DARE DUBU

Por PrincessAmrah

11.5K 1.5K 68

Kaddara! Mece ce ita? Yaya rayuwar yarinya mai karancin shekaru za ta kasance a lokacin da ta tsinci kanta ci... Mais

PROLOGUE
Page 01- Khairi
Page 02- Damuwa
Page 03- Fargaba
Page 04- Mafarin Komai
Page 05- Masauki
Page 06- From God We Are...
Page 07- Tushiya...
Page 08- Zalunci
Page 09- Dream
Page 10- Fushin Masoyi...
Page 11- Kewa
Page 12- Samu da Rashi
Page 13- Mafita
Page 14- Assignment
Page 15- Kudin Fansa
Page 17- Headmaster
Page 18- Tarko
Page 19- Kura Da Fatar Akuya
Page 20- Plan
Page 21- Suspect
Page 22- A Week To Go
Page 23- Informers
Page 24- Bankwana
Page 25- Kiran Sirri
Page 26- Arrest
Page 27- Dare Dubu
Page 28- Next Assignment
Page 29- Soyayya
Page 30- Visiting
Page 31- Alkalamin Kaddara
Page 32- Nusaiba
Page 33- Baby Boy
Page 34- Matar Haidar
Page 35- Award Morning
Page 36- I Love You
Page 37- Kambun Baka
Page 38- Kai Amarya
Page 39- Kukan Zuci
Page 40- Reconciliation
Page 41- Karshen Munafuki...
Page 42- Ruwan Zuma
Page 43- Class Rep.
Page 44- Happy Birthday
Page 45- WTTW
Page 46- Barrista Khairi
Page 47- Rama Sharri da Alheri
Page 48- Kauyawa
Page 49- Court
Page 50- Luck
Page 51- Babbar Kotu
Page 52- Medical Report
Page 53- Doctor Marzuq
Page 54- Shaidar Zur
Page 55- Confess 1
Page 56- Confess 2
Page 57- Wata Sabuwa...
Page 58- Women Leader
Page 59- Bakar Manufa
Page 60- Komai Ya Yi Farko...

Page 16- Daren Farko

182 32 2
Por PrincessAmrah

Page 16

Sai da aka dauki sati hudu cif muna hannun 'yan garkuwa da mutane amma shiru ba wani labari. Da alama har a lokacin cinikinmu ake yi tamkar wasu kaji ko raguna.
Kayan abincinmu tuni sun kare amma sai cewa Zaki ya yi wai mun yi saurin cinyewa, don haka ba za a ba mu wani abincin ba sai dai garin kwaki da gishiri.
Ko mai babu ballantana kuli-kulin cinsa. Kuma a hakan dole shi muke ci tunda ba mu da wata mafita ko zabin abin da za mu cin.

Rayuwa ta yi mana zafi, komai ya kife mana, mun zube, mun lalace. A lokacin da al'ada ta zo mana kuwa, lokacin ne muka dandani wani abu wai shi rashin galihu; don ko audugar mata babu wadda za mu tsaftace jikinmu. Kallabin kayana shi muka dinga yaga muna amfani da shi har sai da muka gama. Sannan da wando guda daya tal, tun wanda aka sace mu da shi a jikinmu. Sai dai idan mutum ya cire ya wanke da jikarsa ya mayar a jiki. Tun muna kyankyami har muka daina, muka rungumi rayuwar a yadda ta zo mana.

A cikin wannan halin ne ciwo ya zo min, wani irin zazzabi da ciwon kai, wannan ciwon kan da nake yi a wadansu lokutan wanda ba ya sauka, har asibiti aka taba kai ni amma ba a gano sanadinsa ba.
Na sha matukar wahala, saboda babu kula, daidai da paracetamol kwaya daya ba a taba kawo min ba, kuma Lanty ta zo ta gan ni a cikin ciwon na kuma tabbatar da ta fada musu.
Wahala sosai Ummu ta sha da ni, don har abinci a baki ta koma ba ni, wanka ita take kama ni ta kai ni har bakin toilet din, ta zuba min ruwa a bokiti bayan ta wanke toilet din tas, sannan ta ce in shiga in yi. Kuma tana nan tsaye tana jira na har sai na gama ta kama ni ta mayar har dakinmu da muka kara yawa zuwa mu shida, ta shafa min mai sannan ta ba ni kayana in mayar.

Tsananin wahala sai da ta kai ta kawo har hannuna wahalar dagawa yake yi min, zazzabi ya ci ni ya cinye duk na zube na lalace. Fuskata kuwa sai manyan idanuwa da katon kai ne kawai ke da auki a ciki.
An saki budurwar nan da karamar yarinyar da na ji an ce miliyan biyar aka biya kudin fansarta saboda iyayenta masu kudi ne.

Ranar da Lanty ta zo ta kawo mana kayan abinci, cikin tsawa ta ce
"Ke kuma gara ma ki gayyato wa kanki kuzari da karfin hali tun wuri, don idan Oga ya gane kina neman zame wa mutane liability sunanki sorry. Wallahi kashe ki za a yi kowa ma ya huta."

Jin hakan ba karamin tsorata mu ya yi ba. Tun daga nan sai kuwa na gayyaci karfin halin, na dinga tafiya da kaina duk da ina yi ina zama in huta ko daga dakinmu zuwa bandaki. Sannan na rage kwanciya. Wata mata ta ba ni shawarar in yawaita shan ruwa saboda shi ruwa waraka ce ta dukkan komai, musamman tun da safe kafin in ci komai. Cikin ikon Allah kuwa sai sauki ya zo, a hankali na fara warkewa har sai da na gama warkewar tas.

Ranar da muka cika wata biyu cif a hannunsu aka sake kiran mu a kan Oga na son ganin mu. Kyakkyawan mari ya dauke Ummu da shi, yana kokarin dawo da shi fuskata Ummu ta yi saurin zubewa kasa. Cikin kuka ta ce
"Na roke ka don Allah kar ka mare ta, ka juye duk sauran marukan a fuskata, Khairi na da matsalar ciwon kai, ban san me zai iya faruwa ba idan ka dauke ta da wannan zazzafan marin naka mai dauke ji da ganin mutum na wucin-gadi."

Sosai na ga karfin halin Ummu, ta yadda har ta iya samun kwarin guiwar yi wa Ogan kidnappers irin wannan maganar.
Bai fasa marin nawa ba, sai da ya dauke ni da shi guda biyu, sannan ya yi wa Ummu guda hudu bayan wancan na farkon.

Tashin hankali wanda ba a sa masa rana, ji na yi tamkar duniyar ce duka ke juyewa saboda azabar da ta shige ni, na fashe da wani irin narkakken kuka, irin wanda ke tasowa tun daga cikin zuciya yana ketowa ta tsakanin idanuwa. Haka Ummu ma, duk azabar da take ji, hakan bai hana ta rike hannuna ba tam, a tunaninta hakan zai rage min radadin marin da ya shige ni.

"Yawwa, haka nake son ji. Watakila idan matsiyatan iyayen naku suka ji yadda sautin kukanku ke fita za su yi hobbasa su kawo mana kudin garkuwarku. Haba! Na gaji haka nan. An kusa zuwa gabar da zan yanke hukunci a kanku."
Yana fadin haka yana latsa kira, bugu biyu kuwa aka daga.
Muryar Baba ce, da sallama a bakinsa don bai gane lambar ba da alama, har sai da Ogan ya yi magana sannan ya gane.
"Ina fatan ita ma waccan komadaddiyar matar tana ji na! Don ba zan sake wahalar kiran ka ba ita ma in kira ta. Tunda dai duk tafiyar guda ce, idan ma ba ta kusa sai ka isar da sakon gare ta."
Ya fada hade da kara wayar tsakanin fuskokinmu, kuka muke yi dukkanmu. Ina jin sadda Baba ya kira sunayenmu, kafin ya dora da
"Ku yi hakuri kun ji, muna nan muna ta bakin kokarinmu wajen ganin mun hada kan kudaden nan, amma abun ya faskara. Kudin ne da yawa, ga shi kuma babu su wallahi sai dai godiyar Allah. Amma da izinin Allah ko rabin abin da aka bukata na mutum daya ne za mu hada mu kawo ko za su ji kanmu su sake ku. Kuna ji na?"
Ya tambaya, jin babu wacce ta yi magana a cikinmu.

Ummu ce ta yi karfin halin cewa
"Baba a taimaka a fitar da mu, wallahi babu dadi a nan din, ga Khairi ba ta da wadatacciyar lafiya, ciwon kan nan nata yana damun ta. Babu abincin kirki Baba, babu sutura, babu bacci mai dadi, komai babu dadi. Ga kewarku, Baba don Allah duk yadda za a yi ku hada kan kudaden nan, na san ba abu ba ne mai sauki, tunda babu."

Fizge wayar Oga ya yi da karfi, sannan ya ce
"Ina fatan ka ji abin da nake son ka ji din. Don haka kuna da wa'adin sati daya, idan har ya cika babu kudin nan, zan fada muku inda za ku dauki gawarsu."
Daga haka ya yanke wayar hade da tattaune layin kamar yadda ya saba.

Na runtse ido ina jin tausayin rayuwarmu da ta iyayenmu, wannan wace irin rayuwa ce? Wane irin zamani muke ciki wanda ake farautar rayuwar mutum tamkar ta dabbobin daji? Sai yaushe ne dan Nigeria zai zama mai 'yancin kansa kamar yadda ake fadin kowa yana da freedom a kasar? Sunan dai Nigeria ta samu 'yancin kanta ne a 1960, amma wannan 'yancin babu shi. Idan kuwa har tana da shi, to lallai 'ya'yan cikinta ba su da shi.
Shin ina shugabanninmu na siyasa suke?
Ina Sarakuna?
Ina manyan Malamai?
Ina sojoji da 'yan sanda?
Ina Mopol da sauran jami'an tsaro?
Duk mene ne amfaninsu idan har za a dinga cinikin fansar mutum a cikin kasarsa?

Da wannan tunane-tunanen aka kore mu zuwa dakunanmu. Zuciyata cike da tunanin ta inda Umma za ta iya samun wadannan kudaden da ba na jin ko a mafarki ta taba mallakarsu. Har gara ma Ummu tunda babanta yana raye, sannan suna da dangi masu yi musu. Ni kuwa fa? Umma ita ce karfin komai namu, sai kuwa taimako da ga Baban Ummu. To kuma an zo gabar da kowa tasa ta fisshe sa ne, don ba zai yi wahalar Neman kudin fansar Ummu ba ya yi tawa.

Kuka sosai na yi a wannan daren, duk kokarin Ummu na ganin na yi shiru amma na kasa, ita gudunta kar ciwon kaina ya taso don ba abu ne mai sauki ba idan ya tasar min har da zazzabi yake hadewa.
Abin da na fahimta shi ne, ita ba ta ma tausayin kanta kamar yadda take tausayina.
Shin waye ya taba ganin zallar soyayya irin wannan?

***
Na sharce hawayena bayana na gama da tunane-tunanen duniya.
To ni kuwa me zai tsorata ni da ba zan iya tsayuwa wajen ganin asirin azzaluman ya tonu ba?
Na shirya, ko da a ce zan rasa numfashina ne in dai a wajen tonuwar asirinsu ne zan yi, kamar yadda na daukar wa kasata alkawari.

Kamar da wasa har karfe ukun dare ta yi bacci bai dauke ni ba, a hankali na dinga jiyo motsi daga waje, na kasa kunnuwana da kyau ina son sanin ta inda motsin nan yake amma na kasa ganewa. Da rashin tsoro irin nawa sai na tashi zaune, na hau takawa a hankali har na isa bakin 'yar kankanuwar tagar da ke cikin dakin, na janye labulen gararar da ke jiki na dan leka, sai na ga wata mata ce ke bin bango cikin sanda za ta fita waje, na darara ido da kyau amma ban gane ko wace ce ba, tunda zuwana duk na ga matan gidan har ma da yara sai da amarya ta yi min bayaninsu.
Kallabin da ke kanta ta sanya ya sauko har saman fuskarta ta yadda ba za a iya gane wace ce ba. Cikin sandan har ta karasa zauren gidan, daga nan kuma ban kara sanin abin da ya faru ba. Na duba wayata, karfe uku da kusan rabi. Mamaki bai bar ni ba na ci gaba da jiran tsammanin dawowar ta amma shiru, sai da ta dauki kusan minti ashirin sannan na yanke wa kaina shawara.
Na lalubi kuguna na daidaita zaman 'yar karamar bindigata wadda ake kira da pocket pistol, sannan cellular phone dita ma ta aiki tana jikina. Kawai sai na samu kwarin guiwar fita, domin ina jin a jikina lokacin fara aikina ya yi, watakila a daren nan zan fara aiwatar da abin da ya kawo ni kauyen.

A hankali nake takawa don kar in tashi amarya da yaranta, na isa bakin kofa har na kusa yin tuntube da fo din da ta ajiye domin fitsari idan sun ji, don an ce a garin ba a fita ko fitsarin dare gudun kar a sace ka tunda bandakunansu a filin tsakar gida suke wasu ma can bayan gida.
A hankali na bude kofar, na janyo ta na rufe ta yadda ba za ta tashe su ba.
Kamar yadda waccan matar ta dinga bin bango ni ma hakan na yi, ban kuma tinkari zaure ba kai tsaye sai na labe daf da kofar.
Kasa-kasa na dinga jiyo muryoyi, duk maza ne sai na mace daya, kuma babbar mace da alama don yanayin m sautin muryar ya bayyana hakan. Na zura kaina ta kofar ko zan iya jiyo wani abu amma shiru ban iya jin komai din ba.
Kusan minti goma ina tsaye, sai can na jiyo suna sallama, kafin kuma na ji ta ce

"Na manta in fada muku, muna da sabon kamu a garin nan, a nan gidan ma. 'Yar bautar kasa ce ta zo."




Amrah A Mashi❤️

Continuar a ler

Também vai Gostar

19.4K 1.7K 100
labarin wani matashi daya auri wata yarinya na wucin gadi saboda wani dalilin sa.
12.3K 606 53
MAKAUNIYAR RAYUWA- KASHI NA UKU- BABI ASHIRIN### Fatan alkhairi gareku masoyana a duk inda kuke,alherin Allah ya kai gareku, ubangijin Allah ya biyaw...
155K 10K 40
WANNAN LABARI NE DA WASU BANGARE YA FARU A GASKE. BAN CANJA SHEKARUN YARINYAR BA KO ALAKA BA,AMMA NA CANJA SUNA, SANNAN BABU SUNAN GARI DA KUMA ANGU...
191K 15.4K 42
story is starting with a business tycoon Vansh raisinghania and a middle class girl Riddhima. Vansh hates women because of his past and he wants a su...