43_44

1K 53 10
                                    

🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥

WUTA A MASAƘA

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)

The experience writer of

*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA)
*BAƘIN TABO (Labarin gasa)
*AƘIDATA (Paid Book)
* WUTA A MASAƘA

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in

❌❌❌
Ƙirƙirarren labari ne, ban yadda ayi amfani da kowane sashi na labarin ba ba tare da izinina ba.

43_44

Se da Amira ta saki ƙara, sakamakon yadda Imran ya janyo ta da ƙarfi sosai.

Ba sani, ba sabo, ba tausayi, ko sassauci Imran ya aikata abunda zuciyarsa ke raya masa akan Amira, ya aikata abunda yake so kansa tsaye, ba tare da wani tausayi ko rangwame ba, sedai kash duk yadda ya zaci abun ba haka yake ba, saboda abunda ya tarar ya girgiza shi ya bashi mamaki matuƙa, he never thought that Amira was virgin.

Seda ya dawo hankalinsa yaji wata irin nadama ta saukar masa, dan kusan abunda ya aikata ba shi da maraba da Fyaɗe, sedai kawai dan matarsa ce, ya kalli in da Amira ke kwance kukan nata ma ba ya fita, se sheshsheƙa da ajiyar zuciya kawai da take yi.

Hannu bibbiyu ya sa ya dafe kansa, yai shiru yana tunani daban daban a zuciyarsa, kunya da tarin Nadama suka baibaye shi.

A hankali ya kuma kallon Amira, jiki a sanyaye yace "Sannu"

Bata ko motsa ba balle ta amsa, ta cigaba da kuka.

Ya janyo bargo ya lulluɓe ta, ya miƙe jiki a sanyaye ya bar ɗakin.

Gaba ɗaya Amira ta kasa banbance a halin da take ciki, a sume take ko a farke ta kasa ganewa.

Ɗagota Imran yai daga kwanciyar da take, ya ɗaura mata towel, yana ƙoƙarin ɗaukanta amma ta bige hannunsa ta sakko daga kan gadon.

"Ki tsaya in taimaka miki mana, na kai miki ruwa toilet ɗina"

Wani banzan kallo tai masa tace "bana so"

Ta lallaɓa jikinta, ta shiga ban ɗaki, ta nemi guri ta zauna, tana zubar da hawaye.

Imran kuwa sake zama yayai yana tunani, ta yaya Amira zata zama virgin? Dama haka tana faruwa ko kuwa dai dama duk abubuwan da take ba ta aikata Zina?.

Nan damuwa ta tarar masa, ya dinga tunani daban daban, yana cikin tunanin ta buɗe ƙofar banɗakin ta fito.

Imran ya tashi da sauri ya tafi inda take, yana jera mata sannu, sedai a sannun nasa ko ɗaya ba ta amsa ba.

Ta nufi ƙofar fita daga ɗakin.

Da sauri yace "ina kuma zaki? Ki zo ki kwanta a nan, in duba first-aid box ɗina, in baki magani"

"Bana so, ba zan sha ba ka riƙe abunka Imran, ai ni be kamata ka tausayamin ba, saboda Karuwace ni da aka tirsasa ka Aura dan ka taimaka Mata, Alhamdilillah yau burina ya cika, kaine ɗa namiji na farko da na fara sani a rayuwata, kuma kaima ka sheda hakan, dan haka daga rana me kamar irin ta yau, kar ka sake kirana da Karuwa, kuma ka sanar da matarka da 'yan uwan ka ni ba Karuwa bace, abunda yake hanani maida martani idan an gayamin Karuwa, shine bani da hujjar kare kaina, Yanzu kuwa na samu wallahi duk wanda ya kuma cemin Karuwa dai dai nake da shi, zan mayarwa mutum daidai da abunda ya gayamin, ni ba Mazinaciya bace, bana aikata zina ban taɓa ba kuma ba zan fara ba, Imran kome na zama A duniya duk lalacewar da nayi a duniya da sa hannunku a ciki kune sila, kasan irin baƙar wahalar da na sha kuwa? Ka san irin raɗaɗi da zafin maraici kuwa,? Maraici na rashin uwa da uba, kuma na tashi a tsakanin maƙiya, mahaifiyarka taƙi karɓata, na tashi ina gararanba a gari wasu lokutan abunda zanci ya gagarrni, bayan tulin aikin da nake kamar jaka, ba wanda ya damu da ina jin yunwa, ƙishirwa ko bani da lafiya, ba wanda ya damu da wani kalar Abinci zanci a ina zan kwanta, saboda na rasa babban jigo abun jigina wato iyaye, ina da ɗan uwan mahaifiya a raye me tarin dukiya, amma na kasa samun gata, kiyayewar Ubangiji ita ta tsareni har na kawo wannan lokaci, amma idonku ya rufe kun gaza ganin naku laifin, kullum se jifana da muguwar kalma me muni, me ɗacin gaske Karuwa, hmmm don't try to pretend that kana jin tausayina yanzu, a baya na fi buƙatar tausaya wa, da ja a jiki amma ban samu ba, se baƙin wulaƙanci da na fuskanta a gidan ka, bakomai Allahn da ya ɗauki iyayena ya na ƙaunata kuma baze bari in taɓe ba"

WUTA A MASAƘAWhere stories live. Discover now