DARE DUBU

By PrincessAmrah

11.5K 1.5K 68

Kaddara! Mece ce ita? Yaya rayuwar yarinya mai karancin shekaru za ta kasance a lokacin da ta tsinci kanta ci... More

PROLOGUE
Page 01- Khairi
Page 02- Damuwa
Page 03- Fargaba
Page 04- Mafarin Komai
Page 05- Masauki
Page 06- From God We Are...
Page 07- Tushiya...
Page 08- Zalunci
Page 09- Dream
Page 10- Fushin Masoyi...
Page 11- Kewa
Page 12- Samu da Rashi
Page 13- Mafita
Page 14- Assignment
Page 15- Kudin Fansa
Page 16- Daren Farko
Page 17- Headmaster
Page 18- Tarko
Page 19- Kura Da Fatar Akuya
Page 20- Plan
Page 21- Suspect
Page 22- A Week To Go
Page 23- Informers
Page 24- Bankwana
Page 25- Kiran Sirri
Page 26- Arrest
Page 27- Dare Dubu
Page 28- Next Assignment
Page 29- Soyayya
Page 30- Visiting
Page 31- Alkalamin Kaddara
Page 32- Nusaiba
Page 33- Baby Boy
Page 34- Matar Haidar
Page 35- Award Morning
Page 36- I Love You
Page 37- Kambun Baka
Page 38- Kai Amarya
Page 39- Kukan Zuci
Page 40- Reconciliation
Page 41- Karshen Munafuki...
Page 42- Ruwan Zuma
Page 43- Class Rep.
Page 44- Happy Birthday
Page 45- WTTW
Page 47- Rama Sharri da Alheri
Page 48- Kauyawa
Page 49- Court
Page 50- Luck
Page 51- Babbar Kotu
Page 52- Medical Report
Page 53- Doctor Marzuq
Page 54- Shaidar Zur
Page 55- Confess 1
Page 56- Confess 2
Page 57- Wata Sabuwa...
Page 58- Women Leader
Page 59- Bakar Manufa
Page 60- Komai Ya Yi Farko...

Page 46- Barrista Khairi

161 20 0
By PrincessAmrah

Page 46

Cike da soyayya da kauna muka ci gaba da rainon Ummunmu. Haidar irin mazan nan ne masu kula, ko sau daya bai taba runtsawa ba matukar ni da Ummu ba mu runtsa ba. Ita kuwa sai ta zabi tashin dare, ba ta bacci sai wuraren ukun dare ko hudu. Da safe kuwa ta sha baccinta har rana.
Haka muke lalacewa kanta ni da shi har wani lokacin ma shi ke daukar ta ya yi ta rirriga har sai ta yi bacci.
Ana cikin haka hutunmu na makaranta ya kare, dole Mami ta samo mana nanny, sunanta Kuluwa, saboda ba zan iya ba da renon Ummu tare da karatu.
A makarantar ma wasu lokutan zuwa yake yi ya duba mu, musamman idan muna da evening lectures.

A hankali Ummu ta fara gyagijewa, ta yi gubul-gubul da ita, ga fara'a, sannan farar fata tas, sumar kanta a kwance luf irin ta mahaifinta. Kowa sha'awar Ummu yake yi tun daga kan malamai har zuwa dalibai.
Wata irin shakuwa ke tsakaninta da mahaifinta, idan zai fita dole ne sai an boye ta, kuma da zarar ta ankara ba ya nan ta dasa kuka kenan, da kyar za a shawo kanta ta yi shiru.

Rayuwa ta ci gaba da tafiya, har zuwa lokacin da na samu wani cikin, a lokacin shekarar Ummu biyu, muna shekara ta karshe a makaranta. Wannan cikin sam ban sha wahala ba kamar wancan. Kasantuwar nanny din Ummu na nan ya sa ban ce Nusaiba ta zo ba.
Muna cikin jarabawar first semester ta final year, na haifi kyakkyawar 'yata mai kama da Ummu sak, har kalar fatarsu da idanuwan da suka dauko na mahaifinsu. An sha shagali sosai kamar na haihuwar farko, Haidar na tsananin kaunar yaransa, sannan ni ma babu abin da ya ragu na daga soyayyar da yake yi min. A take ya yi mata huduba da sunan Mami, Radiya. Su Nusaiba suka zabar mata Afreen a matsayin alkunyarta.

Afreen na da wata shida muka kammala makaranta. Gagarumar walima Haidar ya hada min, inda 'yan'uwa da abokan arziki suka zo, aka ci, aka sha, aka gyagije. Wani irin farinciki nake ciki na irin ci gaba da kullum yake samun rayuwata. Hakika duk wanda ya ce kunci zai dore a rayuwar mutum ya yi karya. Idan na tuno da yadda kaddara ta yi gararamba da rayuwata sai dai kawai in yi murmushi, a wani sa'ilin kuma in yi kuka.
Ga wata irin soyayya da Mami ke gwada mana ni da yarana, tamkar ita ta haife ni.
Sadda aka tashi bikin Safra ita da kanta ta sanya Haidar daukar nauyin kayan daki. A lokacin ba karamin faranta raina ta yi ba, kasantuwar ina matukar tausayin Ummanmu, na kuma san za ta sha wahala sosai tunda ba mataimaki gare ta ba sai Allah. Ina samun kudade sosai saboda ko scholarship da ake ba mu na gwamnati ba kananan kudi ba ne. Idan na karba kuwa kusan duk ga Umma da kannena suke karewa. Ni da kaina na hada wa Safra kayan ado na kawata daki, irin su luxury interiors din nan. Kayan kitchen kuma da ma Umma duk ta gama hada kayanta. Sai kayan dakin ne muke tsaka da neman mafita, sai ga Haidar ya ce ya dauki nauyin komai shi da Maminsa, kuma ita ce ma ta kirkiro shawarar, saboda da ma can suna yi wa marayu kayan aure ita da Haidar, ko da ba su san su ba. Sai dai idan ba su ji ana nema ba.

Na ji dadi, na yi kukan farinciki tare da mika dukkanin ragamar rayuwata ga Haidar Turaki. Sannan Maminsa, Allah ne kadai zai iya biyan ta.

***

Afreen ba ta isa yaye ba amma dole na yaye ta saboda Law School da zan tafi, kuma a ka'ida ba a zuwa da yara, idan ma ba su isa yayen ba dole sai dai ka yi hakurin wata shekara. Wannan dalilin ne ya sanya Haidar ya ba ni goyon bayan yaye ta tunda ta shekara, na tafi na bar ta a hannun Umma tare da Kuluwa; nanny dinsu, da kuma taimakon Sadiya.

A lokacin da zan tafi har da kuka na yi, na shige jikin Haidar don ji na yi ba karamin kewar sa zan yi ba. Da kyar ya rarrashe ni ya kai ni Airport. Ina kuka sosai na tafi na bar shi.
Babu jimawa jirginmu ya tashi. Kabba Law School campus da ke jahar Kogi, a can ne zan yi.

Bayan mun isa na kira Haidar nake shaida masa mun sauka.
"Har na fara kewar ka wallahi Daddy."
Na fada cikin sanyin murya.
"Hmm...ke kenan ma Buttercup. To ni in ce me? Ban san yadda zan yi ba idan dare ya yi, na saba jin ki a cikin jikina."
Na yi gajerarar dariya.
"Ka dauki pillow dina, ka saka a jikinka za ka ji tamkar ni ce."
"Ba ki da abokin tarayya fa, babu abin da zai iya cike min gurbinki. Shekarar nan guda jin ta nake kamar shekara goma."
"Saukin ma ana visiting sweat heart, duk sadda ka samu dama sai ka dauko su Afreen ku kawo min ziyara. Ba zan iya jurar shekara guda ban gan ku ba."

Muka ci gaba da hirarmu ta masoya. Jin jikina babu dadi ne ya sanya na ce bari in watsa ruwa zan kira shi.

***

Tamkar wata daya haka shekara guda ta zagayo, na kammala da Law School dina. A tsayin lokacin nan Haidar ya yi zuwan da ko ni ban san adadinsa ba. A wasu lokutan shi da Ummu da Afreen, Kuluwa, sai kuma Sadiya, haka suke zuwa. Wani lokacin kuwa shi kadai zai zo, ya yi kwana daya ko biyu sannan ya juya ya tafi. Duk sadda zai zo hotel din da ya sauka nake tafiya in kwana a can. Idan tare da su Ummu ya zo kuwa haka muke rabuwa da su suna kuka, musamman ma Ummun da ta yi wayo, ita Afreen saukin rarrashi gare ta, kuma ba ta wani mugun sanin zak'in uwa ba kamar yadda ita Ummu ta sani.

Ranar da na koma, cike na tarar da gidanmu. Yan'uwa duk an zo tarba ta sai murna ake yi. Ummu da Afreen gayu aka ci musu cikin hadaddun dogayen riguna da alama domin wannan ranar kawai Daddynsu ya saya musu.
Gida ya sha gyara, an canja min sababbin kujeru da dining table.

Sai da na yi kwana biyu ina baccin gajiya kafin na wartsake, muka fara nuna wa juna kewar junanmu da muka yi, ni da Haidar. A kwana na uku sai ga dalleliyar mota kirar venza ya canja min. Murna a wurina ba a magana. Da ita na dinga yawata gidajen dangi ina gaishe su saboda jimawar da na yi ba na nan. Afreen tunda na dawo kullum sai ta yi kukan dare saboda rashin sabo. Da kyar dai na shawo kanta ta fara sabawa da ni har ta daina kukan daren.

Bayan sati hudu aka yi posting dinmu NYSC, Allah Ya taimaka na cika married certificate aka bar ni a nan cikin Katsina. Don haka sai lamarin ya yi min dadi don ko camping ma ban yi ba sai da aka gama sannan na fara zuwa wurin bautar Kasata.

Ko da Haidar ya ce min zai sa Ummu makaranta cewa na yi kawai ya hada ya sanya su, a lokacin farkon fara Law School dina ne, sai ita Afreen aka ajiye ta crèche. Shi ya sa a yanzu da na dawo ba ni da haufin tafiya wurin aikina don ta riga ta saba da zuwa makaranta. Sai idan na tashi nake biyawa in dauke su saboda karfe sha biyu kullum nake gamawa.

Wani alwashi da na dauka wanda ko Haidar ban fada wa ba shi ne; zan yi aiki da Human Rights, ba don komai ba sai don raped victims. Su nake son dinga kwato wa fansa gwargwadon iyawa ta.

Na fara duk wani kokarina wajen tinkarar Haidar da batun, duk da na san zai yi wuya ya musa min musamman da ya san ra'ayina ne shige wa raped victims a gaba.

Ranar da muka kammala bautar kasa na tinkare shi da zancen. Ya nuna farincikinsa sosai ya kuma aminta.
"Sai dai ina jiye miki tsoro Baby girl, wallahi rayuwar nan ta zama abin da ta zama, mutane ba sa son gaskiya sam, ba wuya ki ga an illata mutum, daga kokarin bayyanar da gaskiya."
Ya dan yi jim, sannan ya ci gaba da cewa,
"Ko kuma yadda kike da raunin nan, abu kadan zai iya rikita min ke."

Na saki murmushi ina shafar lallausar kasumbarsa,
"Ai ba ka sani ba Daddy, tun da na yi aiki a DSS zuciyata ta zama mai karfi. Ba na jin akwai wani tashin hankalin da zai karya min zuciya."
Ya harare ni yana murmushin shi ma, ya ce,
"Ke din nan da abu kadan kin zubar da hawaye shi ne kike wannan batun? Allah dai Ya kyauta kawai."
"Amin."
Na ce ina kokarin mikewa. Ya sanya hannu ya dawo da ni.
"Allah ba ki isa ba Buttercup. Zo nan ki ba ni tukuicin kammala NYSC. Kin san dai ni ne na farko da na taya ki murna ai ko? To dole a ba ni wani abu..."
Tun bai rufe baki ba na hada bakina da na shi.

***

BAYAN WANI LOKACI.

A cikin ministry of justice, a karkashin  Sexual Assault Referral Centre (SARC), jere lauyoyin da ke bi wa raped victims hakkinsu suke, daga ciki har da ni, watana biyu kenan da na fara aiki, inda na yi shari'a guda biyu. Daya na yi nasara, inda dayar kuma ban samu nasara ba saboda rashin karfafan hujjoji.

Telephone din cikin Office din ne ya yi kara, Barrister Fa'iz ya dauka. Ya dan yi magana sannan ya miko min.
Wanda ke kan telephone din ya ce,
"Barrister UmmulKhairi, akwai wani file da ya iso wurina yanzun nan, case din ya yi tsanani gaskiya, idan kina da ra'ayi, na san ki da tausayi; sai ki zo ki duba."
"Okay Sir."
Na furta cikin sanyin murya. Na ajiye telephone din hade da mikewa na nufi office din na babban lauyan da ke kula da division din, Barrister Nuruddeen.

Ina isa ya miko min file din, ya ce,
"Duba ki gani. Aikin lada ne. Idan za ki iya sai ki samu mataimaki."
Na karba din na fara dubawa. Hannatu Abdulkadir sunan raped victim din. Shekararta goma sha takwas da haihuwa. An yi raping dinta ne a dajin da ke hanyar Polytechnic bayan ta tashi daga makaranta za ta dawo gida.

Dafe kaina na yi cike da alhini ina karantawa. Da na gama na rufe file din, na dubi Barrister Nuru na ce,
"Sir, zan yi in shaa Allah."
Ya saki murmushi hade da fadin,
"I know you can do it. So please try your best, tunda akwai suspects, ki bi mata hakkinta."
Na jinjina kai ina sake duba address da lambar wayar da ke jikin file din wanda za a samu victim din da su.

"You can go with the file. Ki samu ko Barrister Fa'iz ya taimaka miki. A yi duk abin da ya dace, in shaa Allahu nasara tana tare da ku."
"In shaa Allah."
Na maimaita hade da tafiya.

Ko da na ba Barrister Fa'iz file din ya duba, babu tababa ya ce zai taya ni mu yi aikin tare, na ji dadi sosai, muka kuma yanke shawarar daga an tashi aiki kai tsaye gidan su yarinyar za mu tafi.

Muna cikin tattauna maganar ne wayata ta yi kara, cikin shauki na dauki wayar.
"Daddy, good afternoon."
Na fadi da farincikin jin muryarsa.
"Afternoon my Baby girl. Yaya aikin?"
"Alhamdulillahi. Ga shi nan muna ta fama."

Cikin sautin alhini ya ce,
"Wai kin san wani abu? Shekaranjiya ba na fada miki na kai Mami gidan Anti Khadija dubiya ba sai muka tarar wai an tafi asibiti da yarinyar sai Anti Khadijan kawai muka tarar?
Na amsa da
"E haka ka ce.  Jiya kuma da kuka je asibiti ba ku samu ganin Hannatun ba wai likita ne a dakin ko?"
Ya amsa kai tsaye,
"Wai ashe boye-boyen nan da Anti Khadija ke ta faman yi, raping din Hannatun ne aka yi."
Ido bude nake maimaita innalillahi. Na dafe kaina ina tuna halin kirkin Hannatu, da kuma yadda mace ke ji a lokacin da aka haike mata.




Amrah A Mashi❤️

Continue Reading

You'll Also Like

232K 9.6K 25
"မောင် မဆိုးစမ်းနဲ့ကွယ်" "ကျုပ်ကိုမချုပ်ခြယ်နဲ့"
132K 8.6K 55
Kallon kitse ba litaffina bane na marubuciyar nan ne Halima Abdullahi k/mashi
45.1K 2.2K 51
"Don ubanki wanki dana barmiki kimin shine kika kiyimin Kika zauna kika rungume wannan shegiyar d'iyar taki wallahi koki aje ta ko kuma yanzu jikin k...