DARE DUBU

By PrincessAmrah

11.5K 1.5K 68

Kaddara! Mece ce ita? Yaya rayuwar yarinya mai karancin shekaru za ta kasance a lokacin da ta tsinci kanta ci... More

PROLOGUE
Page 01- Khairi
Page 02- Damuwa
Page 03- Fargaba
Page 04- Mafarin Komai
Page 05- Masauki
Page 06- From God We Are...
Page 07- Tushiya...
Page 08- Zalunci
Page 09- Dream
Page 10- Fushin Masoyi...
Page 11- Kewa
Page 12- Samu da Rashi
Page 13- Mafita
Page 14- Assignment
Page 15- Kudin Fansa
Page 16- Daren Farko
Page 17- Headmaster
Page 18- Tarko
Page 19- Kura Da Fatar Akuya
Page 20- Plan
Page 21- Suspect
Page 22- A Week To Go
Page 23- Informers
Page 24- Bankwana
Page 25- Kiran Sirri
Page 26- Arrest
Page 28- Next Assignment
Page 29- Soyayya
Page 30- Visiting
Page 31- Alkalamin Kaddara
Page 32- Nusaiba
Page 33- Baby Boy
Page 34- Matar Haidar
Page 35- Award Morning
Page 36- I Love You
Page 37- Kambun Baka
Page 38- Kai Amarya
Page 39- Kukan Zuci
Page 40- Reconciliation
Page 41- Karshen Munafuki...
Page 42- Ruwan Zuma
Page 43- Class Rep.
Page 44- Happy Birthday
Page 45- WTTW
Page 46- Barrista Khairi
Page 47- Rama Sharri da Alheri
Page 48- Kauyawa
Page 49- Court
Page 50- Luck
Page 51- Babbar Kotu
Page 52- Medical Report
Page 53- Doctor Marzuq
Page 54- Shaidar Zur
Page 55- Confess 1
Page 56- Confess 2
Page 57- Wata Sabuwa...
Page 58- Women Leader
Page 59- Bakar Manufa
Page 60- Komai Ya Yi Farko...

Page 27- Dare Dubu

164 27 2
By PrincessAmrah

Page 27

A hankali na dago kaina ina son neman izinin tashi in tafi, kwatsam idanuwana suka shiga cikin nashi idanuwan, lumsassun nan farare tas. Na yi gaggawar sauke kaina amma sai na ji nashi har yanzu suna kaina, duk sai na tsargu na kasa fadin komai ma.
Mun dauki tsawon lokaci a hakan, kafin ya dan yi gyaran muryar da ya sanya ni sake dago kai sai kawai ya kara sakin murmushi.
"Sir...sir...permit me to..."
"You can go. Ki huta sosai at least for a week kafin ki dawo aiki."
"Sir, zan iya zuwa wurin kidnappers din nan in gan su? I want to confirm something."
"Are your really sure za ki iya ganin su? Ba za su tayar miki da kowanne irin tsohon tabo ba?"
Na daga kai, tabbas za su tayar min din, amma ina son yin magana da ko da daya ko biyu ne daga cikinsu.
"Sir, I want to discuss something with them. Ina son yin confirming ko su suka kashe min Ummu."
"Ko su ne ko ba su ba ne ba dole za a hukunta su Khairi."
"Yes Sir, na san za a hukunta su. Kawai dai..."
Ya katse ni,
"They raped you aren't they?"
Na jinjina kai.
"Za a hukunta su, mummunan hukunci. Kin san cewa ya halalta mu kashe su ba dole sai mun tura su kotu ba?"
Na sake daga masa kai.
"So ki kwantar da hankalinki, ba ki da bukatan ganin su don kar ma ki koma gida a rikice, ki rikita mana Umma, alhali ya kamata a ce kin koma ne cike da nishadin samun nasararki."

Na dan shafi fuskata, ba kuma zan iya sake musa masa ba, sai godiya da na yi na tashi bayan ya ba ni izinin tafiya.

***
Na yi murmushi, na yi dariya, na yi nishadi, sannan na yi farincikin ganin mahaifiyata. Da farko na ma rasa ta inda zan nuna farincikin nawa saboda tsananin kewarta da na yi. Na yi kewar kannena, na yi kewar girkin Ummana, sannan na yi kewar gida bakidaya; duk kuma ban tabbatar da hakan ba sai da na dawo, muka yi kicibis da su.

Uwa-uba kuma ita Umman, na tsinci nishadi da walwala a saman fuskarta, musamman sadda nake ba ta labarin nasarar da muka samu.
"Umma, addu'arku na da matukar tasiri a gare ni, na yarda har da ita, ita ce jigon nasarar ma bakidaya."
"Na san tasirinta gare ku Khairi, shi ya sa ba na kasa a guiwa wurin sanya ku a addu'o'in dukkanin sallolina. Alhamdulillahi! Ina kara godiya ga Allah da Ya nuna min samun nasararki Khairi, ina rokonSa AzzawaJalla da Ya ci gaba da ba ku nasara a dukkan komai."

Tuwon shinkafa da miyar ganye wadda ta ji ganyen ugu aka dafa, nan da nan Safra ta cika gabana da shi, Sadiya kuma ta kawo min kunun ayar da ta yi dazu na tarbar saurayin Safra.
Na yi mamakin jin wai Safra ce da saurayi, na hau tsokanarta tana rufe fuska.
"Wai Umma da yaushe aka fara soyayyar nan ne? Duka-duka yaushe Safran ta girma da har ta fara samari ban sani ba? A ina ta same shi?"

Umma ta yi murmushi ta ce
"Ke dai ki zauna a nan kawai. Bambancin ke da ita fa bai cika shekara biyu ba, kuma ke kanki yanzu kin zarta ashirin a duniya. Kin ga kenan ba abun mamaki ba ne don wadda ta haura wa shekara goma sha takwas ta yi aure. Ni din na  ma ina da sha shida cif aka daura aurena da mahaifinku."

Na kai lomar tuwo a bakina ina jin wani irin dandano mai dadi, dandanon nan da na yi kewa kwarai.
Na ci gaba da ci ina sauraron Umma da ke fadin ni ma ya kamata in samu mijin aure na ci gaba da aikin a gidan mijina idan ya yarda.
Ba ta sani ba ne, amma har yanzu ban taba jin ina sha'awar yin aure ba, saboda ba ni da abin da duk wata mace ke tutiyar zuwa gidan miji da shi. Tuni an raba ni da shi, kuma ba na son in yi aure a zo ana goranta min daga baya; ba na son a fama min tabon da ya riga ya shafe daga zuciyata.

Har ta yi ta gama dai ban ce komai ba, na gama cin tuwona na wanke hannu sannan na shige daki.
Wanka na yi na dauko kaya marassa nauyi na sanya sannan na zira doguwar hijabi na fito.

"Umma, ina son zuwa gidan Mama, na yi kewarta sosai ita da Baba."
"Kin kuwa san Baban naku ma yana nan ya zo, yana ta addu'ar ki dawo kafin ya koma. A dawo lafiya to, ki gaishe su."

Na kama hanya na fita.
Ko da na je Mama har rungume ni ta yi saboda farincikin gani na, ta kuma taya ni farincikin nasarar da muka samu.
Baba ma baki har kunne, yana kara jinjina min musamman da na fada masa ta hanyar da aka samu kama kidnappers din nan da suka jima suna addabar mutane kuma gwamnati ta kasa aikata komai a kansu.

Tambayar nan da nake son yi wa Baba na yi masa, ya dan yi shiru jim, kafin ya ce
"Ashe ba mu taba yin maganar nan da ke ba Khairi."

Mama ta gyada kai,
"Ina fa ta ba mu damar yin duk wata magana ma da ta shafi mutuwar Ummu? Tun lokacin na so mu tattauna a kai amma na lura da ko zancen ma ba ta so. Shi ya sa kawai na rabu da ita, na tabbata akwai ranar da za ta so ta ji, tunda ba nan za ta dawwama da danyen raunin mutuwar ba."

Baba ya yi gajeren murmushi, irin wanda bai da alaka da nishadi, ya ce
"Tabbas bayan na ajiye kudin sun dauka a inda suka sanya ni ajiyewa, da ranta muka bar wurin, ina ta jin dadin ganin ta cikin aminci, ita kuwa maganar farko da ta fara hada mu ita ce
"Baba, a taimaka a karbo min Khairi, Baba wallahi zama a wurin nan babu dadi, muna mu biyun ma babu dadi ballantana kuma da babu ni. Ban san yaya za ta ci gaba da rayuwa ita daya a wurin nan ba."
Na dinga tausarta ina ba ta tabbacin ke ma za a karbo ki da izinin Allah.

Ban san hawa ba ban san sauka ba, ban san daga ina harsashin bindiga ya dirar mata a kirji ba, sai kawai zubewarta na gani. Ban koma ta kan neman wanda ya harbetan ba sai ta kanta, na dinga jijjiga ta ina kiran sunanta amma shiru, na daga hannunta ya koma ya langabe, na saita kunnuwana saitin zuciyarta amma sai na tsinci bugun numfashinta tsaye cak! Ba ya tafiya. Da karfi ta sauke wani irin ajiyar zuciya, wanda ya yi daidai da fitar dukkanin numfashinta.
Babu wanda ya san abin da ya faru har sai da asuba, ko mahaifiyarta ga ta nan ba ta sani ba, saboda ban iso nan gidan ba sai asubar. Ban dauki gawarta ni kadai ba sai da na kira mutum biyu daga cikin 'yan'uwana, daya Yayana sai Kawuna suka zo muka dauke ta, daga nan kuma gidan Kawun nawa muka nufa tunda duk mazauna garin Sassanya ne, kuma ya fiye mana kusa daga dajin a kan mu taho nan Katsina.
Sai da asuba ne muka iso nan din.
Wasu daga cikin dangi da mutanen arziki sun nemi mu sanar da hukuma amma sai na dage a kan lallai a bar zancen kawai, ai lokaci ya riga ya kure, kafin a tafi ake sallama ba sai an dawo ba. Kuma akwai wadanda suka fi mu kudi da mukami, ba su sanar da hukuma ba, ko kuma sun sanar din amma an kasa yi musu komai. To mu su waye da za a iya yi mana wani abu?
Da wannan hujjar muka share batun. Wai kuma da rana sai ga labarin ke ma wani mutumi ya tsince ki, da ya kai ki wurin hukumar garinsu shi ne su kuma suka kawo ki nan Katsina, a asibiti General. Wata kawarki ta je dubiya a dakin ne ta gan ki ta gane ki duk da ba a cikin hayyacinki kike ba, daga nan ne aka sanar da Fatima da 'yan'uwanki fa.
An samu kin dan farfado har kika tambayi Ummu aka shaida miki tana asibiti, sai kuma lum! Kika sake somewa.

Wannan shi ne ainahin abin da ya faru, ba wai tsintar gawar Ummu na yi ba kamar yadda da yawan mutane suka dauka. Da ranta na karbe ta, har magana mun yi, kafin kuma aka kashe ta murus har lahira."

Na sharce gumi hade da hawayen da ke kwance saman kumcina. Mun jima muna alhinin komai kafin na mike na yi musu sallama na tafi. Zuciyata cike da wasi-wasin ba kidnappers din nan suka kashe Ummu ba.
To idan su ne, da wace hujjar za su kashe ta?
Me ya sa za su kashe ta bayan an ba su kudi, kuma sun tabbatar da kudin sun kai adadin da Baba ya fada musu?
Sannan sun tabbatar babu dan sanda ko wani jami'in tsaro tattare da baba. Wadannan dai ai su ne dalilan da ke janyo su kashe mutum bayan an yi yarjejeniyar karbarsa.

Da wannan na isa gida zuciyata fal da tunani. Ina ganin dole sai Oga ya tsaya min na ga su Zaki, ta yiwu su fada min gaskiya. Idan ba su fada ba kuma zan roko Oga a kan a kai case din kotu, watakila za su bayar da tabbacin kisan Ummu, idan har sun rike ta din, don adadin mutanen da suke kamawa ba ma lallai ba ne su rike kowa.

Washegari na shirya na tafi asibiti dubo Aysha tunda an kwantar da ita ne saboda malaria da ta kama ta sosai. Ban wani jima ba saboda danginta sun zo daga Dutse idan ta ji sauki za su wuce da ita har ta dan dawo da kuzarinta.
Daga asibitin kai tsaye gidan Anti Maryam na je. Ta yi farincikin gani na ba kadan ba, ta ce
"Wallahi yanzun nan muka gama zancenki da Abban Rukayya, ya ce zancen scholarship din nan akwai yiwuwar ya taso. Na fada masa ai ko ya tashin ma ba za ki je ba saboda kina aiki yanzu, kuma kina kaunar aikinki."
Na yi shiru kawai sai murmushi da na yi.
"Sannu sannu da zuwa kanwata. Na yi kewarki sosai wallahi. Ina fatan an samu nasarar abin da aka je nema."
Duk da ba ta san inda na je da kuma aikin da na yi ba.
Da annuri a fuskata na ce
"Mun yi nasara sosai Anti Maryam, an kama wadanda suka yi garkuwa da ni, kuma suka yi min fyade."

Ta kwalalo ido tana kasa fadin komai saboda zallan mamaki ta ce
"Shin da gaske kike ko da wasa?"
"Da gaske Anti Maryam."
Na ba ta amsa ina dorawa da
"Aikin da na je yi kenan a kaiyen Kanya da ke cikin kauyukan Meshe. An kama su, har da informers din da suke garin duk an tafi da su, yanzu haka suna can kulle."

Tsabar farinciki har da rungume ni ta yi, da guntuwar kwallarta ta ce
"Wannan lamari ya yi min dadi Khairi. Hakika DARE DUBU na barawo ne, amma DARE GUDA daya tak sai ya kasance na mai kaya. Yau ga dubun azzalumai ta cika, watakila mu samu sassauci a yanzu, mutum ya yi tafiya a tsanake cikin kwanciyar hankali."

Muka ci gaba da hira har bayan la'asar sannan na mata sallama na tafi. Ina kara jinjina yadda matar ke kaunata da zuciyarta guda.
Haka Allah Yake lamarinSa, a lokaci guda sai Ya hada ka da wanda ba ka taba tsammani ba a rayuwarka, kurum don ya zama wani tsani na ginuwar farincikin duniyarka.


Amrah A Mashi❤️

Continue Reading

You'll Also Like

13.9K 1K 47
Rayuwa wani abu ne da kan zo mana da kalubale iri iri, wani muna iya fin karfinshi da taimakon Allah wani ko sede mu zubawa sarautar Allah idanu zuwa...
2.3M 70.4K 98
Previously called Older Brothers Part 1 Completed (Alternate version) part 2 Ongoing "T-trust me?" "Always." It was the promise that they were never...
16.9K 882 32
DR UMAIMAH USMAN BULAMA,Mace yar kimanin shekara ishirin da tara , Babbar surgeon A asibitin CITY TEACHING HOSPITAL , Aure Uku, ƴaƴanta uku . Mace m...
261K 10.7K 37
Complete story of a young girl Ummy.