko ka?"
"Anum aka turo mu kashe don Allah ka min rai wallahi ina da iyali don Allah kayi hakuri"
"Waye ya aiko ku?"
"Mahaifiyar Yarima Barkindo!" A hankali ya ke juya sunab barkindo kafin ya juya ya kalle ta, sai wani cika take ita nan an nime kashe ta.
Mikewa yayi ya fara nad'e kayan shi yana daurawa akan dokin shi, sannan ya haura saman dokin zai wuce.
"Kai barawo kazo nan wallahi baka isa ba, idan na yarda wutar lahira ta ci ni, ba zaka tafi ka bar ni anan inda yake cike da dangin ka makasa ba"

Dan ita har yanzun gani take satotta yayi shi yasa take kiran shi barawo. Janye mayafin fuskar shi tayi ya watsa mata harara.
"Sai idanun sun fado ƙasa zan fahimci kana harara ta, malam saukowa zaka yi ka mai dani inda ka dauko ni" ta tsaya a gaban dokin shi.
Sauka yayi ya riko linzamin dokin ya fara tafiya a hankali, itama ta kad'o shanun ta, suka fara tafiya.
"Allah sai ya saka min cinye abincin da kayi baka bani ba, kuma su wadancan da ka sare su waye zai mai da su gida, kana bako kazo zaka jangwalo mana damuwa, gaskiya ban yafe ba wallahi dole ka nima min abinda xan ci"
Juyawa yayi a fusace, tona aika-aikan da yayi yasa ta, kasa da murya tana faɗin.
"Allah ya baka hakuri" bai kulata ba yayi gaba abin shi, aikuwa ta bi bayan shi da harara. Juyawa yayi ya kamata tana hararan shi bai bi takan ta ba, sai dai yanayin garin da haka kawai ya soma hada hadari yasa shi. Niman irin manyan duwatsun nan da suke a wajen gari(wato mountain) ya shiga zaga cikin shi. Kaf ya duba babu kome sannan ya koma ya dauko dokin shi suka shiga kokon dutsen, ita da shanun ta suka ki Shiga, gani take kamar tana shiga zai mata wani abu shi yasa taki shiga, aikuwa aka fara ruwa kamar da bakin kwarya, fitowa yayi yana kallon ta a tsugune duk sanyi ya dame ta, fita yayi a cikin ruwan can sai gashi da ƙaruwar gada, da kirare ya shiga abin shi ko ta kanta bai bi ba, ya haɗa wuta ya turara kokon sanan ya fede gadar ya shafe ta da gishiri da garin citta da Innayoh ta hado mishi da dan barkono kaɗan, sai yar man shanu shi da ya shafe gadar da shi, ya bankare fadar ya haɗa kome ya hura mata wuta sosai, kallon bakin kokon yayi yaga tana leko kai, bai wani kuma damuwa ba, shi kan ma mamaki yake yar yarinya karama irin ta aka turo a kashe toh me tayi musu?
A hankali kamshin gashin ya fara daukar hankalin na kusa, tun tana iya jure kamshin har ta kasa sai wani sosa soshe take, kai karshe sai gata a cikin kokon ta zauna a gaban wutar tana hàdiye yawun, warware mayafin fuskar shi yayi yana kallon yadda gashin yake daukar kamshi, hàdiye yawun tayi tana kallon lokacin da ya ciro wukar shi ya yanki suka ya duba yaga babu ruwa da jini, sakawa yayi a baki yana taunawa a nutse cikin wani miskilin yanayi yake lumshe idanun shi, yana jin wani dadi da dandano har yana saka kunnen shi rawa,

Sake hàdiye yawun tayi tana motsa bakin ta, tare da gyara zama tana marairaice fuskar ta.
"Allah yana son masu kyauta da bada abinda bai..."
"Kurrrrrrr!" Cikin ta ya bada sauti, kallon shi tayi ta kara marairaice fuska.
Yankar naman yayi sosai ya koma gefe ya zauna yana ci a hankali, ganin yadda yake ci hawaye ya shiga zuba mata cikin shashekar kuka ta ce mishi.
"Don Allah yunwa nake ji" d'ago kai yayi ya zuba mata ido, kafin ya mai da idanun shi kan wukar, itama wukar ta kalla ta mike da sauri ta fara yankar namar jikin ta yana rawa, da wutsiyar ido yake kallon ta, har ta gama ta koma gefe ta fara cin namar, d'ago kai tayi tana kallon shi yadda yake cin namar, kamar bashi ba. Har ya gama ita kan sake karawa tayi yana kallon ta bai hana ta ba, sai da ta gama ta koma gefe jikin ta ta mutu. A hankali ta shiga barci.
Shima kwanciyar yayi yana jin barci, sabida sanyin da ake ga ruwan da ake kwararawa, har barcin shi ya fara nisa. Yaji shashekar kukan ta, bude idanun yayi zuba mata,kafin ya tashi zaune ya ciwo mayafin shi ya lullube ta, sannan ya koma ya kara hada wutar sosai. Sannan ya fita yana duba dabbobin ta. Duk suna nan lafiya lafiya, sannan ya koma yayi alola kafin ya gabatar da sallah azahar, yana kallon har lokacin barci take yi.

Mamaki da barcin ta yake, wuni guda tana barci yayi kokarin tashin ta, amma bata farka ba, ai dole kodan wannan yawon da tayi tayi babu barci, shi yasa bai kuma D'aga ta ba, sai wurin tsakiyar dare ta farka, ta hango shi zaune akan buzu yana karatun Alqur'ani. Kama mayafin tayi tana kallon shi.
Kamar zata ci babu haka ta farka da mugun yunwa, ganin ruwa a gefen ta a cikin goran ruwan shi tayi alola tare da fita waje yaga garin yayi duhu ga sanyi, dan haka ta dawo kokon ta gabatar da sallah tana idarwa ta juya wurin naman da ya saura ta dan kalle shi aikin hankali tayi ta yanki kadan ta bar mishi sauran. Dan haka taci ta koma ta kwanta. Barci me nauyi yayi gaba da ita, sai da ya kara dumama kokon ya kwanta.
**
"Ki min rai! Wallahi wani mutum ne ya taimaka mata, ya kashe kowa da kowa don Allah kar ki kashe ni ina da iyali"
"Ku fitar min da shi" bingel ta bada umarnin a fitar da shi, juyawa tayi tana kallon Mandiya.
"Ta ina zan samu damar kashe ta? Na tsani yarinyar nan"
"Ni kuma ina son ta! Ina kaunar ta innah idan wani abu ya same wallahi ba zan yafe ba, ashe dama kece sanadin b'atar ta?"
Ya tambaye ta yana ihu, bata kula shi ba, amma kuma ranta ya b'aci.
"Zan tafi niman ta" ya fada bayan ya juya dan yasan tunda ta mishi shiru ba zata tab'a kula shi ba. Dan haka ya bar gidan cikin fishi.

Hana shi fita aka yi dan dole ya hakura.
-
A can kuwa suna barci, a hankali yake jin kukan dokin shi bude ido yayi yq dauki takobin shi da bakin wuta ya fita, hango shanu yayi suna guje guje kura ta saka su a gaba,
"Keee!!!" Ya daka mata tsawa, da gudu suka bar wurin ya manta ne bai daure dajin daga dabobbi ba, dan haka ya kama ganye da sauwar shi, ya daure dajin tsaf sannan ya shiga ya ga yadda take barci, juyawa yayi ya kwanta akan buzun shi, har asuba tana barci sallah yayi ya fita farauta.
Koda ya dawo ta hanyar ya gane wasu sun shiga cikin kokon dan haka yana shiga ya hango irin arnan dajin nan, sun rufa akan ta sai dambe suke. Bai kula inda suke ba sai ma aikin da ya tsiro yi, ganin haka suka juya gare shi da sun san ma'anar shirun shi da basu fara wannan kuskuren ba, kawanya suka mishi, kura mishi Idanu suka yi tare da kai hannu suka Safar kadadar shi....
*Lalaci nake ji😿💔🔥*
#Mai_Dambu

KALLABI..! A tsakanin Rawuna...Where stories live. Discover now