NISFU DEENIY.......!

By deejasmah15

1.2K 117 25

She was exactly opposite of what he wants in a wife,,,he vowed not to be with her but fate has its own way as... More

CHAPTER ONE (REJECTION)
CHAPTER TWO (IF ONLY I CAN LET GO)
CHAPTER 3 ( MY PRAYING POINT)
CHAPTER 4 ( HOW I WISH....)
CHAPTER FIVE (MEETING.. ).
CHAPTER 6 ( MISFORTUNE....!)
CHAPTER 7
CHAPTER 8 ( HIS VISIT)
CHAPTER 9 ( THE RIDE)
CHAPTER 10 ( SHE'S BACK)
CHAPTER 11 ( SHE'S BACK II)
CHAPTER 12 ( DAYS TO GO.....)
CHAPTER 13 ( #BECOMINGMRSBAY)
CHAPTER 14 ( DAY ONE)
CHAPTER 15 ( HONEYMOON)
CHAPTER 16 ( A_RIDE_TO_YERWA)
CHAPTER 17 ( LIVING WITH HIM)
CHAPTER 18 ( HER EFFECT)
CHAPTER 19 ( SICK)
CHAPTER 20 ( SHE'S TO SOFT)
CHAPTER 21 ( GETTING TO KNOW HIM)
CHAPTER 22 ( NO, I DON'T)
CHAPTER 23 ( DAY AFTER )
CHAPTER 24 ( GETTING ALONG OR GETTING APART?)
CHAPTER 25 ( SETTING THE GROUNDS)
CHAPTER 26 ( SACRED TRIP)
CHAPTER 27 (THE PERFECT HER)
CHAPTER 28 ( PROUDLY HIS❀)
CHAPTER 29 ( MILESTONE)
CHAPTER 30 ( HURRICANES)
CHAPTER 31 ( MEETING II)
NISFU DEENIY 32 (BROKEN)
CHAPTER 33 ( BROKEN 11)
CHAPTER 34 (DAY-OFF)

PROLOGUE ( TEASER)

116 7 0
By deejasmah15

NISFU DEENIY.......!

KHADEEJAH BINT ISMAIL ( DEEJASMAH )

ELEGANT ONLINE WRITERS (E.O.W)

Ga sabon labari ga maabota bibiyar littafaina, wainda suke bibiye dani tun daga WASU DANGIN, WANI RABON toh an fa riga ya an samu rabon har ta yi masa lak'abi da cikon rayuwarta kuma Rabin Addininta....Nisfu Deeniy labarine akan wata zuria mai girma da tushe wacce ta ke gab da rasa zumuncin da aka dad'e ana yi sakamakon kuskuren y'ay'ansu sai dai kuma hakan bai faru ba saboda tubalin da aka gina zuriyar tafi k'arfin turewa. Amma still sai da suka fuskanci k'alubale sakamakon laifin d'an su ga 'yar lelen su.....

Me labarin ya k'unsa?!
Kuna son sani?

Toh ku kwantar da hankalinku don nesa ta zo kusa domin ko in rabbi ya ara mana numfashi nan da bayan sallah zamu sanya d'amba a tafiya zuwa Yerwa domin binciko wannan sirri.

Tuna da sunan NISFU DEENIY......!!!❤

Dedication

This whole book is dedicated to all Kanuris out there....been one of you is the most beautiful gift ever. I love the fact that I'm blessed to be one of you and I'll proudly shout it to the whole world.......Kanuri to the world.

This whole work is with love Ayusha Adam ( Ayshacool) soyayyarki gareni ta daban ce Allah ya k'ara girma da arziki ❤

Forward
In the name of Allah the most beneficent the merciful may the peace and blessing of Allah be with his most beloved messenger prophet Muhammad SAW his family and his companions and his saints and those that follows his path until the eternal road end.

Allah ka bamu ikon ganin dai dai mu bita ka kuma rabauta mu da ganin akasin hakan mu guje mata. Allah kasa mu sak'a Alkhairi ka rabemu da sharri a koina, a kowani hali.

Allahumma inna nas'alukar ridhaka, wa ridha nabiyuka, wa ridhal ashyaku wa ridhal walidin....

Allahuma j'al ma nuhibbu fima tuhibbu wa tarda....Allahuma j'al fi ikhtiyarina ikktiyari ka wala taj'al illa ilaika id'd'irarina.

Ya rabbana ya khaliqul awalim...kul bainana wa kulli zaleem.

Wajzi li kulli man ilaina ahsan wa jazihi anna zaahal ahsan...bil mustafal shafi'i yaumil mahshari khairil waraa man qad hubi bil Khausari...
Wal jam'a liy fil husnaa....wal katma liy fil husnaa.❤
Wala haula wala quwatti illa billah.

Author's note :

All the characters places ideas and events mentioned in this book are purely fiction and does not relate to any living or dead
All the story setting and other elements are nothing but imaginations and fictional any resemblance to any person's life is coincidence.

©deejasmah 2023❤🌹

PROLOGUE

Gyara zama yayi yana nazartar kalamanta a hankali. Sake tambayarta yayi " lele, kin amince in miki zab'i?,". Kai ta gyad'a kafin cikin voice d'in ta mai taushi tace.

"Na'am Baba na amince da kowa apart from him ". Hararta Abbu yayi yana mai jin tamkar ya tokare ta ta wuntsula. Wai shin ita ce aka tab'awa laifi da ba zata iya yafewa ba?, ina hak'urin da kowa ya shaide ta da shi?. K'wata yayi a hankali ya na mai sauraron Yayan nasu.

Murmushin girma yayi kafin yace " ki kwantar da hankalin ki lele, zan miki zab'in da zakiyi alfahari da shi". A take gabanta ya yanke ya fad'i sai dai kuma ta na k'arfafan kanta da ta daure, ta nuna masa muhimmancinta da martabar ta. Tafi gaban wacce ya keta a baya, ko zata samu tagomashin motsa kambunta a kan sa. Kwatsam ta jiyo muryan Baban ya na cewa.

" Na zab'a miki Farhan a matsayin mijin da zaki aura and I'm very sure ba zaki k'i zab'in da nayi miki ba....." D'ifff duka parlorn ya d'auke tamkar anyi ruwa an d'auke. D'agowa tayi tana mai jin girman furucin na shi.

Ji tayi zafi ya na keto mata Daddy Senator ne yace " Yaya Tijjani Farhan kuma...?". Cikin isa ya d'aga masa hannu alamun yayi shiru hakan yasa ya had'iye kalmomin shi. " Farhan is not a bad choice right?!". Baban ya tambaya ya na kallon ta.

Ji tayi harshen ta yayi mata nauyi, kalmomin kuma sun tsere tamfar bebiya. Matsowa yayi ya kama k'afar Baban cikeda zubda makaman ikon shi yace " Baba kayi hak'uri, kar ka aura mata Farhan don Allah ".

Ture shi yayi yana cewa " I've made my choice, ruwanka ka amince ko akasin hakan. As long as shi ya amince, I know ma ba zai k'i ba". A take kukan Zulfaa ya cika d'akin hakan yasa hankalin kowa ya koma kanta.

Abie yace " Ke wata kalan sakarya ce, zaki sawa mutane ihu haka?". Amsawa tayi da cewa " Haba Abie, ya zaai a had'a Abban Suhail da Bloody?!, Bloody ta fa!!".Cikeda hargowa yace " Haramun ne hakan?" bata iya magana ba sai sake k'ara sautin kukan ta da tayi.  Abbu ne ya amsa da " haba yaya, ai ta mayi k'ok'ari don Allah Yaya Tijjani kar ai wannan had'in".

A take Abba yace " Ba wanda ya isa ya hana wannan had'in ". Nan fa ta mik'e tana cewa " Na shiga uku na, Wayyo Allahna!!". A take Abie ya mik'e yaja hannunta har zuwa k'ofa bud'ewa yayi ya tura ta. Tareda rufewa ya dawo wurin shi ya na zama.

Sake matsawa yayi gaban Abbu yana cewa " Abbu ka sa baki please,,,,this will do more harm than good!!, Don't marry off Jewel to Farhan please". A take Abba yace " sake masa k'afa, sakaran yaro kawai ko ba Jewel ba in banda ma baka da kunya har Yusuf zaka kalla kace masa yasa baki?!, sake mai k'afa nace ".

Sake mai k'afa yayi ya matso gabanta " Jewel ki yafe ni,,, I promise you I'll change, in ma baki so na yanzu naji na amince amma please don't marry Farhan wallahi zan iya mutuwa if you do so!". Kawar da fuska tayi ta na mai jin kamar ta janye kalmominta amma shaidan sai bijiro mata da komai yake yi tamkar yanzu komai yake faruwa.

Cikeda cushewar voice tace " ba ka isa ba!!, Ba zan tab'a bijirewa iyayena saboda kai ba......" A take Farhan da tun d'azu yake zaune kamar mutum-mutumi ya katse ta da cewa " Ashe ko zaki mutu babu aure in dai har ni zaki aura Wallahi.......Guy har abada bazan iya aurenta ba ko da kuwa baka da rai ne balle da rayuwar ka,,tashi daga gabanta in sunga dama su jik'a ta su sha itama in ta ga dama ta auri all the guys in the family.....mtswww kai kake lallab'ata ma......."

''Farhan!!" Mom d'in shi ta furta sai dai bai ko kalleta ba yace " Baba kayi hak'uri, but with due respect I can't marry her a samu wani wanda ke ra'ayi!!" Daga haka ya ja hannun Islam d'in suka fita.

Murmushi Abbu yayi ya na kallonta. Ita ko ji take tamkar k'asa ta tsage ta shige take ji. Yau ita Lelen Yerwa ne ake gwanjonta kamar wata tsohuwar langa?!, wannan wani irin cin mutunci ne. Ba kowa bane ya ja mata sai Islam da banzar zuciyarta da ta sanya har ta sallama kanta gareshi a shekarun baya. Wanda har da k'uruciya a ciki, yanzu kam ba da bane.

Abbu yace " sai ki tashi kema ki b'ace mana da gani shashan banza kawai!". A tsorace ta tashi ta nufi k'ofa ko waiwaye babu. D'akin Hajja ta nufa tana kuka tamkar ance Yasen ya rasu.
Yau ne take jin maraicin rasuwar Hajja ta dawo mata sabuwa fil, ta tabbatar inda Hajja tana nan ba wanda ya isa yai wa lelenta dole.

A can hall d'in kuwa bayan fitan ta Baba Tijjani yace " a yau zan aurar da ita ga wanda nake raayi, na lura cewa kanta ya na kulle da komai wanda ba laifinta bane but laifin shi wanda ni da ku mun san da hakan..but ina son muyi hak'uri ba ya a tsarina yi mata auren dole amma bamu da yanda zamuyi....." Nisawa yayi kafin ya d'aura El-Sadeeq yace " But Baba da hak'ura akayi da maganar auren har zuwa sanda zata sauko da kanta".

Murmushi Baban yayi Abba kuma yace " Tabbas haka maganar ka take Ba'anah, Yaya please a dakatar da auren nan". Kallon su yayi da kyau ya san ba zasu tab'a yarda da abunda zai cutawa lele ba shima kuma hakan ne.

But ya tabbatar za suyi alfahari da zab'in da zai mata. And he's sure that ba zasu taba kaicon zab'in shi ba. Ko da ko bai da rayuwa ne, a take yace " kayyah!, a gaban kowa ta bani zab'i kuma ni zan tabbatar da aurenta a yau d'innan ko don in cika alk'awarin da nayi ga Hajja,,,,,,,,,Ku matan nan ku shiga cikin gida kai kuma Hafeez aje a fiddo kayan d'aurin aure".

A take mata da yara suka fice daga hall d'in. Maza kawai aka bari a ciki inda aka fara shigo da kayan d'aurin aure na al'adar kanuri. Ganin sun gama shigo da komai ne ya sa Baba Tijjani bud'e 'yar jakar hannun shi. A take sisin zinari ya bayyana, duban Abba Adam yayi yace " Ka zama waliyin ango ni ne waliyin Lele ku zaku zama shedu zaa d'aura auren ta a yau in muna numfashi......."

Daga haka yayi shiru, shirun da ya haifar da damuwa da kuma firgici a zuciyoyin mazan da ke wurin. Musamman da ya kasance Abba Adam ne zai d'aura auren. Zaheer a take jikin shi ya fara rawa tunanin shi ko da shi za a d'aura auren, kasancewar tunda Bahaja ta rasu bai sake aure ba. Shiko Safwan kamar ya ruga yake ji don akwai jik'ak'ka tsakanin su da Baba Tijjani akan aure.  Suma haka sauran mazan da suke parlorn kowa yana tsoron ace da shi ne!!.....

A cikin gida kuwa Suliem ce ta shiga wurin ta. Tana zama tace " Lovie ki kwantar da hankalin ki, Baba ya tabbatar da ba zaki auri Yaa Islam ba,,,,and he mean it ". A hankali tace " Mom Aleenah to da wa zai d'aura min auren,,,,,,innalillahi me zai sa ba zaa barni da shi mu sasanta ba". Hannun suliem dake bin ta da kallon you are sick tayi tace " In suka aura min wani ba shi ba mutuwa zan yi wallahi ".

Cewa tayi " me yasa baki sanar da hakan a idanun kowa ba, meyasa kika zab'i zaluntar kan ki akan abunda kike so,,,shin ya zaki bari shaidan yai miki gangi har ki rasa yin tunanin makomar ki,,,,,,shin kina tunanin cewa akwai inda zakije da zai fi nan inda yake ne?".

Hawayen da take faman yi ne ya sake zubar mata a rikice tace " Ya zanyi Mom Aleenah?" Kafin ta bata amsa message ya shigo wayarta " Babe me yasa kika zab'i cutar mana da zukata a dai-dai lokacin nan?!, shin yaushe kika zama mara tausayi har haka?!, me yasa ba zaki iya yafe min laifukan da na aikata a bisa rashin sani ba?, well gashi kin ja mana one word could have change everything but kin zab'i wahal da zukatan mu,,,,,  yanzu kuma bakin alk'alami ya bushe ni dake mun rabu da juna rabuwa ta har abada............"

Kuka ta saka tana cewa " Na shiga uku,,,,barin je wurin Baba Tijjani...." a dai dai lokacin ne Mommy Hafsah ta shigo d'akin da bag da kuma kud'i tace " ga shi nan an d'aura aurenki,,,,,ruwanki kiyi biyayya da hakan ruwanki ki bijire sai dai ina miki bushara da cewa duk abunda kika gani toh da kanki zaki koka ba wani ba......" Daga haka ta juya ta fice ba tare da lura da halin da ta shiga ba.

Suliem ce ta sanya ihu tana cewa " Leleeeee!!" Sakamakon kifawar da tayi babu ko alamun rai tare da ita. Hakan ne ya jawo hankalin mutanen da ke parlorn kusa da su har suka shigo ciki. Sai dai duk wanda ya ganta sai firgicin halin da suka shiga ya kama su, a take drs dake wurin suka fara bata kulawar da ta dace da ita har akai nasarar samo numfashin ta da k'yar............

Nisfu Deeniy!!!.....littafine da ya ginu akan soyayya, rikitacciyar soyayya mai cikeda chakwakiyar zumunci... Kar ku yadda ayi babu ku.

Continue Reading

You'll Also Like

425K 26.5K 19
Β© 2018 All Rights Reserved Yusrah's life takes a dramatic turn when her parents decide to get her married to Masoud Abdullah. That wasn't the life Yu...
1.3M 114K 42
✫ 𝐁𝐨𝐨𝐀 𝐎𝐧𝐞 𝐈𝐧 π‘πšπ­π‘π¨π«πž π†πžπ§'𝐬 π‹π¨π―πž π’πšπ πš π’πžπ«π’πžπ¬ ⁎⁎⁎⁎⁎⁎⁎⁎⁎⁎⁎ She is shy He is outspoken She is clumsy He is graceful...
377K 5K 32
Rajveer is not in love with Prachi and wants to take revenge from her . He knows she is a virgin and is very peculiar that nobody touches her. Prachi...
2.4M 141K 46
"You all must have heard that a ray of light is definitely visible in the darkness which takes us towards light. But what if instead of light the dev...