DARE DUBU

By PrincessAmrah

11.5K 1.5K 68

Kaddara! Mece ce ita? Yaya rayuwar yarinya mai karancin shekaru za ta kasance a lokacin da ta tsinci kanta ci... More

PROLOGUE
Page 01- Khairi
Page 02- Damuwa
Page 03- Fargaba
Page 04- Mafarin Komai
Page 05- Masauki
Page 06- From God We Are...
Page 07- Tushiya...
Page 08- Zalunci
Page 09- Dream
Page 10- Fushin Masoyi...
Page 11- Kewa
Page 12- Samu da Rashi
Page 13- Mafita
Page 14- Assignment
Page 15- Kudin Fansa
Page 16- Daren Farko
Page 17- Headmaster
Page 18- Tarko
Page 19- Kura Da Fatar Akuya
Page 20- Plan
Page 21- Suspect
Page 22- A Week To Go
Page 23- Informers
Page 24- Bankwana
Page 25- Kiran Sirri
Page 26- Arrest
Page 27- Dare Dubu
Page 28- Next Assignment
Page 30- Visiting
Page 31- Alkalamin Kaddara
Page 32- Nusaiba
Page 33- Baby Boy
Page 34- Matar Haidar
Page 35- Award Morning
Page 36- I Love You
Page 37- Kambun Baka
Page 38- Kai Amarya
Page 39- Kukan Zuci
Page 40- Reconciliation
Page 41- Karshen Munafuki...
Page 42- Ruwan Zuma
Page 43- Class Rep.
Page 44- Happy Birthday
Page 45- WTTW
Page 46- Barrista Khairi
Page 47- Rama Sharri da Alheri
Page 48- Kauyawa
Page 49- Court
Page 50- Luck
Page 51- Babbar Kotu
Page 52- Medical Report
Page 53- Doctor Marzuq
Page 54- Shaidar Zur
Page 55- Confess 1
Page 56- Confess 2
Page 57- Wata Sabuwa...
Page 58- Women Leader
Page 59- Bakar Manufa
Page 60- Komai Ya Yi Farko...

Page 29- Soyayya

172 28 3
By PrincessAmrah

Page 29

Wasu irin tsumammun hawaye ne na ji suna sauka a bisa kumcina, wadanda suka jima suna son saukowa ina danne su saboda son shafe duk wani babin fyaden da aka taba yi min.
Na dukar da kaina, kuka nake sosai, irin kukan nan da bai da sauti mai yawa, sai dai karkarwar jiki.
Ganin yadda kafadata ke hawa da sauka ya sanya shi fadin
"Kina tayar min da hankali Khairi, kukanki daidai yake da duk wani tashin hankalina. Gabana yana faduwa, ina jin kamar ban samu karbuwa ba ne."

Ta ina ma zai samu karbuwar kuwa bayan babu tsarin aure a rayuwata? Me ya sa yake neman dagula tsarina a lokaci guda? Na tabbata idan Umma ta ji zancen nan da gudu za ta amince, ta kuma tilasta min ko ina so ko ba na so.

"Ban zo nan da nufin sanya ki kuka ba Khairi, ki daina zubar min da wannan precious hawayen naki don Allah. Ba na so."
Rarrashina yake sai dai ko alama ba shiga ta yake ba. Yadda aka haike min nake tunawa, sai kuma darajar nan da ake yawan nanata duk budurwar da ta yi rashinta ta yi babban rashin da babu abin da zai iya cike gurbinta.
Budurcin nan da kowacce mace ke burin isar da shi ga mijinta; yadda nake yawan jin ana girmama budurci amma ni na yi rashin nawa. To me ya yi saura wanda zan kai wa mijin aurena?

Ina kallon sa ya dafe keya da dukkanin tafukan hannuwansa, ya ma rasa abin da zai fadi sai idanuwansa da nake jin suna bibiyar duk wata halitta tawa.

Mun jima a haka kafin na ce
"Ba zan boye maka komai ba Sir, ba zan iya aurenka ba. Ba wai don ina kin ka ba face dalilai guda biyu..."
Na yi kokarin shanye kukana, sannan na ci gaba da fadin
"Dalili na farko shi ne aure shi ne abu na farko da na cire rai da shi a rayuwata. Sannan abu na biyu, ina tsoron abin da zai je ya dawo..."
"Kamar me kenan?"
Ya yi saurin tarba ta.
"Gori..."
"Wane irin gori? Wace irin magana ce kike yi haka Khairi for God's sake kamar wani dan yaro? Ina ce na san da raping din naki da aka yi amma duk da haka na kawo kaina? Ya kamata ki san ni ba irin wasu mazajen ba ne, na san me nake yi fa."

Shiru na yi ina samun 'yar nutsuwa da kalaman nashi, sai dai ni ba wai shi din nake ji ba, dangi; ba lallai ba ne su karbe ni tare da mummunar kaddarata ba.
Kamar ya san abin da nake tunani kuwa sai cewa ya yi
"Ba wani zai zauna min da ke ba, ni na ji zan iya. Da kaddarar da ta taba afka mikin nake son ki, don zan iya cewa ma tana daga cikin dalilan da suka assasa kaunarki a cikin zuciyata. Da tausayinki na fara, ashe da gaske ne da ake cewa tausayi soyayya ce. Har ga shi zuciyata ta cika taf da kaunarki, irin cikar da ke daf da fara ambaliya."
Ya saki guntun murmushi.
"Da dukkanin zuciyata nake kaunarki Khairi. Burina ki zama matata nan da dan lokaci kankani."

Ya daure ni mini zuciya tam! Sai kawai na yi shiru ina tunanin ta yadda zan iya kauce masa. Kafin in samu mafita ya mike tsaye tare da fadin,
"Idan kin shiga ki turo min kanwata Halimatu. Sannan Allah na ganin ki idan kika ci gaba da zubar min da tsadaddun hawayen nan naki. I love you so much Buttercup."

Tamkar wadda aka daure wa kafafuwa haka na ji, na yi yunkurin tashin amma sai ji na yi tsayuwa ma tana Neman gagara ta. Da kyar dai na samu na taka na shiga daki. Tun kafin in fada wa Sadiya sakon kiran ya da yake ta fita don babu tazara ana iya jiyo duk maganganun da ake yi.

"Allah Yaya wannan kukan samun wuri ne kike yi. Ki samu mutum mai yi miki irin wannan kaunar ai sai ki daga hannuwa ki gode wa Allah. Mutum kyakkyawa da shi ga kudi ga kwarjini, komai ya hada fa."
Tsaki kawai na yi ina jin yadda kaina ke sarawa saboda kukan da na yi. Sai ga Sadiya ta shigo da rafar 'yan dari biyar ta watso su a kan gado hade da sakin ihu tana tsalle.

"Na rantse muku mutumin nan karshe ne. Yaya Sadiya kin amince kamar yadda na amince ko kuwa dai za ki je ki yi tunani ne irin na Yaya Khairi?"

Ni dai ina jin su sai murna suke yi. Can kuma sai ga Umma ta shigo, wuri ta nema ta zauna, sannan ta dube ni da alama magana mai muhimmanci take son ta yi da ni.
Na sunkuyar da kaina da idanuwana da ke min radadin kuka. Ta ce
"Aliyu ya yi min magana yanzun a tsakar gida kafin ya fita. Ya shaida min yana son aurenki idan har ba a yi miki miji ba, ni kuma na amsa masa a kan ya nemi soyayya daga wurinki, ni dai don ta ni babu matsala. Sannan na shaida masa zan fada wa Kanin mahaifinki a waya, sai ya ba shi lokacin da zai je ya nemi izini a wurinsa tunda ni mace ce, kuma bai kamata a soka mace cikin lamarin neman aure ba."
Ta yi shiru hade da kama hannuna, sannan ta dora da
"Ban ga aibunsa ba UmmulKhairi. Tunda ke da kanki kike yabon kyawawan halayensa tun farko fara aikinki a garin nan. Sannan duk wanda zai girmama naka to babu tamkarsa. Ni dai Aliyu ya yi min dari bisa dari, amma ba zan yi miki tilas ba, sai dai zan iya ba ki shawara a matsayina na mahaifiyarki, uwar da take son farincikin diyarta. Ki tuna kaddarar da ta hau rayuwarki, ya sani amma duk da haka ya zabe ki a matsayin wadda yake son aure. Sannan ko ba komai ya taba aure, mutuwa ce ta raba shi da matarsa, kin ga ya san ciwon kansa, ina ji a jikina ba zai wulakanta ki a gaba saboda kaddararki ba."

Na saki kuka da karfi bayan na fada jikinta, na ce
"Umma ba wai shi din nake ji ba, kar a je sai na saki jiki komai lafiya kuma a samu masu goranta min daga gefe. Kin san an ce ba a mugun sarki sai mugun bafade."
Umma ta ci gaba da shafa bayana a hankali,
"Haka ne Khairi. Sai dai ki sani shi ne mai auren ba kowa ba, kuma shi din dai ne ya ce ya ji ya gani zai iya. Don haka kar ki dauki wannan a matsayin matsala. Sai dai abu daya da nake so ki kwana da saninsa shi ne; ba kowa ba ne zai kaunace ki ba daga danginsa, ba wai shi din ba ma, duk wanda za ki aura  ba za ki iya tsallake wadannan surutan daga bakin mutane ba. Dole ne sai kin toshe kunnuwanki, ki ji ki hakura, farincikin mijinki kawai kike so ba na kowa ba."

Sosai kalaman nata suka sanyaya zuciyata. Ta fahimci hakan kuwa sai ta ci gaba da amfani da kalaman da ta san za su kwantar min da hankali har sai da ta samu galaba a kaina.

***
Ina kwance dadaddare sai ga kiran sa ya shigo wayata. Kura wa wayar ido na yi ina tunanin a wanne matsayi zan dauki kiran, ya ce idan ba a Office muke ba shi ba Oga Ahmad ba ne, sunansa Aliyu Haidar Turaki. To daga Aliyun ma kuma ya koma matsayin mai neman aurena. Har yanzu zuciyata ta gaza tantance muhallin da yake. Tabbas ba na jin kiyayyarsa, haka kuma ba na jin sa can cikin zuciyata saboda dalilan nan guda biyu da na fada wa Umma. Sai dai kuma maganganunta sun shige ni; da ma ba lallai ba ne in samu karbuwa a wurin kowa, dole in yi facing different challenges na rayuwa tunda na shiga halin da ba lallai in iya ketare challenges din ba. Ita mace da ma ko babu raping ba lallai ba ne kowa ya so ta a cikin dangin miji, to ballantana kuma mace irina, wacce ta hadu da mummunan tsautsayin nan.

Har wayar ta tsinke ban dauka ba ina ta tunane-tunane, can kuma sai ga kiran nashi ya sake shigowa. Na dauka cikin sanyin murya na masa sallama, a maimakon ya amsa sai ajiyar zuciya da ya sauke, can ya nisa hade da fadin,
"A cikin dictionary dina Khairi, babu wani abu wai shi hakuri, musamman kuma hakuri irin wanda zai cutar da ni. Naci gare ni sosai. Don haka ki sa a ranki ba zan daina damun ki ba har sai sadda kika aminta da batun aurena."
"Ina wuni."
Na bude baki na gaishe shi ba tare da ba shi martanin maganar da ya yi min din ba."
"Kina lafiya?"
"Alhamdulillah."
Na ba shi amsa cikin sanyin murya.
"Ya Ummanmu take? Ina kannena kuma?"
"Duk suna lafiya alhamdulillah."
"To ma shaa Allah. Ni kullum ina tambayar ki tamu Umman amma ke ba ki taba tambaya ta tawa ba, ko?"
Dafe baki na yi ina jin kunya sosai don da gasken ban taba tambayarsa ba, sau daya ya taba yi min zancen ya ba ta labarin namijin kokarin da na yi a wurin aikina amma daga nan ban sake jin sunanta ba a bakinsa.
"Ka yi hakuri Sir..."
"Buttercup..."
Ya yi gaggawar dakatar da ni.
"Don Allah ki daina kira na da Sir din nan, ni dai har a office din ma na yafe, please ki dinga kira na da Haidar idan ma sunan soyayyar ba zai samu ba."

Bayyananniyar dariya na yi saboda yadda ya yi maganar cikin wani yanayi. Sai kuwa ya sauke ajiyar zuciya tare da sakin hamdala.
"Ba ki ji yadda dariyarkin nan ta sanyaya zuciyata ba wallahi. Dan Allah Khairi ba sai mun je da nisa ba ki aminta da ni don tuni zuciyata ta fada min kina so na, sai dai kin kasa karbar gaskiyarta ne. Kuma ni dai zuciyata ba za ta yi min karya ba tunda ba ta taba yin karyar ba. So nake gobe idan na je gaishe da Mamina weekend, in ba ta kyakkyawan albishirin na samu matar aure kamar yadda take ta min fata tun bayan rasuwar Maryam."

A daidai wannan lokacin ba zan iya ci gaba da yi masa shiru ba bayan shawarwarin da Umma ta ba ni da kuma yadda zuciyar tawa ta aminta da batun aurensa duk da ba na jin digin soyayyarsa a cikinta. Don haka sai na ce masa
"Idan ka je gidan Mami gobe ka gaishe ta, sannan ka fada mata ta shirya tarbar UmmulKhairi a matsayin matar danta Oga Haidar."
Daga nan na yanke wayar cike da kunya ina jin cewa hakan da na yi shi ne daidai, duk da ba zan fasa yi wa kaina addu'ar tabbatuwar alkhairi ba. Idan har aurena da Haidar ya kasance, na sani shi ne alkhairi gare ni. Idan kuma bai yiwu ba to babu alkhairi a ciki, saboda koyaushe cikin neman zabin alkhairi a rayuwata nake, haka mahaifiyata ma.
Allah Sarki Ummu! Sai kuma tunaninta ya zo min. Da tana raye da na tabbata a wurinta Haidar zai yi kamun kafa saboda muhimmancinta gare ni. Da tana nan da tuni ta fara batun shirye-shiryen aure tunda kullum burinmu shi ne mu ga auren junanmu bayan mun zama likitocin da muke mafarkin zama.
Amma ga shi a lokacin da na samu mijin aure babu ita, babu Ummu a duniyar ta tafi ta bar ni.
Na saki wani irin kasallallen kuka, ina jin cewa tabbas aikina bai kare ba, har sai na tabbatar da wadanda suka kashe Ummu sun shiga hannun hukuma kamar yadda na yi silar kama wadanda suka yi min fyade a hasashen su suka kashe ta.

Amrah A Mashi❤️

Continue Reading

You'll Also Like

45.1K 2.2K 51
"Don ubanki wanki dana barmiki kimin shine kika kiyimin Kika zauna kika rungume wannan shegiyar d'iyar taki wallahi koki aje ta ko kuma yanzu jikin k...
132K 8.6K 55
Kallon kitse ba litaffina bane na marubuciyar nan ne Halima Abdullahi k/mashi
2.3M 70.5K 98
Previously called Older Brothers Part 1 Completed (Alternate version) part 2 Ongoing "T-trust me?" "Always." It was the promise that they were never...
538K 35.2K 76
A story of a young Prince and his Mother with two sisters who have been deprived of their rights by a very heartless woman #MAGAJIYA#.......