DARE DUBU

By PrincessAmrah

11.5K 1.5K 68

Kaddara! Mece ce ita? Yaya rayuwar yarinya mai karancin shekaru za ta kasance a lokacin da ta tsinci kanta ci... More

PROLOGUE
Page 01- Khairi
Page 02- Damuwa
Page 03- Fargaba
Page 04- Mafarin Komai
Page 05- Masauki
Page 07- Tushiya...
Page 08- Zalunci
Page 09- Dream
Page 10- Fushin Masoyi...
Page 11- Kewa
Page 12- Samu da Rashi
Page 13- Mafita
Page 14- Assignment
Page 15- Kudin Fansa
Page 16- Daren Farko
Page 17- Headmaster
Page 18- Tarko
Page 19- Kura Da Fatar Akuya
Page 20- Plan
Page 21- Suspect
Page 22- A Week To Go
Page 23- Informers
Page 24- Bankwana
Page 25- Kiran Sirri
Page 26- Arrest
Page 27- Dare Dubu
Page 28- Next Assignment
Page 29- Soyayya
Page 30- Visiting
Page 31- Alkalamin Kaddara
Page 32- Nusaiba
Page 33- Baby Boy
Page 34- Matar Haidar
Page 35- Award Morning
Page 36- I Love You
Page 37- Kambun Baka
Page 38- Kai Amarya
Page 39- Kukan Zuci
Page 40- Reconciliation
Page 41- Karshen Munafuki...
Page 42- Ruwan Zuma
Page 43- Class Rep.
Page 44- Happy Birthday
Page 45- WTTW
Page 46- Barrista Khairi
Page 47- Rama Sharri da Alheri
Page 48- Kauyawa
Page 49- Court
Page 50- Luck
Page 51- Babbar Kotu
Page 52- Medical Report
Page 53- Doctor Marzuq
Page 54- Shaidar Zur
Page 55- Confess 1
Page 56- Confess 2
Page 57- Wata Sabuwa...
Page 58- Women Leader
Page 59- Bakar Manufa
Page 60- Komai Ya Yi Farko...

Page 06- From God We Are...

223 29 3
By PrincessAmrah

Page 06

Hannuna rike da na Ummu bayan na dauki sabulun wanka guda muka nufi inda aka mana kwatance da bandaki. Shiga na fara yi sai dai da hanzari na fito saboda kazantar da na tarar a ciki. Haka Allah Ya halicce ni da kyankyami musamman na bandaki. Ummu na gani na ta gane dalili, shiga ta yi ta sheka ruwa ta dan gyara shi sama-sama sannan ta yi nata wankan ta fito.
"Shiga ki yi na gyara."
Tunda muka zo sai a sannan ne ta yi magana. Sai na ji wani sanyi a raina, na karbi sabulun na shiga na watsa sannan na fito na tarar Ummu na tsaye tana jira na.
"Kin dauko sabulun?"
Ta tambaye ni. Ni na ma manta, ta shiga ta dauko sannan ta zo muka wuce bayan mun yi alwalla.

Daya daga cikin man shafawar da aka ba mu na bude, muka shafa sannan sai sallah. Bayan gama sallar ma sai da na zauna a wurin na fada wa Allah tare da neman agajinSa AzzawaJalla. Na kai kuka sosai kafin na kishingida a wurin ina tunanin rayuwa.
Ko yaya danginmu suka kare?
Wace irin rayuwa suke cikin bayan batan mu?
Yaya makomar Mama da ba ta da wasu yaran bayan Ummu?
Na tabbata sai hawan jinin Ummana ya tashi, karamin abu ma yana tayar da shi ballantana kuma batan dan mutum, mutum din ma kuma budurwa.
Sai a sannan wasu irin zafafan hawaye suka hau ambaliya a saman kumatuna, kuka nake sosai, irin wanda ke fitowa tun daga cikin zuciyata, jikina sai karkarwa yake yi, ga wani irin zafi da zuciyata ke yi.

A hankali Ummu ta tako ta iso inda nake, bakin hijabinta ta yi amfani da shi ta hau share mini hawayena,
"Ki daina kuka Khairi..."
Kawai ta samu daman fadi ita ma nata hawayen suka fara kwaranya.
Wani irin yanayi ne dukkanmu muka shiga, irin yanayin da duk yadda zan kwatanta shi babu wanda zai taba fahimta face wanda ya shiga kwatankwacinsa.
A rana guda ka wayi gari a hannun 'yan garkuwa da mutane, ban san yadda zan ba da labarin yanayin ba.

Rarrashi na Ummu ke yi sai dai ita ma kukan take yi. Tare muka dinga kukan har sai da muka gaji don kanmu sannan muka daina.

***
Wani irin zafi gami da radadi nake jin zuciyata tana yi a lokacin da na dawo daga duniyar tunanin da na lula. Shin da gaske karshen farincikina ya zo? Wani sashen na zuciyata ya ba ni tabbacin da gaske ne, matukar dai Ummu ta tafin, to ba ni da sauran farinciki ko jin dadi a rayuwata.
Kuka nake son na yi ko zan samu sassauci, sai dai zuciyata ta ki ta ba kwayar idanuwana hadin kai, ko kadan hawayen ya gagara fitowa sai zafin nan da zuciyata ke yi tamkar danyen raunin da aka watsa wa yajin tsidahu.

"Da gaske UmmulKhairi ta rasu, gawarta aka tsinta a bayan gari."
Muryar Anti Maryam ta yi mini shigar suruf a na'urar shige da ficen sautina.
"Ta rasu Khairi, sai dai mu bi ta da addu'a."
Ta nanata min a lokacin da take kokarin hada idanuwa da ni.

"To kin ji UmmulKhairi, takwararki Allah Ya yi mata rasuwa. Na san dole za ki damu, amma dole za ki jure, dukkan mai rai mamaci ne, dukkanmu nan sai mun dandani mutuwa."
Dakta Gumel ya fada cikin sigar rarrashi.
Da fari tsoron sa nake, tsoron duk wani namiji ma. Sai dai a yanzu da yake jaddada mini mutuwar Ummu, wani irin haushi da takaicinsa ne nake ji.

"Ki yi kuka Khairi, kukanki zai taimaki aikinmu ya tafi yadda ya kamata. Rashin fitar hawayenki ba karamin dakile ci gaban da muke son samu zai yi ba."
Jin sa kawai nake yi, amma ban san ta inda hawayen da ke soya zuciyata za su fito ba. Don kuwa idanuwana kamas suke tamkar an soya gyada a cikinsu.

Ya kalli Anti Maryam ya ce
"Ku tafi gida, a kwantar mata da hankali ta dawo cikin nutsuwar ta, sannan ku dawo bayan sati biyu. In shaa Allahu komai zai wuce tamkar ba a yi ba."

A nufinsa, komai din na nufin har mutuwar Ummu? Ban taba tunanin akwai wata mummunar kaddarar da za ta shafe keta haddin da aka yi mini ba, sai dai jin zancen mutuwar Ummu, yadda ya jijjiga komai na halittata, a take na ji batun fyade ya kau, burin da na ci game da wannan aika-aikar da aka yi mini duk ya shafe. A yanzu ba ni da wani burin da ya wuce kwatar wa Ummu fansa, durkusar da wadanda suka kashe ta, da izinin Allah sai na kai su kasa, komai daren dadewa.

"Tashi mu je Khairi. Sai hakuri kin ji."
Tamkar tana magana da dutse, na dai ji ta, amma kwata-kwata hankalina bai kai ga abin da take nufi ba.
Sai da ta kama ni ta mikar sannan ma na gane ashe nufinta in tashi mu tafi.

"Allah Ya kara sauki UmmulKhairi. Please try your best ki yi kuka. Barin kashi a ciki ba ya maganin yunwa."
Dakta Gumel ya fada cike da tausayi. Ban amsa masa ba muka bar office din, zuciyata na karyata batun mutuwar Ummu. In bancin kar in yi sabo da sai in ce ban shirya rabuwa da ita ba, bai kamata a ce ta tafi ta bar ni ba tare da dukkan burikanmu sun cika ba.

A kan hanya Anti Maryam ta yi ta kokarin kwantar mini da hankali amma ko uffan na kasa ce mata. Ta dai ci sa'a ina daga mata kai amma na gagara furta kalma guda ma.
Har muka isa gida ban ce komai ba, sai da muka shiga gida ta hau labarta wa Umma duk abin da ya faru, a lokacin ne kuma na rushe da kakkarfan kuka bayan na fada jikin Ummata.
"Umma...ashe Ummu ta rasu, ta tafi...ta bar ni..."
Na so in kara da wani abun amma kuka ya ci karfina, tunanin rayuwa da komai nake, tunanin yadda zan ci gaba da rayuwa ba tare da Ummu ba.

A hankali take dan bubbuga bayana,
"Sai hakuri Khairi, Ummu ta tafi inda ba a dawowa, inda da ni da ke duk sai mun tafi. Ki sanya wa zuciyarki salama, da sannu zai sanyaya miki komai AzzawaJalla. Ki yi addu'a, ki fada maSa komai, Shi ne mai maganin kowacce irin damuwa kuma zai magance miki. Duk wannan kukan ba zai amfana miki komai ba face wata cutar da zai janyo miki. Kina ganin ba lafiyar kirki kike da ita ba, ba na so ana tufka kina warwara."

Suka hadu ita da Anti Maryam suna ta ba ni maganganu amma ina! Na yi nisan da ba na jin kira. A yanzu dai babu wata magana da za ta kwantar mini hankali a kan mutuwar Ummu. Shakuwa da soyayyar da ke tsakaninmu ta fi karfin in manta da ita a dan lokaci kankani.

***
Kamar da wasa sai da na cinye wata biyar cif a cikin larurin depression, depression ciwo ne irin wanda damuwa ke haddada shi, sannan shi ba shi da kwayar magani ko allura. Mun yi zarya wajen Dakta Gumel fiye da sau bakwai amma babu wata nasara sai dai sauki daga wurin Allah. Tun abun ba ya tsorata su Umma sosai har ya fara.
Idan na zauna ni kadai ma magana nake yi ina ambatar sunan Ummu, ina tuna wadansu moments na rayuwarmu.
Rayuwa ta yi mini juyin waina a kasko, ko kuma dai juyewar gawayi zuwa danyar wuta.
Duk wanda ya san ni a baya idan ya dube ni a yanzu ya san an samu sauyi, irin mummunan sauyin nan wanda ba a so.
Ga wata irin rama da na yi jikina duk kashi, ni da ma ba wata kiba ce da ni ba, balle kuma a yanzu da komai ya karasa lalace min.

***
Zumbur na tashi zaune ina share kwallar da ta zame min tamkar ibada kullum sai ta zubo min ba dare ba rana. Zaman hijabin jikina na gyara, sannan cikin rashin kwarin guiwa na mike.
A tsakar gida na samu Umma tana wanki su Safra na makaranta.
Ta dago kanta ta dube ni ta ce
"Khairi sai ina?"
Na kara sharce kwallar da ke sake zubowa,
"Gidan su Ummu zan leka."

Ajiye rigar da take wankewa ta yi ta zo inda nake, ta dafe kafafa ta ce
"Idan kin san zuwa gidansu zai kara tayar da hankalinki ki yi hakuri kar ki je Khairi, kin ga muna dan murna jikin naki ya fara kyau kuma kar ki je angulu ta koma gidanta na tsamiya. Ba na fatan ki sake shiga irin wancan mummunan yanayin, duk da a yanzu din ma ba gama warkewa kika yi ba."

Na kirkiro murmushin da bai da alaka da nishadi na ce
"Tun da Ummu ta rasu ban leka gidansu ba, amana ba ta ce haka ba Umma. Ba na so Mama ta zaci don rashin Ummu ne ya sa ba na shiga gidan."

"Maman Ummu ta san larurin da yake addabarki tunda har ganin ki tana shigowa yi, ko jiyan nan dai ta zo. Ba za ta yi wani zaton na daban ba."
"Duk da haka dai Umma ina son zuwa in gaishe ta da kaina."

Ta saki ajiyar zuciya ta ce
"Shi kenan. In dai hakan zai faranta miki rai babu komai ki je. Ki ce ina gaishe ta."

"Za ta ji Umma."
Na furta cikin sassanyar murya, sannan na kama hanya na tafi gidansu. Ba wata tafiya mai nisa ba ce, duka-duka ba zai wuce gidaje uku ba ne a tsakaninmu, nan da nan na isa.
Na samu Baba zaune kan tabarma, Mama na dama masa fura.
Da annuri suka tarbe ni ni ma na kirkiri nawa annurin duk da bai kai ciki ba.

Har kasa na tsugunna na gaishe su kamar yadda na saba, Mama ta ce in je in dauko kujera in zauna amma Baba ya ce sai dai in zauna a kan tabarmarsa. Babu musu na zauna.
"Yaya karfin jikin naki? Jiya na leka Ummanku ke fada min bacci kike ai."
"Eh Mama, ta fada min. Jiki ya yi sauki."
"To alhamdulillahi ai haka ake so. Sai ke ma ki kara kokarin fitar da komai daga ranki kin ji? Allah shi ke bayarwa kuma Shi Yake kwacewa a duk sadda Ya so. Addu'a za mu yi Allah Ya toni asirin azzaluman, ita kuma UmmulKhairi Allah Ya haskaka makwancinta Ya kara mana hakurin rashinta."

Sai kawai na ji hawaye na bin kumatuna. Har yanzu na kasa sabawa da rashin Ummu, da zarar an min zancen mutuwarta sai na ji komai tamkar sabo. Na dukar da kaina kasa ina shawarar hawayen.

"Idan kin koma gida ki dauko mini kananan hotunanki, sannan ki rubuta sunanki a bayan kowanne hoto. In shaa Allahu gobe zan je in biya miki kudin jarabawa kamar yadda na yi alkawari. Da NECO ce da JAMB kadai, amma tunda babu Ummu, sai in yi amfani da kudin natan a biya miki duka biyun, WAEC da NECO din kenan."

'Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!' Na hau maimaitawa a cikin zuciyata. Wannan maganar ta Baba ji na yi tamkar ya zuba mini narkakkiyar dalma a cikin kunne.

"Ki daina kuka diyata. Ko da ma can duk daya na dauke ku ke da ita, ballantana kuma a yanzu da babu ita. Ina rokon Allah Ya cika miki burikanki kamar yadda kuka fara ke da 'yar'uwarki..."
Shi kansa Baban cikin rauni yake maganar wanda har ya dakata ba tare da ya kai inda yake son tsayawa ba.


Amrah A Mashi❤️

Continue Reading

You'll Also Like

12.3K 568 13
Love, romance, destiny, paid
132K 8.6K 55
Kallon kitse ba litaffina bane na marubuciyar nan ne Halima Abdullahi k/mashi
234K 9.8K 25
"မောင် မဆိုးစမ်းနဲ့ကွယ်" "ကျုပ်ကိုမချုပ်ခြယ်နဲ့"
13.9K 1K 47
Rayuwa wani abu ne da kan zo mana da kalubale iri iri, wani muna iya fin karfinshi da taimakon Allah wani ko sede mu zubawa sarautar Allah idanu zuwa...