DARE DUBU

By PrincessAmrah

11.5K 1.5K 68

Kaddara! Mece ce ita? Yaya rayuwar yarinya mai karancin shekaru za ta kasance a lokacin da ta tsinci kanta ci... More

PROLOGUE
Page 01- Khairi
Page 02- Damuwa
Page 03- Fargaba
Page 04- Mafarin Komai
Page 05- Masauki
Page 06- From God We Are...
Page 07- Tushiya...
Page 08- Zalunci
Page 09- Dream
Page 10- Fushin Masoyi...
Page 11- Kewa
Page 12- Samu da Rashi
Page 13- Mafita
Page 14- Assignment
Page 15- Kudin Fansa
Page 16- Daren Farko
Page 17- Headmaster
Page 18- Tarko
Page 19- Kura Da Fatar Akuya
Page 20- Plan
Page 21- Suspect
Page 22- A Week To Go
Page 23- Informers
Page 24- Bankwana
Page 25- Kiran Sirri
Page 26- Arrest
Page 27- Dare Dubu
Page 28- Next Assignment
Page 29- Soyayya
Page 30- Visiting
Page 31- Alkalamin Kaddara
Page 32- Nusaiba
Page 33- Baby Boy
Page 34- Matar Haidar
Page 35- Award Morning
Page 37- Kambun Baka
Page 38- Kai Amarya
Page 39- Kukan Zuci
Page 40- Reconciliation
Page 41- Karshen Munafuki...
Page 42- Ruwan Zuma
Page 43- Class Rep.
Page 44- Happy Birthday
Page 45- WTTW
Page 46- Barrista Khairi
Page 47- Rama Sharri da Alheri
Page 48- Kauyawa
Page 49- Court
Page 50- Luck
Page 51- Babbar Kotu
Page 52- Medical Report
Page 53- Doctor Marzuq
Page 54- Shaidar Zur
Page 55- Confess 1
Page 56- Confess 2
Page 57- Wata Sabuwa...
Page 58- Women Leader
Page 59- Bakar Manufa
Page 60- Komai Ya Yi Farko...

Page 36- I Love You

143 26 2
By PrincessAmrah

Page 36-

Ana tashi daga office muka nufi gida tare da shi ya sauke ni sannan ya wuce. Na tarar gidan har yanzu da mutane ana ta zuwa yi wa Umma murnar kambun girmamawar da na samu. Bayan na gaisa da mutane na shige daki saboda ina da bukatar hutawa. Wanka kawai na yi ko abinci ban nema ba na kwanta sai bacci.

Sai daf da mgahriba sannan na tashi na nufi sallah na zuba abinci. Ina cikin ci Haidar ya kira ni. Ban dauka ba sai da na gama tas don na san idan na dauka abincin da ba zan gama ci ba kenan zai cika ni da daddad'ar hirarsa har sai abincin ya fice daga raina.
Ina gamawa na kira shi ya kashe sannan ya biyo kiran.
"Babydoll, yaya gajiya?"
"Alhamdulillahi. Na sha bacci sosai, ban jima da tashi ba. Kai fa?"
"Ban yi ba fa wallahi. Hidimarki ba za ta bar ni hutawa ba buttercup har sai na ga na kammala da komai."
Na yi murmushi don na gane hidimar tawa da yake nufi.
"Thank you baby boy, I mean thanks for everything."
"Godiyan fa ta mece ce Muffin?"
Ya fada cike da shauki a cikin muryarsa.
"Thank you for loving me, a yadda nake din nan. Thank you for supporting me, thank you, thank you, thank..."
"It's okay dan Allah. Na ji, ni ma thank you for loving me. Shi kenan."
Na saki murmushi. Komai na Haidar abun so ne gare ni. Na gama yarda cewa Haidar shi ne cikon farincikina, shi ne duniyata bakidaya.
Sai kawai na saki kuka, irin kukan da ake kira da na farinciki. A baya, na cire tsammanin samun soyayyar namiji, sai dai a yanzu da Haidar ya shigo cikin duniyata, na yakice wancan tunanin nawa. Ashe shi ya sa ba a so bawa ya yanke wa kansa kauna.
"Kukan fa?"
Ya tambaya yanayin muryarsa na sauyawa.
"Na tsantsar soyayyarka ne Aliyu Haidar..."
"Ki taimaka ki adana min hawayen nan da duk kalaman har sai na zo ki yi su a gabana. Na miki alkawarin samun kyakkyawan martani."
"Na ki wayon."
Na fadi ga dariya ga kuka.
"I love you so much."
Na fada hade da yanke wayar, ina jin cewa na gama samun dukkan farincikin duniya tunda na samu Haidar a matsayin mijin aurena.

***

Bayan sati uku da daura aurenmu ina zaune ina karatun wani katon littafi, daya daga cikin wadanda Mama ta ba ni na Ummu, sai Umma ta kwala min kira. Ajiye littafin na yi bayan na amsa na nufi inda suke zaune ita da Sadiya, Safra sun fita da wata kawarta.
Zama na yi, na mata sannu da hutawa ta amsa, sannan ta ce,
"Da ma game da batun tarewar ki ne, mun yi shawara da Mamanku, da su Marwa, a kan karshen watan gobe za a yi biki ki tare. Tunda dai Aliyun ya saukaka mana komai ya ce ba ya bukatar a kai ki da komai. Amma duk da haka akwai kayayyankin kitchen da na fara tara muku ke da Safra, ai kin san da su ko?"
Ba ta jira na ba ta amsa ba ta ci gaba da cewa,
"Zan kara wadansu abubuwan sai a kai miki. Hankalina zai fi kwanciya ki kalli wani abun ki tuna naki ne na aure da mahaifiyarki ta saya miki."

Cike da tausayi da kaunar mahaifiyata na ce,
"Umma, don Allah kar ki ba kanki wahala. Tunda ya ce ba sai an kai komai ba, ki bar wa Sadiya nawan, kudin hannunki kuma ki ci gaba da tara wa Safra. Ita ma Sadiyar ai ba wuya kin ga lokaci ya yi, tunda girman mace ba wuya gare shi ba. Ki yi saving kudinki don Allah."

Ta gyada kai da guntun murmushi,
"Ba za ki gane ba a yanzu Khairi, sai nan gaba kadan za ki san hakan da na yi daidai ne. Kowacce mace tana alfahari da abin da iyayenta suka yi mata na aure. Ban ki ta Aliyun ba, ba kuma zan hana shi ba tunda da kansa ya yi niyya. Amma ni ma zan kara nawa a kan nashi, ko da za ki hada abu biyu iri daya ne, ai dai watarana za ki kalla ki tuna da ni ko? Akwai ma sadda za ki gwada wa 'ya'yanki ki ce wannan naki ne na aure da mahaifiyarki ta saya miki."

Hawaye na saki tare da gamsuwa da maganarta. Ga wata irin kunya kuma da ta lullube ni.

"Idan kun yi waya da shi Aliyun, ki shaida masa in shaa Allahu karshen sabon watan da za a shiga jibi za a yi taron biki. 'Yan'uwa da dangina su zo su shaida, tunda an daura aure a gaggauce ba tare da an gayyaci kowa ba."
Kaina sunkuye kasa na amsa mata, hade da mikewa na koma daki.

Ina kiran Haidar ya dauka, wani abu da ya ba ni mamaki saboda duk sadda zan kira shi sai dai ya latse, ya kira ni. Amma yanzu ina kira ya dauka. Tun kafin in ce komai ya ce,
"Ga mu nan asibiti Buttercup, Nusaiba ce ba ta da lafiya yanzu Mami ta kira ta shaida min, an shiga emergency da ita."
Ta yanayin muryarsa kawai za a tsinci zallar tashin hankali a cikinta.

"Subhanallahi! Me ya same ta? Ko jiya fa mun yi waya da ita ba ta fada min ba ta da lafiya ba."
"Asthma ce ta yi attacking dinta."
Ya ba ni amsa cike da alhini.
"Allah Sarki! Allah Ya ba ta lafiya Ya sa kaffara ne. Zuwa an jima zan zo sai in duba ta. Nusaiba na da kirki sosai."
"Ba sai kin zo ba Buttercup, don ko kin zo din a yanzu ba barin ki za a yi ki gan ta ba, saboda mu ma ga mu nan a reception tsaye tun da muka kawo ta, sai dai tambayar update a kan halin da take ciki muke yi. Ko me kenan zan kira ki in shaa Allah, ko zuwa gobe ne sai in zo in dauke ki ki duba tan ko?"

Cikin damuwa na amsa masa da to, har ya yi min sallama sai kuma na ga bai kamata in kyale shi haka ba tare da na kwantar masa da hankali ba a matsayina na matarsa. Na ce
"Baby boy..."
A hankali ya amsa.
"Everything is going to be alright ka ji?"
Ya maimaita
"In shaa Allah."
"Ka kwantar da hankalinka. Za ta ji sauki, za ta ga bikinmu ni da kai, da yardar Allah."
"In shaa Allahu." Din dai ya sake maimaitawa.
"Ka yi ta ambaton Allah kana yi wa Annabi SAW kirari, kana istighfaari, tare da nema mata sauki a wurin Allah. Da izinin Allah daga nan zuwa anjima kadan za ta wartsake."

Sosai na fahimci ya ji dadin kalamaina. Sai da na ji ya dan samu nutsuwa sannan na yi masa sallama na yanke kiran.
Wata irin shakuwa ce tsakanin Haidar Turaki da 'yar'uwarsa Nusaiba Turaki, wacce ban taba ganin Yaya da kanwa sun yi irinta ba. A yadda take fada min, ko sirrinsa bai cika boye mata ba. Haka ita ma, idan sabon saurayi ko sabuwar kawa ta yi shi ne mutum na farko da zai sani. Duk wata bukata tata ba ta taba kwana da ita ba ba tare da ya cika mata ita ba, matukar dai ta fada masa. Wannan dalilin ne ya sa ni ma ta dauki soyayyar duk duniya ta dora a kaina. Take kyautata min tamkar jininmu daya. Ni ma kuma ganin hakan ya sa ta shiga raina sosai, zuciya tana son mai kyautata mata.

Jiki sabule haka na kasance har sai da Umma ta fahimta, tana tambaya ta na shaida mata Nusaiba ce ba lafiya, asthma ta tasar mata tana ma asibiti kwance. Ita kanta ta shiga alhini don Nusaiba kowa nata ne. Daga lokacin da ta fara zuwa gidanmu, zuwa yanzu ta yi zuwa ya kai biyar, kuma duk zuwan da za ta yi akwai abin da za ta riko wa Umma wai na gaisuwa ne.
Haka dai muka kwana daga ni har kannena cike da tunanin halin da take ciki. Mun yi waya da Haidar fiye da bakwai ina tambayarsa update amma sai ya ce har yanzu dai tana emergency ba a bari sun shiga ba.

Washegari da safe bayan na yi wanka, ko karyawa ban yi ba na kira Haidar na fada masa ga ni nan zuwa asibitin.
"Kin yi breakfast?"
Ya tambaye ni cikin sanyin murya. Na amsa masa da a'a sai na dawo tukunna.
"Duka-duka karfe tara da rabi yanzu Buttercup, ki samu ki nutsu ko ruwan zafi ne ki sha, in ya so ko zuwa sha biyu zan zo in dauke ki sai ki duba ta."
Ba don na so ba na amsa masa da to. Don ni kam burina in duba ta, an ce ka kula da mai kula da kai.

Sha biyu da kusan rabi ya zo. Har ciki ya shigo ya gaishe da Umma ta yi masa ya mai jiki, ya shaida mata da ta ji sauki sosai don an mayar da ita ma amenity. Umma ta ji dadi sosai ta yi mata addu'a sannan muka tafi, na so tafiya da daya daga cikin su Sadiya amma ba su nan duk suna makaranta.
Riga da skirt ne na saka na maroon din leshin da ya yi daidai da kalar farar fatata. Sannan na yafa golden din medium mayafin da ya tafi da kalar adon golden da ke jikin leshin. Mayafin bai wani kare surar jikina sosai ba, duk shape dina ya bayyana, ga kuma heel shoe da na sa wanda ya sanya tafiyata komawa tamkar 'yar wasan fashion.
Ya riga ni fitowa ya jira ni a mota, tunda na fita idonsa yake a kaina, fuskarsa daure babu annuri har na karaso na shiga motar.
Gaishe shi na yi amma sai bai amsa ba, ya ci gaba da tukinsa har zuwa sadda muka hau kan babban titi.

"Kar ki kara yafa irin wannan mayafin."
Ya furta ba tare da ya kalle ni ba, idanuwansa na saitin titi kamar ba shi ba ne ya yi maganar.
Shiru na yi ina jin wani iri don ba mu saba irin haka da shi ba, ban saba ganin sa a irin wannan yanayin ba. Sai na mayar ko saboda jikin Nusaiba ne ya sanya bai sakar min fuska ba, duk da ya sakar wa Umma sosai.

"Kin ji ni ba? Wallahi duk ranar da kika kara sanya irinsu sai kin koma kin sauya shi da dogon hijabi, ko kuma ma ki fasa fitar duka."
Sai yanzu na gane. Wato kishi ne ke dawainiya da shi ashe. Haka nan ake cewa kishi kumallon mata, Hausa ce kurum, amma kishi kumallon maza shi ya fi cancanta a fadi.

"Am sorry."
Na ce ina dukar da kaina.
"It's Okay."
Ya fadi amma bai yi min murmushin ba ballantana in sa ran zai amsa gaisuwata. Duk sai na sha jinin jikina don bai saba daure min fuska irin haka ba.




Amrah A Mashi❤️

Continue Reading

You'll Also Like

64K 5.6K 36
U+Z ဒီနေ့မင်းလွင် + ဒီယောရာဇာဓိရာဇ်
191K 15.4K 42
story is starting with a business tycoon Vansh raisinghania and a middle class girl Riddhima. Vansh hates women because of his past and he wants a su...
99.7K 6.5K 16
حسيت كل جسمي مات من الخوف ورجفه لزمتني شنو الي جاي يصير ياربي ماجاي يستوعب عقلي شنو الي أسوي راح اروح بالرجلين ! اباوع الة متمد گبالي وأگع شلون أگعد...
155K 10K 40
WANNAN LABARI NE DA WASU BANGARE YA FARU A GASKE. BAN CANJA SHEKARUN YARINYAR BA KO ALAKA BA,AMMA NA CANJA SUNA, SANNAN BABU SUNAN GARI DA KUMA ANGU...