The messges

652 62 9
                                    

*💖JYY💖*






*46-47*





'''NIMCYLUV🤏🏼'''



'''Wattpad'''
https://my.w.tt/jN2GLY5RKcb


*_@Telegram_* https://t.me/joinchat/U6Qw0BuhKkqh5GZ8RadieQ





_______
_______

Durƙushewa yay a wajan yayinda zuciyarsa ta shiga ta farfasa jikinsa ya ɗauki rawa idanunsa suka sauya kala daga farin zuwa jaa,wasu hawayene masu zafi suka shiga fita daga cikin idanunsa,ya rasa mai yasa yake da rauni a kanta,mai yasa ƙwalla bata fita daga idanunsa saita dalilinta,itace mutum na farko daya sashi zubda hawaye gashi still bai daina ba,shin wanne irin mijine shi da har yay sake aka ɗauke masa mata a lkcn da yafi buƙatar kasan cewa da ita a koda yaushe,hannusa yasa ya dafe kansa a hankali ya shiga furta "Hasbunallahu wani'iemal wakil,Ubangiji kayimin maganin abinda yake shirin tun karuni,ya Allah kayimin maganin waɗannan mutanan danka fini saninsu,ya wahabu kayimin tsakani dasu,ya ganiyu ka karemin matana daga kaidinsu,ya laɗifu ka haskamin inda zan ganta na samuta,ya hakamu ka sassautamin daga ciwo da raɗaɗin da suka saka zuciyna,Ya Allah nasan baka goyan bayan azzalumi Allah nayi tawassali da ƙyawawan sunayenka guda ɗari babu ɗaya,Allah nayi imanin da Annabi Muhammad S.a.w,Ya samadu nayi imani da ƙaddara wlh nayi imani da ita Allah ka shigemin gaba ka zama jagorana mai bani kariya My sunshine bby stop cry i knew kina cikin tashin hankali da yardar Ubangiji saina samuki"

Da sauri ya miƙe ya nufi inda motarsa take yana zuwa ya faɗa ya jata da gudu babu inda ya tsaya police station da Agent vizer sai kuma tashoshin mota haka ya dinga bulayi a gari babu Lili babu labarinta,lkcn guda ya fita a hayyacinsa baya gane komai sbd tsananin tashin hankali,bai dawo gida ba sai wajan 11 na dare,yana zuwa ya samu Mama da Najma sai Kuma Sufyan Fairus da Khalid,yana shiga bai tsaya takan kuwa ba duk da irin kiran da Mama take masa amma bai kulata ba bare tasa ran zai tankata,cike da tashin hankali Mama tabi bayan Fahad da kallo haka kawai jikinta ya gaya mata ba lafiya musamman da bata ganshi da Lubna ba.

"Mama lafiyansa lou kuwa banga rabin rai ba?"cewar Najma ta faɗa cikin damuwa kafin Mama tai magana Fairus yace "gsky dai banjin lafiya domin yanayinsa kawai zai nuna ba lafiya ba"shuru Mama tayi abin duniya duk ya dameta sosai zuciyarsata tayi sanyi jiki babu ƙwari ta miƙe tare da nufar ɗakinsa Najma ce fa rufa mata baya a tare suka shiga a nan tsakiyar bed suka samesa ƙwance idanunsa a rufe ruf,yana jin shiguwarsu amma ko mutsi baiyi ba,Najma ce tace "Yaya hope komai nrml"idanunsa da sukai masa nauyi ya buɗe tare da watsasu kan Najma hantar cikinta ce ta kaɗan musamman kallon da taga nayayi mata mai kama da tuhuma yasa tayi saurin ficewa a ɗakin,zama Mama tayi tare da shafa kansa tace "Yarona ina fatan ba wani abun bane na ganka a hargitse?"idanu ya zuba mata kafin wasu hawaye su shiga zuba daga idanunsa,a ɗan rikice Mama tace "ya salam kuka a idanun gwarzon namiji lallai ko mene wannan ya taɓa ranka"rungometa yay tare da fashewa da kuka bubbuga bayansa ta shigayi tare da shafa kansa sosai yake kuka da ƙyar Mama ta samu ya lafa ya shiga sauke ajjiyar zuciya "mene?" shine tambayar da Mama ta cilla masa,hannunta ya riƙe cikin muryar kuka yace "Mama sun ɗauken mata,sun ɗauken farin cikina zuciyata ciwo bazan juri rashinta ba dan Allah ki nemomin ita"salati Mama ta shigayi tare dayin shuru ta ɓoye damuwar dake ranta tace "Ka ƙwantar da hankalinka inaji a jikina babu abinda zai sameta duk inda take,kuma duk mai ƙoƙarin cutar da mutum Allah baya bashi iko,tabbas sun cika azzalumai mai suke so?mai suke nema da zasu ɗauki matar aure?"shuru yay yana tunani kala² a ransa yama rasa gane kan abun duk inda yake tunanin ganin ya duba babu ita,cikinsa ta shafa tace "Yarona ba dai bakaci abinci ba?"fuska ya ƙwaɓe ba tare daya ce komai ba,miƙewa tayi ta nufi haɗu masa coffee tana fita ya miƙe ya sawa ƙofar key dan baijin zai iyacin wani abu a halin da yake ciki.

 JUYAYIWhere stories live. Discover now