DARE DUBU

By PrincessAmrah

11.5K 1.5K 68

Kaddara! Mece ce ita? Yaya rayuwar yarinya mai karancin shekaru za ta kasance a lokacin da ta tsinci kanta ci... More

PROLOGUE
Page 01- Khairi
Page 02- Damuwa
Page 03- Fargaba
Page 04- Mafarin Komai
Page 05- Masauki
Page 06- From God We Are...
Page 07- Tushiya...
Page 08- Zalunci
Page 09- Dream
Page 10- Fushin Masoyi...
Page 11- Kewa
Page 12- Samu da Rashi
Page 13- Mafita
Page 14- Assignment
Page 15- Kudin Fansa
Page 16- Daren Farko
Page 17- Headmaster
Page 18- Tarko
Page 19- Kura Da Fatar Akuya
Page 20- Plan
Page 21- Suspect
Page 22- A Week To Go
Page 23- Informers
Page 24- Bankwana
Page 25- Kiran Sirri
Page 26- Arrest
Page 27- Dare Dubu
Page 28- Next Assignment
Page 29- Soyayya
Page 30- Visiting
Page 31- Alkalamin Kaddara
Page 32- Nusaiba
Page 33- Baby Boy
Page 34- Matar Haidar
Page 35- Award Morning
Page 36- I Love You
Page 37- Kambun Baka
Page 38- Kai Amarya
Page 39- Kukan Zuci
Page 40- Reconciliation
Page 41- Karshen Munafuki...
Page 42- Ruwan Zuma
Page 43- Class Rep.
Page 44- Happy Birthday
Page 45- WTTW
Page 46- Barrista Khairi
Page 47- Rama Sharri da Alheri
Page 48- Kauyawa
Page 49- Court
Page 50- Luck
Page 51- Babbar Kotu
Page 52- Medical Report
Page 53- Doctor Marzuq
Page 54- Shaidar Zur
Page 55- Confess 1
Page 57- Wata Sabuwa...
Page 58- Women Leader
Page 59- Bakar Manufa
Page 60- Komai Ya Yi Farko...

Page 56- Confess 2

129 23 2
By PrincessAmrah

Page 56

Cike da farinciki muka fito daga kotun. Yayin da iyalan Alhaji Abdulkadir suka kasance cikin alhinin wannan al'amari tare da mamakin matar da ta sanya a kuntata wa Hannatu.

A mota na samu Haidar bayan mun gama tattaunawa ni da Fa'iz. Da annuri ya kama hannuna ya rike yana fadin,
"Barka da arziki Buttercup."
Na sakan masa murmushi.
"Na sani ba komai ba ne ba face karfin addu'a Daddy. Addu'a ce ta yi tasiri har Allah Ya matsi bakinsa ya tona asiri."
"Gaskiya ita ce tabbas."
Ya tayar da motar.
"Mu je ko City Restaurant mu ci abinci ko? Tunda akwai wadataccen lokaci."
Na daga masa kai.

"Wato mutum mugun icce ne Daddy. Kodayake ni fa ban ma yi mamaki sosai ba Allah. Dan wannan matar ba karamar muguwa ba ce."
Daga nan na hau ba shi labarin yadda ta dinga zaluntarmu ni da Ummu kawai saboda ba ta kaunarmu don muna da kokari, ashe ita haka take, hassada gare ta."
"Ai ga shi nan yau dubunta ta cika."
"Tabbas kuwa Daddy. Don yanzu hukunci iridaya za a yanke musu; da su da suka aikata fyaden, da ita da ta sanya su, zunubinsu iridaya ne, ba za a bambanta su ba a wurin hukunci."
Haidar ya yi kwafa,
"Ai gara a kashe matsiyata."
Na saki murmushi ina kallon shi.
"Ai a dokar kasarmu ba kashe su za a yi ba. Daurin rai da rai ne za a yi musu. Amma ka ga China, hukuncin kisa ake yanke wa Rapist, haka ma Egypt, Saudi Arabia, da kuma North Korea. Su ma duk kisa ne hukuncinsu. Amma ka ga India, UK, da US duk life imprisonment ne irin na Nigeria. Su kuma Israel 16 years imprisonment."
Haidar ya yi tsaki.
"Ai wallahi da ma mazakutarsu aka dinga cire musu. Da an raba su da abin da ya aikata aika-aikar, kila da wasu sun hankalta sun daina."

Dariya na dinga yi sosai har muka isa restaurant din.

***
Karfe daya da rabi aka dawo kotu. Bayan shigowar alkali, sai ga su Ahmadu ma an shigo da su, sannan Malama Zainab, wata 'yar sanda mace na tura ta amma tana tirjiya. Har sai da alkali ya daka mata tsawa sannan ta nutsu ta shigo wurin tsayuwar masu laifi.

"Ko za ka maimaita mana abin da ka fada kafin mu tafi hutu?"
Alkalin ya tambaya idonsa a kan Ibro.
"Yallabai, duk abin da muka aikata wannan muguwar matar ce ta saka mu. Ta kashe mana rayuwa tun da kuruciya muke yi mata aiki. Da ta ga kamar muna neman kama gabanmu ne ya sa ta saman mana wannan aikin a cikin estate dinsu, tunda abokin mijinta ne mallakin estate din. Sannan da tsiya ta cusa mu wurin mijinta, har ya aminta da mu. Daga nan ne sai muka samu kwanciyar hankalin ci gaba da mu'amala da ita, amma cikin taka-tsan-tsan. Ba gida daya suke da kishiyarta ba amma duk cikin estate guda ne.
Ranar goma sha tara ga watan tara na wannan shekarar, muna zaune a cikin daya daga cikin gine-ginen da ake yi, ta kira wayar Saminu. Ta ce tana son ganin mu, sannan ta fada masa a inda za mu same ta.
Ko da muka je, jakar kudi ta nuna mana, kudi ne makil 'yan dari biyar-biyar. Ta ce,
"Wani aiki nake so ku yi min, idan har kuka yi shi ba tare da kun bar wata alama da za ta darsa zargin wanda ya yi abun ba, duk kudin nan naku ne."
Muka hau tafa hannuwa, sai ta ci gaba da cewa,
"Kun san Hannatu ai. Ita nake so ku aika lahira."
Dukkanmu mun tsorata da jin hakan, saboda diyar Oga ce, kuma yarinyar ba ta da matsala. Wani lokacin har abinci take ba mu idan muka je gidan.
"An riga an cire wa uwarta mahaifa, ba za ta taba sake haihuwa ba. To ni kuma nake so har ita Hannatun ta fita daga jerin 'ya'yan Alhaji AK. Ya zamana daga ni sai 'ya'yana kawai. Kafin ita ma uwar tata a aika ta inda diyar ta tafi."
Ta fiddo bandir hudu na kudin ta mika mana kowa guda-guda.
"Wannan somin-tab'i ne. Idan kuka aiwatar da aikin, zan ba ku irinsu sau hurhud'u, kun ga duk mutum daya zai tashi da dubu dari biyu da hamsin kenan."

Jin hakan sai ya faranta mana rayuka. Muka kara tafa hannu muna shewa.
"Abu mai sauki ma kenan Hajjatu. Ai ki sa a ranki an yi an gama. Kamar yadda ba a taba samun mishkila ba a aikinmu, haka wannan din ma ba za a samu ba."

Daga haka ta sallame mu ta tafi. Mu kuma muka zauna shawarar ta inda za mu fara. Shi ne a karshe muka tsaya a kan za mu kwashi romo daga jikinta, kafin mu yanka ta da wukar da ke jikin Saminu. Wannan shi ne gaskiyar abin da ya faru."

Ya karasa maganar cike da rauni. Ai kuwa kotu ta kaure da hayaniya. Alhaji Abdulkadir shiru ya yi da alama ya zama speechless. Na mayar da duba na ga Anti Khadija, kuka take wiwi.
Can na tsinto muryar Malama Zainab, cikin hargowa tana fadin,
"Wallahi karya suke yi min...ku jiye mini masharrantan yara. Ni ina ma na taba ganin ku? Wallahi ban san su ba yallabai..."

"Order!"
Alkali ya fada cikin tsawa. Dole ta shiga taitayinta, ta hau mazurai.
Saminu da hawaye suka gama wankewa, ya daga hannunsa. Alkali ya ba shi izinin magana.
"Yallabai, duk abin da Ibro ya fada haka ne. Wallahi da gaskiyarsa. Wannan matar muguwa ce. Ta jima tana sanya mu aikata mummunan abu. Dan ko matar nan da aka kawo dazu, aka ce wai mahaifiyata ce, wallahi ban taba ganin ta ba sai yau. Ni dai lauyanmu ya same mu, ya shaida mana za a kawo wata mata da za ta zama mahaifiyata, wai daga wata asibiti suka je suka samo ta a kan cewa za a biya mata kudin magunguna idan har ta bayar da shaidar ita ce mahaifiyata. Amma Allah na sama Yana gani ban san ta ba."

Sama'ila ya karbe da fadin,
"Da gaske ta jima tana sanya mu aiki. Daga cikin ayyukan da muka yi mata har da kisan 'yar'uwar waccan."
Ya nuna ni da hannu.
"Ni dai ban san mene ne ya hada su ba da farko. Amma dai ta sanya mu mun ci gaba da bibiyar su, daga makaranta zuwa gida. Amma a lokacin sai muka kyale su saboda hanyar cike take da mutane dole idan muka taba su za a iya ganewa.
Daga baya kuma sai muka samu labarin an sace su, masu garkuwa da mutane. Hajiya ta yi ta dariya tana cewa Allah Ya kara. Amma duk da haka ta ce ba za mu kyale su ba, yadda suka ja ta hakura da aikinta duk son da take yi masa, ba za ta taba kyale su ba. Sai ta ce mu kashe musu iyaye, ko mu nakasa su. Ita da kanta ta samo mana bindiga, ta damka mana tare da cewa mu lura sosai, mu yi aiki yadda ya kamata.
A lokacin da muka fara bibiyar Baban nasu, sai kawai muka gan shi yana ta nufan wani daji bayan mun sauka daga motar garin Sassanya da muka hau. Daga nan muka fara tsorata, sai muka jira a bakin wani icce. Can kuma sai ga shi ya taho tare da daya daga cikinsu, shi ne mu kuma muka saita mata bindiga, a take ta fadi wurin, hakan ya ba mu tabbacin ta mutu. Sai muka samu muka gudu ba tare da barin shaidar komai ba.
Samun nasarar kashe ta ya sanya ta ce ita gudar, wato waccan lauyar, mu bar ta kawai, radadin mutuwar 'yar'uwarta ba zai taba barin ta jin dadin duniya ba."

Duk da gudumar da alkali ke bugawa yana fadin
"Order!"
Hakan bai sanya aka yi shiru ba, har sai da aka dauki dogon lokaci kafin aka nutsu.
Na dago kai na dube ta, kai kawai na gyada ina sharce hawayena.
Wannan fa shi ne ana zaton wuta a makera...na yi shiru da tunanin, jin alkali ya fara magana.

"A bisa zantukan da duk muka saurara, masu laifi sun amsa laifinsu. Sannan sun tona wa wacce da sanya su, suke yi mata aiki, asiri. Kotu ta yanke wa Ahmadu, Saminu, Ibrahim (Ibro) da kuma Sama'il, daurin rai da rai a gidan yari, tare da horo mai tsanani. Kotu ta sassauta musu ne bisa ga la'akari da tona wa kansu asiri da suka yi."
Ya yi gajeren rubutu, ya dago fuskarsa ya ce,
"Sannan Mrs Zainab Abdulkadir, kotu ta yanke mata hukuncin kisa ta hanyar rataya, tare da tarar naira miliyan biyu ga Hannatu da aka keta wa haddi."
Ya buga guduma hade da fadin,
"Kooootu!"
Ya mike ya fice.

In ban da gunjin kukansu babu abin da yake tashi. Ni kuwa fuskata fal da annuri. Farinciki biyu a lokaci guda; ga na samun nasarar shari'armu, ga kuma ta tonuwar asirin makasan 'yar'uwata, aminiyata, wacce kullum nake kwana na tashi da takaicin rashin gane wadanda suka kashetan.
A lokaci guda muka kalli juna ni da Barrista Rafiq, ya sakar min murmushi ya ce,
"Congratulations Barrista Khairi. Sai mun hadu next time?"
Na daga masa kai.
"In shaa Allahu an dasa yin nasara kenan a kanka Barrista. Da kai da ire-irenka ma."
Sannan na dubi Fa'iz da ke fadin
"Congratulation Barrister Khairi."
Ni ma na maimaita masa,
"Congratulations Barrista Fa'iz."
Sannan duk muka mike.

Ji na yi an rungume ni, ina dubawa na ga Hannatu ce. Kuka mai hade da dariya take yi. Na hau bubbuga bayanta a hankali ina fadin,
"Barka da arziki Hannatu. A yau Allah Ya nufa an karban miki hakkinki. Duk da babu abin da zai iya maye gurbin babban abin da kika yi rashi, amma at least za ki rage kaso mai yawa na daga cikin kuncinki."
Ta dago daga jikina ta ce,
"Dukkanin kokarin naki ne Aunty Khairi. Ba zan taba mantawa da ke da tarin alkhairinki ba a gare ni. Hakika sunanki ya cancanta a gare ki sosai, uwar alkhairi, domin kuwa na ga alkhairin naki."

Kama ta na yi muka fita, saboda duk idanuwanmu mutane a kanmu suke. Muna tsayuwa sai ji na yi an taba ni. Anti Khadija ce. Kafin fadan komai sai gani na yi ta zube a kasa, guiwoyinta bisa kasa, ba ta damu da dattin da za ta iya kwasa ba. Ta kama bakin gyalena. Cikin kuka ta ce,
"Ban san da wane baki zan iya gode miki ba Khairi. Hakika kin saka sharri da alheri, kin nuna min kin fi ni. Yau ga ranar da Allah Ya nuna min iyakata, ke din da na dinga aibuntawa a baya, kin yi min abin da ba ni da bakin gode miki. Allah'n da Ya halicce ni, Ya san sirrin da ke cikin kalbi, Shi kadai ne zai iya biyan ki. Abu daya da zan iya cewa a yanzu shi ne, ki yafe min komai, idan na ce komai, ina nufin komai da komai. Ki manta da baya, ki kalle ni a matsayin 'yar'uwarki mai kaunarki har cikin zuciya. Wallahi na ga ishara...na ga ishara Khairi."

Kuka take yi sosai, wani irin tausayinta ne ya shige ni, na kama hannunta na mikar tsaye, sai kawai na ji kwallan ni ma sun zo min, muka rungume juna muna sakin kuka a tare.

Amrah A Mashi❤️

Continue Reading

You'll Also Like

807K 69.4K 59
Zanen ƙaddaransa yana cikin zuciyarta, kamar yanda zanen nata ƙaddan ke cikin tasa zuciyar. Idan zuciyoyi suka haɗe waje guda akan samu wata irin zaz...
11.1K 72 15
está es una historia donde nos demuestran que el amor no tiene límites te vas a enamorar de un mafioso? no importa en esta historia te lo demostrarem...
5.2K 465 111
Labarin tsantsar soyayya me cike da sarkakiya ce ta kullu a tsakanin su. Ummulkhair ta zamo Allura cikin ruwa wanda me rabo ne ze dauka. Shin wa zat...
65.9K 5.8K 36
U+Z ဒီနေ့မင်းလွင် + ဒီယောရာဇာဓိရာဇ်