41_42

1K 67 7
                                    

🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥

WUTA A MASAƘA

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)

The experience writer of

*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA)
*BAƘIN TABO (Labarin gasa)
*AƘIDATA (Paid Book)
* WUTA A MASAƘA

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in

❌❌❌
Ƙirƙirarren labari ne, ban yadda ayi amfani da kowane sashi na labarin ba ba tare da izinina ba.

*🌈NIMCY'S LIBRARY🌈*

_Readers gareku, masu tambayar old books na NIMCYLUV SARAUTA, tayi shiru ne domin tana bada bunus kafin azumi, to Finally the day is here, tana sai da littafan ta gaba ɗaya akan 3k gaba ɗaya littafan guda 14 ne, to bisa Bunus ɗin da tayi na tsayin sati guda dukkan mai so zai biya 1500 mai makon 3k😍, nasan baku karanta littafan ta na baya ba, da am sure za kuce sunma fi na yanzu daɗi❤️🤨_

So what are waiting for.....??? Go and subscribe your own...

Abu Maleek
Sirrin mu
Uncle ne
The new emir
Izzar so
Sai na aureta😍
Tsintacciya
E.t.c guda 13 via 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 a biya asha karatu Tabbas za kuyi farin ciki littafan babu baya #Love #Romance #Destiny

Bonos ya fara 6/2/2022
Share fisabilillahi😍



41_42


Ya ajiye wayar, ya kalli Ihsan zeyi magana ta ɗaga masa hannu, "Yanzu Imran da ita za ka tafi, ina ji ina gani ka barni a nan? Ka ɗauketa ku tafi, Imran ina alƙawarin da kai min? Nasan ba zaka taɓa cikawa ba".
Tai maganar zuciyata na matuƙar tafasa.

Imran ya gyara zamansa Sannan yace "Ihsan, wallahi dan ta ni kin san ba zan ɗau yarinyar nan in ce zan tafi da ita ba, da kunnenki kin ji ai, Abba ne ya bada umarnin nan ba wai ra'ayina ne hakan ba, ki fahimceni mana".

"Ni ka ƙyaleni, ba abunda zan fahimta, wannan ai cin fuskane taya zaka je ka zauna daga ita se kai a gida, kuma hankalina ya kwanta ba abunda ze faru? Gaskiya ni ban yadda ba"

"To me ki ke so ayi? In cewa Abba bazan tafi da ita ba ko kuma yaya?, Da da bani da Aure mutuwa nayi? Ko kuma kwanakin da nayi a daji ba mace wani abu ta sameni, ke kanki da nake so in ki kamin laifi muna kwana shimfiɗa ɗaya kuma in ƙaurace miki, meyasa kike tunanin wani abu ze haɗani da ita, haryanzu kin kasa yadda dani"

Gaba ɗaya maganganun Imran jin su take a matsayin kalaman yaudara da rainin hankali, ta miƙe ta ɗau wayarta, ta tafi ɗayan ɗakin ta rufe ƙofarta.

Imran ya shafi sumar kansa, ya kwanta akan gadon, ya fuskanci idan ya biyewa matan nan zasu maida shi mara hankali, kowacce da kalar tata rigimar, ba ƙaramin kwarjini ne da shi ba ko a wajen aiki, amma idan ya dawo gida mata su dinga caza masa kai, ya ɗakko wayarsa ya hau chatting.

Yana dubawa ya ga Khalid online, yai masa sallama Khalid ya amsa yace "kai Angon biyu ya? Ka wartsake kenan?"

"Tun yaushe, zan dawo aiki ma"

Khalid yace "Haba? Yaushe zaka zo?"

"Jibi in Allah ya kaimu, zan taho insha Allah"

"Masha Allah, wannan karon kai ɗaya zaka taho ne?"

WUTA A MASAƘAWhere stories live. Discover now