CHAPTER 17

54 7 0
                                    

  Na idar da sallah ina Kan sallaya Ina adduaa naji sallamar ya khalifa,Kan kujera ya samu ya zauna Yana fadin asamu a aduua,gyada Kai nayi alaman toh,nagama addua na,ban tashi ba nadai jingina a jikin gado Ina facing Yaya khalifa,kallona yayi da damuwa yace meke damunki ne,Sai naji zuciya ta takara karaya,ido na ya ciko da kwalla yace Kar kiyimin kuka ki Zama jaruma Mana kanwar soja,meke faruwa,ce Masa nayi Yaya khalifa tanimu mutuwa zeyi, subhanallahi meke damunshi yafada,nace cancer gareshi Kuma ya kamashi sosai Ni ya zanyi yanzu inya mutu,Nima saidai in mutu kawai,hannu yasa ya rufe bakinshi alaman inyi shiru,yace Yi shiru banson sakarci.
   Inaso kisan kowa Sai lokacin sa yayi ze mutu,duk Mai Rai mamaci ne,kinsan kalan aiki na Nima akwai hadari sosai,wani lokacin in zamu fita operation Sai inji kaman bazan dawo ba,Amma Kuma Sai ince ko da na mutu ai lokaci na ne yayi,hakan ke sawa ina Kara gyara halaye na Nima,saboda ko da na mutu inje aljanna in huta,mutuwan ta zama hutu a gareni, lallai cuta ba mutuwa ba ce,lallai Allah ya jarabci tanimu da babbar jarabawa na ciwon cancer Amma ya kamata ki zamto Mai karfafa Masa guiwa da kasancewa tare da shi sosai because yanzu ne zai bukaci kulawan masoyanshi,cancer Ana Jin sauki Amma Kuma gaskiya akwai wahalhalu kala kala,yanda cutar ke cin jiki ga tsadar magunguna,ga zafin chemotherapy 🥺,zafin sa Yana Kona gashin jikin Wanda akeyi ma,ba tsoro nakeso in Baki ba,Amma Ina so kisan it's not going to be easy but you have to be very strong for tanimu ba wannan kukan ba,ki zamto cikin masu karfafa Masa guiwa,kidinga yimasa adduaa sosai sosai,kema Zaki samu ladan hakan,banaso inganki a cikin damuwa kuma shima nasan ba zai so hakan ba,kiyi hakuri da kaddarar Allah kidinga Yi Masa adduaa da kulawa zaifi bukatar hakan.
Duk maganan da ya khalifa keyi kaina Yana kasa Ina jinsa hawayen sun daina zubo min,saidai jikina yayi sanyi Kuma maganan ta karfafa min guiwa,yace Asiya kinyi shiru kinji ni kuwa,cewa nayi eh najika ya khalifa,yauwa kanwar soja Ina so ki San kema yanzu wani yaki ne kikeyi,Sai kin jajirce sannan ki cinye ta,Allah ubangiji ya bashi lafiya,kibani number shi zanje har gida in duba shi,Dan inaso jibi Zan koma aiki,hutun kwana uku ne dama nazo inyi.
  Da Kuma ganin hafsa ko,a hankali nafada hakan yace yauwa gulmammiya Ashe kina sane,nace ai Ina jiranka kayi min bayanin abinda nagani ne,ke dayar gulmammiya fito in kin Gama leken namu,kofa ya kalla aikuwa Sai ga siyama nan ta fito tana kyalkyala dariya,cewa tayi nifa yanzu nazo zanyi sallama kenan naji kayi magana ta,harara ya khalifa ya balla Mata,yace kedai Zo kiji gulman da kukeson ji,siyama harda gyara Zama Dan muji me zaice ,cewa yayi toh ku shirya in Allah yaso aure zamuyi nida hafsa Dan gaskiya ta sace min zuciya ta.
   Naje wurin aiki watarana munsha operation Mai zafi mu da bandits kamar bazamuyi Rai ba,dama Ni tun Ina chan wurin a Raina nace yakamata fa inzo inyi aure Kar in mutu ban bar ko yara ba,a Raina nace in nadawo Zan dinga Dan duba Yan Mata dan ko kallo Basu isheni ba Inna gansu ya kamata in Fara dubawa yanzu,aikuwa nadawo gida nayi salloli na na roki Allah ya hadani da matar aurena, Kamar yanda na Saba,na koma na kwanta naji wayata na ringing,na duba Naga number da bansani ba,Sai naji wata Yan Mata,katsesa nayi da dariya nace ahap Ni nasan hafsa ce ta Kira ka dama ba Kai ka neme ta ba,cewa yayi ai ba laifi tayi ba Ni ta burgeni.
Siyama tace lallai Yaya har shigan Mata fada kafara Yi,dariya yayi yace toh ku hade min Kai,mikewa yayi Wai shi yafasa karasa Mana labarin,kawo shi nayi siyama ma najan shi a dole Sai ya karasa Mana labarin,har dakin shi ya koma mukuma Muna biye dashi Kamar mayu a dole Sai munji yanda akayi.
  Saida yaga dama ya cigaba da labarin,aikuwa Sai tace sunan ta hafsa ai ta kirane ta gaishe Ni,abinki da lonely soldier ya dawo yaki na biye Mata nace toh daga Ina,Haka duk tabani labarin ta,Nima daga nan Sai Ina kiranta time to time,sannan nace ta turo pictures tace dai Inna Zo kaduna inzo gidansu,Saida nadawo yau nace first abinda zanyi Zan Fara zuwa gidansu,tace daga kaduna ko lokacin tunanin hafsa kawarki bezo min ba har Sai yau da naje har gidansu naganta sannan,Kuma kawai Wai Sai gaku kunzo kun kamani a gidan,kiyi hakuri dama nayi niyyar da nadawo in fada miki,kawai sai kuka Zo kuka ganmu coincidentally,Soo we are sorry on behalf of me and my wife to be,shewa mukayi sosai nida siyama,firar mu dai muketa Yi har mama ta leko dakin ta ganmu,ko ban fada ba nasan dadin yanda ta ganmu tare gaba daya Muna fira taji saboda yanda ta ke kallonmu da kulawa,Allah sarki "NI DA YAN GIDANMU".
    Damuwa ta Sai naji duk ta ragu,lallai ba abinda ya fi fira da Dan uwa Dadi, alhamdulillah.

NI DA YAN GIDAN MUWhere stories live. Discover now