DARE DUBU

By PrincessAmrah

11.5K 1.5K 68

Kaddara! Mece ce ita? Yaya rayuwar yarinya mai karancin shekaru za ta kasance a lokacin da ta tsinci kanta ci... More

PROLOGUE
Page 01- Khairi
Page 02- Damuwa
Page 03- Fargaba
Page 04- Mafarin Komai
Page 05- Masauki
Page 06- From God We Are...
Page 08- Zalunci
Page 09- Dream
Page 10- Fushin Masoyi...
Page 11- Kewa
Page 12- Samu da Rashi
Page 13- Mafita
Page 14- Assignment
Page 15- Kudin Fansa
Page 16- Daren Farko
Page 17- Headmaster
Page 18- Tarko
Page 19- Kura Da Fatar Akuya
Page 20- Plan
Page 21- Suspect
Page 22- A Week To Go
Page 23- Informers
Page 24- Bankwana
Page 25- Kiran Sirri
Page 26- Arrest
Page 27- Dare Dubu
Page 28- Next Assignment
Page 29- Soyayya
Page 30- Visiting
Page 31- Alkalamin Kaddara
Page 32- Nusaiba
Page 33- Baby Boy
Page 34- Matar Haidar
Page 35- Award Morning
Page 36- I Love You
Page 37- Kambun Baka
Page 38- Kai Amarya
Page 39- Kukan Zuci
Page 40- Reconciliation
Page 41- Karshen Munafuki...
Page 42- Ruwan Zuma
Page 43- Class Rep.
Page 44- Happy Birthday
Page 45- WTTW
Page 46- Barrista Khairi
Page 47- Rama Sharri da Alheri
Page 48- Kauyawa
Page 49- Court
Page 50- Luck
Page 51- Babbar Kotu
Page 52- Medical Report
Page 53- Doctor Marzuq
Page 54- Shaidar Zur
Page 55- Confess 1
Page 56- Confess 2
Page 57- Wata Sabuwa...
Page 58- Women Leader
Page 59- Bakar Manufa
Page 60- Komai Ya Yi Farko...

Page 07- Tushiya...

228 27 6
By PrincessAmrah

Page 07

Barka da zagayowar ranar Hausa ta duniya (26th/8/2023)

***

Cikin dauriya na ce
"Na gode Baba, Allah Ya kara girma."
Kuka sosai nake yi, tuna da a ce Ummu na nan da yanzu ta harare ni jin ina yi wa iyayenta godiya, abin da ta ki jini kenan, wai kamar ban dauke su nawa iyayen ba.

"Ya isa haka, ki daina kuka Khairi."
Mama ta furta cikin nata raunin.

"Babu ranar da zan daina kukan rashin Ummu, rashinta wani irin babban gibi ne a rayuwata, irin wanda babu abin da zai iya cike shi. Ban san dalili ba, amma ji nake tamkar ba ni da sauran amfani a duni..."
"Ki daina fadan haka mana Khairi kar ki yi sabo."
Mama ta yi saurin kwaba ta. Na yi shiru kawai amma ina jaddada wa kaina hakan ne, babu ko tantama rayuwar nishadi ta yi kaura a duniyata.

Na mike cikin sanyin jiki na yi musu sallama. Baba ya kara jaddada min a kan in kawo abubuwan da ya ce din daga na koma gida, ko kuma idan su Sadiya sun dawo daga makaranta in ba su su kawo na amsa da to sannan na tafi, zuciyata na kara ingizo hawayen da na gagara dakatar da shi.

Bayan sati daya aka bukaci in je domin a dauki thumb print dina. Ko da na je makarantarmu malamai da yawa tambaya ta suke ina UmmulKhairi lukuta, kamar yadda ake kiran mu ni siririya ita kuma lukuta. Wasu sun ji labarin rasuwarta suka yi min gaisuwa amma wasu ba su sani ba su ne dai masu tambayar ina Hassanar tawa tunda ba su saba gani na babu ita ba. Ko larurin ciwo ba ya sanya a ga daya ba a ga daya ba sai dai idan kar a gan mu mu duka.
Ta rasu kawai nake fada musu ba tare da wani dogon bayani ba. Wadanda suka san da zancen garkuwan da aka yi da mu suka hau jajanta min, suna karawa da tambayar ko dai a can ne aka kashe Ummu ko kuma wani ciwon ta yi?
Ni dai babu mai samun amsa daga gare ni sai hawayena kawai da nake sharewa.

Da muka gama duka ofishin rijistar JAMB muka je tare da Baba. A can aka yi mini komai na cike, sai dai wani al'amarin Allah, a maimakon in cike medicine din da ya kasance mafarkinmu, sai na kasa. Na juya na kalli Baba da shi ma din ni yake kallo. Sannan na kalli mai cikewar na ce
"Don Allah idan ina son zama jami'ar tsaro me ya kamata in cike?"

Murmushi mutumin ya yi, ya ce
"Jami'ar tsaro kuma kina mace? Wannan aikin ai bai cancance ki ba gaskiya. Ki bar wa maza dai su ya fi dacewa da su. Idan har kika ga mace jami'ar tsaro to sai dai yare ba Bahaushiya ba."

Ko kadan kalaman nashi ba shiga ta suke ba. Fahimtar hakan ya sanya shi cewa
"Me zai hana ki cike mass com? Ma'ana aikin 'yar jarida. Kusan duk inda jami'in tsaro zai je to shi ma dan jaridar zai je har ma ya zarce. Sannan babu ruwansa da mace ko namiji kowa zai iya yin sa. Ni dai ina mai ba ki shawara da ki karance shi, zai dace da ke sosai."

Ko kadan ba wai burge ni yake yi ba, ina nan kan baka ta ba gudu ba ja da baya. Sai dai kafin in ba shi amsa, Baba ya ce
"Abin da ya fada gaskiya ne UmmulKhairi. Ke diya mace ce kuma Hausa-Fulani. Aikin jami'an tsaro ko kadan bai dace da ke ba. Na san dalilin da ya sa kike son ki yi shi, saboda daukan fansar abin da aka yi wa 'yar'uwarki. Ki jingine wannan tunanin don ba lallai burinki ya cika ba. Ki cike likitanci abin da kuka jima kuna mafarki ke da 'yar'uwarki Ummu."

Kuka nake sosai ina gyada kai,
"Ba zan iya ba Baba, ba zan iya zama likita ba alhali babu Ummu. Da burin zama likitoci muka girma, da shi muka yi wayo tun kafin mu san kanmu, kafin ma mu san mene ne likitancin. Don haka ba zan iya zama likita ba a lokacin da babu Ummu a duniyar."

Baba ya sauke ajiyar zuciya ya ce
"Shi kenan to ki daina kukan. Bawan Allah ka cike mata mass com din sai ta karance shi."

Ba zan iya sake yi wa Baba musu ba, don haka na sanya ido kawai aka cike min shi din, ina jin a raina ina nan kan bakana ba zan fasa zama jami'ar tsaro ba, ko ba don fansar abin da aka yi mana ba, ko don dakile yawaitar 'yan ta'adda.

Bayan mun gama komai muka dawo gida, sai da Baba ya ga na shiga gida sannan ya tafi.
Ina shiga na shaida wa Umma komai, cikin farinciki ta ce
"Wadannan mutane karamcinsu har ya yi yawa. Ni ban ma san ta inda zan fara yi musu godiya ba. Wallahi mutanen kirki ne."

Ni dai shiru kawai na yi a raina ina cewa daga gare su ne Ummu ta gaji halayen kwarai.

***
Ban jima da dawowa ba sai ga Anti Maryam ta zo sanye da fararen kaya, da alama daga wajen aikinta take. Da annuri a fuskarta ta shigo tana sallama. Na amsa sannan na shimfida mata tabarma ina gaishe ta.

"Ah lallai jiki ya yi kyau UmmulKhairi. Ji yadda kika fara murmurewa kamar ba ke ba."
Murmushi kawai na yi wanda iyakacinsa bisa lebena.

"Ina Umma ko ba ta nan?"
"Ga ni nan Maryama. Barka da zuwa."
"Yawwa Umma. Ya kwana biyu? Kun ji ni shiru wallahi ayyuka ne sun yi yawa. Ya mai jiki?"

Ta tambaya tana mayar da kallon ta gare ni. Ita ma Umma kallon nawa ta yi ta ce
"Jiki da sauki Sista. Kin gan ta nan yanzu haka daga makaranta take. Babansu ya yi mata rijistar komai lokaci kawai ake jira yanzu."

Cikin fadada annuri Anti Maryam ta ce
"Madalla madalla! Kai alhamdulillah! Wallahi na ji dadin wannan labari Umma. Ashe 'yar kanwata ta kusa cika burinta."
"Ga ta nan ki yi mata fada Sista. Wai ta fasa zama likitar. Yanzu haka fadan da na gama yi mata kenan ta tashi ta cike wai aikin jarida. Ba ma wannan ba, shi kansa jaridar wai ba shi take so ba, so take ta zama jami'ar tsaro."

Zaro ido Anti Maryam ta yi tana sake bi na da kallo.
"Wannan wane irin tunani ne kika yi Khairi? Shin da wa ma kika yi wannan shawarar?"
Na sunkuyar da kaina ina rasa amsar ba ta.

"Me ya sa ba ki kira kin ji daga gare ni ba? Ba har lambar wayata na ajiye a cikin wayar Umma na ce ki dinga nema na ba idan bukatar hakan ta taso? Wallahi ba ki kyauta min ba ni dai Khairi. Me mass com zai yi miki ke da nake son ki zama kwararriyar barrister?"

Na san abin da take so in yi kenan tunda ko kwanaki ta fada min, sai dai ko kadan ni ba ni da wannan burin.
Shi barrister sai jami'an tsaro sun kamo sun kai kotu sannan ne zai yi nashi aikin.
To idan kuma jami'an tsaron ba su kama ba fa?
Ni fa burina kenan, kuma ba na jin akwai wanda zai sauya mini shi.
Na dai yi shiru ina jin su ita da Umma sai aikin fada suke amma ba dauka nake yi ba.

"To ni dai yanzu ba zan fasa abin da na yi niyya ba, maganar scholarship din nan da na fara yi muku, yanzu haka abin da ya biyo da ni nan kenan daga asibiti. Jiya Abban su Rukayya ke ce min a yi kokari a ga dai ta samu O level mai kyau, shi da kansa zai tsaya ganin an samu scholarship din zuwa Sudan ko Egypt ta hanyar mai kudin nan Alhaji Kabiru Kaita. Don bana kam ana kyautata zaton zai tsaya sosai wajen bayar da admission din tunda siyasa ta kusa, kuma yana so ya ci."
Ta dube ni ta ce
"Law din nan dai shi za ki nema da yardar Allah kuma za a dace. Babu abin da ya dace da ke face shi."

Umma ta saki murmushi ta ce
"Na ji dadin wannan bayani Maryama. Da ma ni dai wallahi sam ba na son wannan aikin jaridar. Allah Ya sa a dace."
"To amin Umma. Sai mu kara dagewa da addu'a, da yardar Allah nasara na nan tare da mu."
"To Allah Ya amince."
Umma ta furta tana mikewa ganin Anti Maryam din ma ta mike.

"Ni zan wuce Khairi. Allah Ya kara sauki."

Kasa-kasa na amsa da amin, domin ni dai ina nan kan bakana, zan kuma ci gaba da binciken yadda za a yi in samu aikin jami'ar tsaro ko da karami ne, har sai lokacin da na dace.

***
Bayan fitar Anti Maryam na koma daki na kwanta kawai na hau tariyar rayuwar duniya, silar kawancenmu da Ummu, kawancen da ya rikide ya zama 'yan'uwantaka...

TUNA BAYA

Ranar da aka haifi Sadiya, a lokacin Abbanmu yana raye, na hada kai da guiwa kurum saboda Umma ta ce sai na je islamiyya, ni kuwa irin abun nan na an haihu a gidanmu, sai cewa na yi babu inda za ni ai kuwa Umma ta hau duka na ta ce dole sai na je.
Cikin rarrashi Abbana ya kira sunana, na dago kan nawa sai gani na yi yana yi min murmushi.

"Maza tashi mu je in raka ki islamiyya tun kafin Ummanki ta kara miki wani dukan. In ban da abin ki Khairi, wa ya fada miki ana fashin makaranta babu dalili? Ko kina so malaminku ya zane ki?"

Na gyada kai.
"To idan dai ba kya son duka da dorina tashi mu tafi yau da kaina ma zan raka ki, sannan har da kudin shan alewa ma ga su nan."

Na kuwa saki murmushi har da tsalle na bi bayansa muka kama hanyar makaranta.
Ta gaban gidan su Ummu muka gitta, a lokacin sabon gida ne wanda ko kammala shi ba a yi ba don ko shafen simintin waje ma ba a yi ba.

Sai ga Baba ya fito hannunsa rike da Ummu, ganin za mu gitta ta gaban gidan ya sanya shi mika wa Abbana hannu suka gaisa.

"Barka da dawowa unguwarmu Mallam. Na ji labarin dawowar taku ai mako daya da ya wuce."
Abba ya furta da fara'a yana duban Baba.

"Eh wallahi. Ni kuma kullum uzuri. Ina ta son yin sallama ga makwabta a gaisa dai har yanzu Allah bai nufa ba."
"To ai da ma komai sai Allah Ya bayar da iko ake yi."

Baba ya dube ni da busasshen hawayena ya ce
"Yanmata ya aka yi ake kuka?"
"Makaranta ce wai ba za ta ba tunda Ummanta ta haihu yau. Shi ne ta sha duka. Ni kuma na ce yau da kaina ma zan raka ta."

Baba ya dafa kaina yana murmushi ya ce
"Ma shaa Allah! Watakila ma makaranta guda ce za mu je. Ni ma waccan islamiyar ta can kasa zan kai ta. Tun jiya na je na mata komai shi ne aka ce yau ta fara zuwa."
"Ka ga faduwa ta zo daidai da zama kenan. Bismillah sai mu tafi ai ko? Khairi, kama hannunta mu je."

Jin Abba ya kira ni da Khairi ya sa Baba tambayar sa sunana ya fada masa.
"Wannan fa shi ne babban katari. Ka ga ita ma wannan sunanta kenan UmmulKhairi. Amma ita Ummu ake kiran ta."

Hirar su suke ta sha yayin da ni da Ummu muka rike hannun juna ina ba ta labarin jaririyar da aka haifa mana fara kyakkyawa.

Wannan ranar ita ce mafarin komai, ita ce silar kawancenmu, ita ce silar amincin da ya kulla tsakanin iyayenmu, wanda kuma mu ne silar bunkasuwarsa.


Amrah A Mashi❤️

Continue Reading

You'll Also Like

807K 69.4K 59
Zanen ƙaddaransa yana cikin zuciyarta, kamar yanda zanen nata ƙaddan ke cikin tasa zuciyar. Idan zuciyoyi suka haɗe waje guda akan samu wata irin zaz...
155K 10K 40
WANNAN LABARI NE DA WASU BANGARE YA FARU A GASKE. BAN CANJA SHEKARUN YARINYAR BA KO ALAKA BA,AMMA NA CANJA SUNA, SANNAN BABU SUNAN GARI DA KUMA ANGU...
12.3K 606 53
MAKAUNIYAR RAYUWA- KASHI NA UKU- BABI ASHIRIN### Fatan alkhairi gareku masoyana a duk inda kuke,alherin Allah ya kai gareku, ubangijin Allah ya biyaw...
45.1K 2.2K 51
"Don ubanki wanki dana barmiki kimin shine kika kiyimin Kika zauna kika rungume wannan shegiyar d'iyar taki wallahi koki aje ta ko kuma yanzu jikin k...