DARE DUBU

By PrincessAmrah

11.5K 1.5K 68

Kaddara! Mece ce ita? Yaya rayuwar yarinya mai karancin shekaru za ta kasance a lokacin da ta tsinci kanta ci... More

PROLOGUE
Page 01- Khairi
Page 02- Damuwa
Page 03- Fargaba
Page 04- Mafarin Komai
Page 05- Masauki
Page 06- From God We Are...
Page 07- Tushiya...
Page 08- Zalunci
Page 09- Dream
Page 10- Fushin Masoyi...
Page 11- Kewa
Page 12- Samu da Rashi
Page 13- Mafita
Page 14- Assignment
Page 15- Kudin Fansa
Page 16- Daren Farko
Page 17- Headmaster
Page 18- Tarko
Page 19- Kura Da Fatar Akuya
Page 20- Plan
Page 21- Suspect
Page 22- A Week To Go
Page 23- Informers
Page 24- Bankwana
Page 25- Kiran Sirri
Page 27- Dare Dubu
Page 28- Next Assignment
Page 29- Soyayya
Page 30- Visiting
Page 31- Alkalamin Kaddara
Page 32- Nusaiba
Page 33- Baby Boy
Page 34- Matar Haidar
Page 35- Award Morning
Page 36- I Love You
Page 37- Kambun Baka
Page 38- Kai Amarya
Page 39- Kukan Zuci
Page 40- Reconciliation
Page 41- Karshen Munafuki...
Page 42- Ruwan Zuma
Page 43- Class Rep.
Page 44- Happy Birthday
Page 45- WTTW
Page 46- Barrista Khairi
Page 47- Rama Sharri da Alheri
Page 48- Kauyawa
Page 49- Court
Page 50- Luck
Page 51- Babbar Kotu
Page 52- Medical Report
Page 53- Doctor Marzuq
Page 54- Shaidar Zur
Page 55- Confess 1
Page 56- Confess 2
Page 57- Wata Sabuwa...
Page 58- Women Leader
Page 59- Bakar Manufa
Page 60- Komai Ya Yi Farko...

Page 26- Arrest

155 26 0
By PrincessAmrah

Page 26

Cikin sanyin murya yake rarrashina, yana kokarin kwantar min da hankali amma ban yi shirun ba har sai da na yi mai isa ta sannan na tsagaita.
Jin na yi shiru ya sanya shi fadin
"Ki kwantar da hankalinki Khairi, ki fada min abin da ya faru. Ko ba ki da lafiya ne? Akwai wani abu da ya kamata in sani?"
Cikin rawar murya na shaida masa komai, tun hirar mu da Shamsu har zuwa kiran sa da aka yi da labarin mutuwarsa.

Ina jin yadda ya sauke nannauyar ajiyar zuciya, ya ce
"Yanzu Khairi duk wannan uban kukan da kike na mutuwar Shamsu ne? To idan kuma labarin tawa mutuwar kika ji wane irin kuka za ki yi?"
Na yi shiru ina sauraren sa.

"Ya isa haka kin ji. Mutumin nan fa da ma he deserves it. Don ko ba su kashe shi ba soyayyar da yake yi miki ba za ta hana mu kama shi a hukunta shi a kan laifinsa ba. Kin ga kenan sun taimaka masa da suka kashe shi ai ko?"

Ban taba jin takaicin kalaman Oga Ahmad ba irin wannan lokacin. Duk da ba son Shamsu nake ba, ban taba jin soyayyarsa ba ko sau daya ba amma ba na kin sa, musamman da na ji tarihin mafarin fara aiki da su.
Ba tare da na ce komai ba na yanke kiran. Ina kallo yana ci gaba da kira amma na ki dauka. A karshe ma barin wurin na yi na koma gida ina jin zuciyata babu dadi.

Mutuwar Shamsu na daga cikin abubuwan da har in koma ga mahaliccina ba zan manta da su ba, saboda kamar abun ya zo ne baghtatan ba zato ba tsammani.
Daren ranar haka na kwana ban runtsa ba sai tunanin duniya, tunanin Ummu da ta tafi ta bar ni, don da a ce tana nan tare da ni, da yanzu ta rarrashe ni, da ta dora fuskata a saman kafadarta ta yi ta ba ni baki har sai sadda na samu sassauci. Sai dai tuni mutuwa ta yi mana yankan kauna, ta dauke min Ummu ba tare da noticing ba.

Washegari da sassafe ko karyawa ban yi ba sai ga kira ya shigo ta cellular phone dita ta Office, kai tsaye na gane daga wurin aiki ne, official call. Sai da na dudduba babu kowa ko a kusa da dakin sannan na dauka,
"Sagir is on the way, Sagir and Usman. Za ku yi arresting matar gidan nan, sannan za ta kai ku inda sauran informers din garin suke. Make sure everything goes smoothly. Mu ma muna hanyan shiga daji ne."
"But Sir...?"
"Na sani, you are not supposed to arrest them tunda silent assignment ne aikinki. But you have to. Tunda hakan ya kama ne, idan kika riga kika tafi tunda matar nan ta san ko ke wace ce, za ta iya guduwa ko kuma ta kawo wani dalili da zai bata mana aiki. So ki yi hakan kawai. Just arrest her, ki share da batun silent."
"Okay Sir."
Na furta ina jin wani irin yanayi mai kama da fargaba, shakku-shakku, mai sirke da farinciki kuma. Muryar Oga Ahmad ce, sai dai a yau cike take da seriousness, kamar ranar da na fara ganin sa, da kuma rana ta biyu da na gan shi a Kaduna. Wannan ba Oga Ahmad din nan ba ne mai nishadi, idan an shiga fagen aiki babu wasa, ba sani ba sabo.

Na ajiye wayar daga gefe na tashi na cire kaya na saka bakaken khakina da ban taba sanya su ba tunda na zo garin. Na mayar da cellular dina a cikin jikina, da ma bindigata tana cikin pant dina, na soka ID card a gaban aljihuna, na dora hula a bisa kai, sannan na zuba dogon hijabi ina jiran isowar su Oga Sagir.

Kasa cin komai na yi saboda yanayin da nake ciki, yau ce ranar farko da zan fara irin wannan aikin, dole ne komai taurin zuciyar mutum ya karaya ko yaya ne. Don haka sai na samu kaina da faduwar gaba.

Ban wani jima ba sai ga kira ya sake shigowa, na dauka na ji Oga Sagir ne, ya ce min ga su nan sun iso, suna kofar gida, ni ce mace, ni nake da damar arresting Inna Azumi su kuma za su karasa wurin fada domin su sanar da maigari abin da ke tafe da su.

Na zare hijabin da ke jikina sannan na cire har kaina, dan karamin hijabi mai tsayawa daidai wuya, irin wanda aka amince mana mu saka ne na sa sannan na dora hular khakina a saman hijabin. Na bude jakata na ciro dayar bindigata ba karamar da ke boye ba, na daura rufaffun takalmana sannan na taka a hankali na fice zuwa tsakar gida.
A lokacin duk matan gidan suna zaune kowa na sha'anin gabanta, Azumi kuwa tagumi ta rafka da alama hankalinta ma ba ya tattare da su.

Gani na da kalar wannan shigar ya sanya su duk kallo na fuskokinsu na nuna alamun mamaki. Na dauke kaina daga duban Amarya da ta gama cika da al'ajabi, na karasa daf da Azumi.
Bindigata na saita a daidai fuskarta, tamkar ban taba murmushi ba a duniya nake bin ta da kallo, yayin da duk su kuma iyalan gidan suke bi na da kallo, yaran gida kuwa wasu kuka suka fasa da alama sun san bindiga sun kuma san amfaninta ko da a talabijin ne. Cikin daurewar fuska na ce
"Kar ki kuskura ki motsa daga nan wurin, motsawarki daidai take da motsawar rayuwarki. You are under arrest."

Ta dora hannuwanta bisa kai tana fashewa da wani irin kuka,
"Don Allah ki yi min rai diyar nan. Ina ce da kika hana ni fita ba ki ga na sake fita ba? Me kuma na yi da za ki saita mini bindiga. Na roke ki da Allah kar ki kashe ni..."
Na zaro cellular phone dita na latsa kira,
"Gidan maigari Mati Amadu, copy. Azumi matar maigari Mati, copy."
Sannan na mayar da wayar a ma'ajiyarta, still bindigar tana saitin fuskar Azumi.
"Muna zarginki ne da hada baki da 'yan garkuwa da mutane kina ba su boyayyun bayanai game da wannan garin. Number two, muna zargin an hada baki da ke wajen sace d'an mijinki wanda kike riko, har aka kashe shi."

Ta zaro ido cike da tsoro ta ce
"Wallahi diyar nan ba ni na ce su kashe shi ba, ban kashe shi ba, na dai san na ce su sace shi don mu samu kudi daga wajen maigari, amma babu ni a batun kisan sa, hasali ma sai da na fada musu ban so su kashe..."

"Duk wadannan bayanan ba muhallin yinsu ba ne nan, kina iya tattara su watakila za su yi miki amfani a gaba."
Na juya kaina jin motsin mutane daga bakin kofa, sai ga maigari da tawagarsa ta fada, da Oga Sagir da Oga Usman biye da su.

Oga Sagir ya jinjina min tare da fadin
"Weldone UmmulKhairi. You did a good job."
Ya juya ga Azumi sannan ya dube ni,
"Handcuff her."
Na karbi ankwa daga hannun Oga Usman na zarga mata.

Maigari sai kuka, matansa kuka, yara kanana kowa kuka. A cikin kukan maigari ke fadin
"Kin cuci kanki Azumi, don ba zan ce kin cuce ni ba, kanki kika cuta. Kin ga yanzu za ki je ki kare rayuwarki ne a gidan yari, yayin da mu kuma za mu ci gaba da rayuwarmu cikin kwanciyar hankali.
Na jima ina rokon Allah a kan Ya kawo mana dauki, ya toni asirin duk wasu azzaluman da suke kewaye da mu, ashe wannan ranar tana nan zuwa, ashe kina daya daga cikin azzaluman nan da nake addu'a a kansu."
Ya juyo gare ni bayan ya share hawayensa, ya ce
"Kin yi kokari sosai diyar nan, ta yadda kika yi aiki ba tare da ko alamar fahimtar wani abu ba game da ke. Kin cancanci lambar yabo. Allah Ya ci gaba da dafa miki, Ya kare ku a duk inda kuke."

Kaina sunkuye nake amsawa da amin.
Na juya na sara wa su Oga Sagir, kafin muka fice waje aka sanya ta cikin mota tare da sauran ma'aikatanmu da ke jan motar da gadinta.

Sauran gidajen wadanda Oga Sagir ya zayyane wa maigari muka nufa, duk babu wani bata lokaci aka kama su. Mutum daya ne dai ba mu samu a gida ba, ashe wai ya ji labarin abin da ke faruwa shi ne ya gaggauta guduwa. Matarsa da ta ji muna neman hadawa da ita sai ta tona masa asirin ya yi shigar mata ne ya tafi, idan an gaggauta za a same shi a hanya.
Mun kuwa same shi din har ya tsayar da babur zai hau, aka shako shi sannan Oga Usman ya cire masa hijabin jikinsa, daga nan muka karasa kofar gidan maigari.

Mutane da yawa kofar gidan maigarin, mata da maza; manya da yara sai alhinin wannan abu ake. Babu wanda ake zato a cikin duk wadanda aka kama, saboda a fuska mutanen kwarai ake musu kallo, sai dai hakan ba shi ba ne halayen da ke lullube da zukatansu.

Shiga cikin gidan na yi na dauko akwati da jakar goyona na fito, na je har inda Amarya take na yi mata godiya sosai, na jinjina wa karamcinta da na yaranta, sannan na koma wurin motarmu, daga nan kawai muka wuce.

Oga Sagir ya kira waya, bayan ya gama ya ce a yanzu haka ana can daji ana fafatawa, ba a dai cafke kowa ba tunda ba su gano ainahin wurin zaman kidnappers din ba, sai dai suna jin harbe-harbe daga nesa, su ma kuma suna yin nasu harbin.
Babu hadin guiwar police ko army, mu ne kadai muke kidinmu muke kuma rawarmu, muna fatan dacewa a cikin kankanin lokaci. Da ma kuma tafe suke da map, shi suke bi domin ya isar da su ainahin mazaunar kidnappers din.

Mun kuwa dace din, don babu mutum daya da aka kashe daga cikin ma'aikatanmu, sai dai harbi, an samu har mutum biyu amma an ci sa'a babu wanda bullet ya zauna a jikinsa. An samu nasarar kama kaf kidnappers din da suke cikin dajin, sannan an kubutar da mutum sama da ashirin da suka sace.
Babu wata tazara a tsakanin isarmu da isarsu.
Aka kulle informers wurinsu daban, sannan kidnappers ma wurinsu daban.
Sauran victims din kuwa, aka sallame su, Oga Ahmad ya sanya a kai su tasha, tare da kudaden mota ga kowannensu. Ni da Aysha rungume juna muka yi sadda muka hadu. Daga nan aka wuce asibiti da ita domin auna lafiyarta saboda zazzabi da take ta fama da shi.

A lokacin da na shiga office din Oga Ahmad waya yake yi, na ci gaba da tsayuwa har sai da ya gama ya ba ni izinin motsawa, ya ce in zauna a kan kujera.
Tun kafin in ce komai ya riga ni,
"Weldone, Weldone UmmulKhairi. Kin yi aiki mai kyau wanda kika cancanci babbar kyauta."
Ya saki murmushi.
"Sai dai duk kin yi baki, kin rame. Duk zaman kauyen ne, ko kuwa rasuwar saurayinki ne har yanzu a ranki?"
Na sunkuyar da kaina ban ce komai ba. Ya ci gaba da fadin
"Hakika wannan aikin namu ba iya na maza kawai ba ne kamar yadda mutane ke daukan bai dace ga mata ba. Tunda idan da aikin maza ne kawai ta yaya za ki shiga jikin Shamsu har ki samu muhimman bayanan da muka samu? Ga Azumi ita ma, da namiji ne watakila da corper's lodge za su sauke shi, da ba za mu samu komai dangane da ita ba.
Kina da kwazo sosai, ina son aiki da mutum mai kwazo irinki. Don haka na jinjina miki, and you deserve to be awarded."
"Thank you Sir."
Na furta a hankali ina jin dadin kalaman nashi.
"Your award will be ready in few days in shaa Allah. Za a yi taron karrama ki idan mun gama da wadancan mugayen mun tura su court."
Na sake yi masa godiya. Ya ce
"Ki samu ki je gida ki huta sosai. Ki ga Umma don na san kina cike da kewarta ko?"
Na yi murmushin jin dadi.



Amrah A Mashi❤️

Continue Reading

You'll Also Like

45.1K 2.2K 51
"Don ubanki wanki dana barmiki kimin shine kika kiyimin Kika zauna kika rungume wannan shegiyar d'iyar taki wallahi koki aje ta ko kuma yanzu jikin k...
16.8K 882 32
DR UMAIMAH USMAN BULAMA,Mace yar kimanin shekara ishirin da tara , Babbar surgeon A asibitin CITY TEACHING HOSPITAL , Aure Uku, ƴaƴanta uku . Mace m...
13.8K 1K 47
Rayuwa wani abu ne da kan zo mana da kalubale iri iri, wani muna iya fin karfinshi da taimakon Allah wani ko sede mu zubawa sarautar Allah idanu zuwa...
2.3M 70.4K 98
Previously called Older Brothers Part 1 Completed (Alternate version) part 2 Ongoing "T-trust me?" "Always." It was the promise that they were never...