47_48

921 44 8
                                    


🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥

WUTA A MASAƘA

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)

The experience writer of

*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA)
*BAƘIN TABO (Labarin gasa)
*AƘIDATA (Paid Book)
* WUTA A MASAƘA

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in

❌❌❌
Ƙirƙirarren labari ne, ban yadda ayi amfani da kowane sashi na labarin ba ba tare da izinina ba.






47_48



Gaba ɗaya suka mai da hankalin su kan ta, ta yunƙura zata bar falon amma abun yaci ƙarfinta, haka ta tsaya ta yi shi a falon.

"La'ila ha ilalla la, Muhammad rasulillah Sallallahu alaihi Wasallama, Imran me nake gani haka? Ba dai ciki ne da Yarinyar nan ba?"

Gaba ɗaya Imran ya dirirce yace 'Amm, mm dama, dama fa bata da lafiya Ammi, ba ta jin daɗi jiya har Asibiti muka je aka ce typhoid ne da ulcer ke damunta"

"Zan ɗura maka ashar ka kuma nema ka rainamin hankali, uwar typhoid ɗin da uban ulcer, kalli yadda yarinya ta ɗashe, tai haske amma kace min ulcer"

"Allah Ammi ba su cemin ta na da ciki ba"

"Rufemin baki, ni zaka rainawa hankali, wannan uban aman da tai ne za ka ce wai ma malaria ne, ka kyauta ds tsallake umarnina Imran, amma ka tabattar ka nemwa ɗan da zata haifa wata kakar ba ni ba, dan ba zan karɓi ɗan da ya fito daga tsatson karuwai ba, dan bani da tabbas na ka ne ko ba naka ba"

Duk da Amira na fama da kanta, dan a inda ta gama amana, ta kwanta akan kujera, gaba ɗaya jikinta yai sanyi, gaɓoɓin ta na mata ciwo, ga wani irin azababben ciwon kai da jiri da ke damunta.

Ihsan kuwa ɓangaren ta tayi da sauri, tana kuka yanzu Dagaske Amira ciki ne da ita, shikenan ta tabbata Imran ya zama nata, dan yadda yake ƙawazucin ta samu ciki ba ta samu b, Amira ta samu ze sake tattare wa ne a gurinta.

Nan ta sake jinjinawa ƙarya da rashin alƙawarin maza, yanzu duk daɗin bakin nan da yai ta mata, da alwashinsa akan ba ze kusanci Amira ba, katsam se aka haihu a ragaya, wai Amira da ciki.

Ta sake rushewa da kuka hadda sheshsheƙa.

Shikuwa Imran cigaba da lallaɓa Ammi yayi da rantse rantse, "Ammi dan Allah karki sheganta abunda take ɗauke da shi, wallahi Ammi Amira ba karuwa bace ba, na rantse miki"

"Eh tunda dama taje ta maka surkullen da zatayi dole ka zo gabana kana gayamin haka, kana nufin duk gantalin da ta dinga yi, har wasu garuruwan da'awa ta tafi ko jihadi? Ina ce nan hotunan ta suka dinga yawo tana rawar gala, wace 'yar mutuncin ce za tai abunda tayi?"

"Na sani Ammi, amma maraici ne da rashin gata ya sa ta tashi a haka, amma ba karuwa bace"

"Wallahi ka kuma cemin ba karuwa bace, zan zabga maka mari, shashasha dama tunda ka saki labule da ita ai dole ka faɗi haka, kar idan ka koma ta hanaka, ka kyautawa ranka, kuma bari in naka kashedi, billahilazi duk ranar da ka kuma dukar min yarinya saboda kilaki seta bar gidanka a ranar, kuma yanzu ma ba ƙyale ku nai ba, ba zan bari a haifi wannan cikin a gidan nan ba, dan ina tantama a kansa, ka bani mamaki ka bani kunya idan har kai ke da alhakin cikin nan Imran, kuma zan maka kashedi da gargaɗi idan harka kusakura ka canzawa Ihsan, ko kai mata wani abu mara daɗi naji labari, wallahi zamu gauraya da kai.

WUTA A MASAƘAWhere stories live. Discover now