DARE DUBU

By PrincessAmrah

11.4K 1.5K 68

Kaddara! Mece ce ita? Yaya rayuwar yarinya mai karancin shekaru za ta kasance a lokacin da ta tsinci kanta ci... More

PROLOGUE
Page 01- Khairi
Page 02- Damuwa
Page 03- Fargaba
Page 04- Mafarin Komai
Page 05- Masauki
Page 06- From God We Are...
Page 07- Tushiya...
Page 08- Zalunci
Page 09- Dream
Page 10- Fushin Masoyi...
Page 11- Kewa
Page 12- Samu da Rashi
Page 13- Mafita
Page 14- Assignment
Page 15- Kudin Fansa
Page 16- Daren Farko
Page 17- Headmaster
Page 18- Tarko
Page 19- Kura Da Fatar Akuya
Page 20- Plan
Page 21- Suspect
Page 22- A Week To Go
Page 23- Informers
Page 24- Bankwana
Page 25- Kiran Sirri
Page 26- Arrest
Page 27- Dare Dubu
Page 28- Next Assignment
Page 29- Soyayya
Page 30- Visiting
Page 31- Alkalamin Kaddara
Page 32- Nusaiba
Page 33- Baby Boy
Page 34- Matar Haidar
Page 35- Award Morning
Page 36- I Love You
Page 37- Kambun Baka
Page 38- Kai Amarya
Page 39- Kukan Zuci
Page 40- Reconciliation
Page 41- Karshen Munafuki...
Page 42- Ruwan Zuma
Page 43- Class Rep.
Page 44- Happy Birthday
Page 45- WTTW
Page 46- Barrista Khairi
Page 47- Rama Sharri da Alheri
Page 48- Kauyawa
Page 49- Court
Page 51- Babbar Kotu
Page 52- Medical Report
Page 53- Doctor Marzuq
Page 54- Shaidar Zur
Page 55- Confess 1
Page 56- Confess 2
Page 57- Wata Sabuwa...
Page 58- Women Leader
Page 59- Bakar Manufa
Page 60- Komai Ya Yi Farko...

Page 50- Luck

123 25 1
By PrincessAmrah

Page 50

Raina a dagule na koma gida. Haidar ya dinga kokarin kwantar min da hankali amma ko kadan hankalin nawa bai kwanta ba. Idan har ban samu hujjojin da zan mika wa kotu ba na tabbata next zaman da za a yi alkali zai yi watsi da shari'ar tunda ban tanadi komai ba.
Ganin yadda na gaza samun nutsuwa ya sanya shi fadin,

"Ni dai ina da shawara guda daya. Ban san ko za ta yi amfani ba."
Na dube shi a sanyaye na ce,
"Go ahead Daddy. It might help ai, ba a san inda rana ke faduwa ba."

Idanuwansa a cikin nawa ya ce,
"Ko zuwa gobe da yamma idan kin taso daga aiki, kina iya zuwa ki dauki Hannatun, ku je ta raka ki har inda abun ya faru, next village daga wurin za ku tsaya. Watakila za ku ga kauyawan nan da ta ce sun gani."

Na gyada kai, cikin damuwa na ce,
"Ta ce ko ta gan su ba za ta iya gane su ba ai."

Ya dan yi shiru jim, kafin ya ce,
"Ni a gani na sai dai idan ba ta gan su ba din. Da ta gan su kina iya ganin ta gane. Idan ma ita ba ta gane su ba ai su sun san ta ko? Za su iya gane ta, ina kyautata zaton idan sun gane ta din za su taimaka wajen zuwa kotu su bayar da shaida."

Wannan ma shawara ce mai kyau. Na kama hannunsa, fuskata dauke da fara'a na ce,
"Thanks for this idea my darling husband. Tabbas hakan za a yi. Sai dai kuma ka san kauyawa da tsoro fa."
Ya ce,
"Tun da har suka taimaka suka dauke ta a cikin mawuyancin hali suka kai asibiti, duk da tsoron da aka san bakauyen mutum da shi, ina tunanin a yanzu ma za su taimaka din."

Na jinjina kai.
"Haka ne. Amma tare ya kamata mu yi tafiyar nan da kai, ba zai yiwu mu kadai mata mu tafi ba. Ka ga ko ba komai mu tafi tare da jami'in tsaro ai ya fi ko?"

Murmushi ya yi ya ce,
"Matsoraciya. Ke dai kawai ki ce kina jin tsoron kar a kama ku a cikin daji."
Murmushin na yi ni ma na kai masa dukan wasa,
"Ba wani tsoro fa. Tsaro ne kawai."
Ya daga kai.
"Haka ne. Amma tare da abokin aikinki ya kamata mu tafi, idan suka gan mu da dan yawa za su fi sauraren mu."
"E kuma fa. Goben da safe muna isa zan fada masa. Ba ma zan fita da motata ba sai ka sauke ni wurin aikin. Za mu jira ka idan mun gama."
Da wannan shawarar na kwana cikin raina tare da fatan za ta yi aiki.

Washegari muka tafi, Hannatun ita ke gwada mana hanyar da mai napep ya shiga da ita, har zuwa daidai wurin da komai ya faru. Sai da na dauki hoton tsarin wurin, da jikin katangar da ke zagaye da poly inda suka manna ta. Sannan muka wuce.

Mun yi tafiya mai nisa kafin muka isa wani kauye. Da yara muka fara cin karo sun yi tsaitsaye sai kallon motarmu suke.
Barrista Fa'iz ya ce wa Haidar
"Allah dai Ya sa kar mu tsorata su ma. Ka ga yadda suke bin mu da kallo sai ka ce ba su taba ganin mota ba."
Dariya Haidar ma ya yi muka ci gaba da tafiya har zuwa inda gidaje suke. Kauyen bai da wani girma amma sai yawan jama'a, mun fahimci hakan ne daga yanayin yawan yaran da ke yawo ko'ina.

"To wai yanzu ta ina za mu fara ma? Ni dai wallahi kaina a cikin duhu yake."
Na fada ina kallon Haidar ta cikin mirror, da yake bayansa nake, Fa'iz ne a gaba kusa da shi.

"Ku da kuke barristers ma ba ku sani ba sai ni ne zan sani?"
"Sai ka sani mana Daddy. Kai fa jami'in tsaro ne."
Ya ce
"To amma kuma ai ba zan yi amfani da shi ba a yanzu. Don ina nunan musu da haka ba za su yarda su bi mu ba wallahi, duk yadda zan yi da su kuwa."

Barrista Fa'iz ne ya ce,
"Ina da idea guda daya. Allah dai Ya sa ta haifar mana da d'a mai ido."

Haidar ya dube shi ya ce,
"What? Allah dai Ya sa ba kana planning mu bi gida-gida ba ne. Sunan wani gwamna."
Duk muka sa dariya.
Ya ce,
"Ba haka ba ne. Gidan mai gari dai ya kamata mu nema, mu fada masa gaskiyar abin da ya kawo mu, watakila ya fahimci manufarmu."
"Ta yaya kenan? Kana tunanin daga mun fadi haka shi kenan kuma sai a same su?"
Na gaggauta tambayar sa.
"A'a. Ina tunanin watakila idan mun shaida masa ranar da abun ya faru, a yi shela ana neman magidanta, daga nan idan an dace shi kenan."

Haidar ya goyi bayan wannan idea, don haka sai muka yi parking a gaban wani gida. Ni da Hannatu ne a karshe su biyu kuma gabanmu.

Wasu yara Haidar ya tambaya gidan mai gari. A tsorace suke, don haka sai ya saki murmushi, ya ce,
"Kun ga ba ku san mu ba ko? Baki ne daga birni muke. Akwai wasu bayin Allah ne da muka zo mu saka musu da alkhairi kwatankwacin yadda suka saka mana mu ma."
Barrista Fa'iz ya dora da
"Watakila ma kun san su. Wasu mata da miji ne, za ku gan su tare suke tafiya ko'ina, har cikin Katsina suke zuwa su biyun."

Gudan yaron har da saurinsa ya ce,
"Wasu wanda matar ba ta da tsayi amma shi namijin dogo ne ko?
Na yi saurin daga musu kai duk da ban san hakan ne ko ba haka ba.
Yaron ya ce,
"Kai Habu ba ka gane su ba? Kawu Sada ne fa shi da Inna Safare. Ka tuna har Baba na yi musu fada a kan yawan tafiyar kafa da suke yi har zuwa Katsina? Ai yanzu ma haka ba su nan suna can Katsinar."
"Ka tabbata?"
Yaron ya jinjina kai.
"Ai duk kauyen nan babu mai tafiya tare da matarsa idan ba Kawu Sada ba. An ce wai aiki suke zuwa a wani gida, shi ya sa sai karshen mako suke zuwa nan."

Na fada kogin tunani. Can kuma na ce,
"A wace rana ce suke tafiya, kuma yaushe suke dawowa?"
Na fadi hakan ne ina tuna ranar da kaddarar can ta afka wa Hannatu.
"Akwai dai ranar da na ga za su tafi, kamar ranar Litinin ne da safe."
Dayan ya yi caraf ya ce,
"E Litinin ne ka ma tuna min. Ba har Ummaru ya ce zai dinga bin su ya je makaranta ba?"
"Haka ne."
Ya ba shi amsa.
"Kamar dai ranar Jumu'a ne suke dawowa nan."

Kawai sai na ji hankalina ya kwanta da bayanin yaran. Ta yiwu su din ne, ta yiwu kuma ba su ba ne. Na dubi Haidar da Fa'iz na ce,
"Ina ji a jikina fa mun dace."
Ashe su ma tunanin da suke yi kenan. Fa'iz ya ce,
"Za mu tabbatar da hakan ne idan muka dawo ranar Asabar."
Ya dubi dayan yaron ya ce,
"Yaya sunanka?"
"Garbati."
Ya ba shi amsa.
"Ina ne gidanku?"
Da hannu ya gwada mana gidan nasu, babu nisa daga nan.
Haidar ya dube shi, ya ce,
"Ka san yadda za a yi? Ranar Asabar idan Allah Ya kai mu, za mu dawo, da yamma kamar haka dai bayan la'asar. Sai ka jira mu a daidai nan, daga nan ka raka mu gidan nasu."
Yaro ya jinjina kai.
"To sai kun zo."
Haidar ya zaro dari biyu ya ba su ya ce su raba. A take fuskarsu ta fadada da annuri, mu kuma muka koma cikin mota tare da fatan wannan hikimar da muka yi mu dace.

Hakan da ya faru sai ni ma na samu wata idea din. Na dubi Hannatu na ce,
"Kin ce za ki gane mai keke napep din nan da ya dauke ki ko?"
Ta daga kai.
"Har keken nashi ma zan iya ganewa. Hatta lambar keken ma..."
Ta dan yi gajeren tunani, kafin ta ce,
"Tabbas na rike ta."
Na saki hamdala a bayyane, domin hakan ba karamin taimaka wa bincikenmu zai yi ba.
Na zaro takarda da biro daga cikin jakata na mika mata na ce,
"Rubuta lambar a nan."
Sannan na daga kaina na ce wa Haidar da Fa'iz,
"Kun san me za mu yi daga wannan step din?"
Dukkansu suka gyada kai. Na ce,
"Kamar yadda masu motocin haya suke da kungiya haka su ma masu keken suke da ita. Tunda ta rike lambar, da ita za mu yi amfani mu je wurin masu keken, mu nemi shugabansu sai ya nemo mana shi, idan har ya yi rijista da kungiyarsu gano shi ba zai mana wahala ba. Sai dai fatan dacewa."

Duk suka hada baki wajen fadin,
"Good idea."
Haidar har da tafa min yake.

Bayan mun iso cikin gari, kai tsaye ofishin masu keke napep muka nema, duk da maghriba ta fara gabatowa amma muka yanke zuwa a yanzun domin kammala komai a kan lokaci. Domin Hausawa sun ce da sanyin safiya ake kamun fara.

Da muka isa wurin, Chairman muka nema wanda shi ne Ogansu duka. Haidar ya mika masa takardar bayan dogon bayanin da Barrista Fa'iz ya yi masa.
Ya duba lambar sosai, kafin ya dago kai ya ce,
"Ban dai gane lambar ba gaskiya, amma zan duba cikin gwanen lambobin da ke jikin littafinmu. Sai dai wani hanzari ba gudu ba, gaskiya mun tashi aikin yau, gobe da safe ku dawo."

Barrista Fa'iz ya zaro kudi daga cikin aljihunsa wanda za su iya kai dubu biyar, ya mika su ga mutumin hade da fadin,
"Sauri muke yi ne ta yadda ba za mu iya jira har sai gobe sannan ka duba mana ba. Ka dai taimaka mana don Allah."

Da fara'arsa ya karbe kudi ya ce mu biyo shi zuwa ofishinsa.
Wani tsohon office ne, kujerun cikin duk sun mutu, ga wani teburi da ke jibge da tulin takardu duk kura.
Zama ya yi a kan kujerar ya hau bincikar wani long book, yana yi yana kara duba takardar da na ba shi.
Ya dan jima yana dubawa sannan ya dago ya ce,
"Kun taki babbar sa'a kuwa, Habibu ne. Yaro mai hankali na tabbata zai yi muku abin da kuke so."

Dukkanmu muka hau godiya ga Allah, na ce,
"Lambar wayarsa fa? Ko za mu iya samun sa a yau?"
"Ga lambarsa nan a gaban lambar keken tashi ai."
Fa'iz ya matsa ya kwafi lambar a wayarsa.
"Idan kun taki sa'a kuna iya samun ganin shi a yau din ma. Idan kuma wayarsa ba ta shiga ba ku yi hakurin gobe."

Godiya muka yi masa tare da tafiya zukatanmu fayau. A raina addu'a nake Allah Ya sa mu same shi.

Fa'iz ya latsa kiran sa sai dai a kashe ya ji wayar. Haidar ya ce,
"Maghiba ta riga ta yi, ni ina ganin a hakura kawai har zuwa gobe sai a neme shi. In shaa Allahu za a dace."

Daga haka muka tsaya. Har gida Haidar ya kai Fa'iz sannan muka biya muka sauke Hannatu ma, a lokacin isha'i ake neman kira. Ko da muka isa gida wanka da sallah kawai na yi, ko abinci ban iya ci ba sai bacci, saboda gajiyar da na yi.



Amrah A Mashi❤️

Continue Reading

You'll Also Like

2.3K 231 15
Saboda yadda mahaifin mu ya din ga saka Mana suna Fatima, har se da nayi tunanin ko Muna da alaka da shi'a ne, saboda Naga yawancin sune mutanen da k...
226K 9.5K 25
"မောင် မဆိုးစမ်းနဲ့ကွယ်" "ကျုပ်ကိုမချုပ်ခြယ်နဲ့"
63.2K 5.6K 36
U+Z ဒီနေ့မင်းလွင် + ဒီယောရာဇာဓိရာဇ်
11.1K 72 15
está es una historia donde nos demuestran que el amor no tiene límites te vas a enamorar de un mafioso? no importa en esta historia te lo demostrarem...