WUTA A MASAƘA

By Ayshercool7724

27.6K 1.6K 154

labari akan wata yarinya me rawar kai da rashin jin magana sam, labari akan taɓarɓarewar zumunci, tarbiyya da... More

WUTA A MASAƘA
WUTA A MASAƘA 2
3
WUTA A MASAƘA 4
CHAPTER 5_6
7_8
9_10
11_12
WUTA A MASAƘA 13_14
WITA A MASAƘA 15_16
WUTA A MASAƘA 17_18
WUTA A MASAƘA 19_20
WUTA A MASAƘA 21_22
WUTA A MASAƘA 23-24
WUTA A MASAƘA 23_24
WUTA A MASAƘA 27_28
WUTA A MASAƘA 29_30
WUTA A MASAƘA 31_32
33_34
35_36
37_38
37_38
39_40
41_42
43_44
47_48
47_48
49_50
51-52
53_54

45_46

994 60 10
By Ayshercool7724

🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥

WUTA A MASAƘA

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)

The experience writer of

*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA)
*BAƘIN TABO (Labarin gasa)
*AƘIDATA (Paid Book)
* WUTA A MASAƘA

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in

❌❌❌
Ƙirƙirarren labari ne, ban yadda ayi amfani da kowane sashi na labarin ba ba tare da izinina ba.







45_46

Amira ta cigaba da cewa "tun daga lokacin da na fara iya hawa kan stage, a gaban dubun dubatar jama'a inyi rawa, kunya ta ƙauracewa idona, mussaman da Ni nake ɗaukar ɗawainiyar kaina, ni nake wa kaina komai, dan haka na dinga ganin nafi ƙarfin kowa, ba wanda ze taka ni in saurara masa.

Sultan ya dinga goyon bayana, yana tafiya dani guraren raye raye, sedai ya kan cemin 'Amira ba'a son raina nake zuwa dake gurin rawa ba, ina fatan Ubangiji Allah ya baki miji me sonki, wanda ze riƙeki da amana"

Ya yadda yaje dani ko ina, in dai fannin rawa ne ba zan ba shi kunya ba, sedai be yadda wani yaci mutuncina ba, Mutane na zaton mutuniyar banza ce ni, sedai duk wanda ya raɓeni da maganar banza, sena masa ƙaramin hauka, dan tabbas har da ƙaramar wuƙa nake yawo saboda tsaro.

Idan aka ɓatamin rai a gidan, gidan Anty Fa'iza nake tafiya, saboda tun tasowa ta ban san wani abu wai shi rarrashi ko ja a jiki ba, amma ba dangin iya ba na Baba, mijinta Bashir yake mutuntani, yake girmamani kamar ƙanwarsa.

Shiyasa nake tafiya gidan inyi kwanaki, tunda aka gane ina zuwa raye raye, Yadikko ta laƙaba min kalmar Karuwanci, ni kuma na karɓa na hau kai na zauna, na nuna mata na amince itan ce, saboda ba abunda zanyi wanda zesa ta janye abunda take faɗa a kaina.

Wannan shine dalilin da yasa nake rashin ji, nima ba son raina bane rashin gata ne, mata da yawa suna lalacewa ne saboda rashin gata, wata da ta rasa breziar da zata saka gara ta bada jikinta ta sam kuɗi, amma ni bana aikata zina ni ba karuwa bace.

Tai maganar tana rushewa da wani irin kula me Ratsa zuciya.

Imran yai ajiyar zuciya, ya rungumeta tana dukan bayanta a hankali da sigar rarrashi yace "Am so sorry Amira, tabbas an miki ba daidai ba, an cutar dake sosai mussaman da munanan kalamai, daga gareni amma dan Allah ina neman afuwarki Amira, dan Allah kiyi haƙuri ki yafemin"

Ba ta iya cewa Komai ba , se cigaba da kukan ta da tayi, ya rungume ta yana shafa bayanta.

Tun daga ranar Imran ya shiga matsananciyar Nadama, yake nan nan da Amira, duk a ƙoƙarin sa na wanke laifinsa, dan tabbas yasan abunda mahaifiyarsa ma tayi ba ta kyauta ba, na nunawa Amira tsana tun tana ƙarama, ba zata taɓa mantawa da abunda tai mata ba, da wanda take mata a yanzu ba.

Amira ta nuna kamar ba abun ɓaci rai da Imran ya taɓa yi mata, hakan ba ƙaramin ƙara mata kima yai a idon sa ba, duk da wasu lokutan idan taso tsiya, rashin mutunci take masa, amma baya duba hakan dan shi be zaci ma za ta iya saurarsa ba haka da wuri, saboda yadda ya dinga mata a baya.

Tana kula dashi sosai, ba ƙorafi da yawan kawo matsala, sedai in kishin ya motsa ko Ihsan ta kira ta yayyaɓa masa Magana son ranta.

Basu ƙara raba gurin kwana ba, daren da yake idan ya fita ya dena, kullum yana manne da Amira (maza manya, ya manta da kashedin Ammi 😂😂😂)

Ranar Saturday yana baccin safe, Amira ta tashi duk tayi aikinta, tai wanka tai kwalliya, ta zo ta zauna kusa da shi, ya ɗora hannunsa a ƙirjinsa yana bacci, ta ɗora nata hannun akan nasa, hannunta ya sha jan rani, ta ɗau wayarsa ta ɗauki hotunan hannunsu a haka, ta ajiye masa wayarsa.

"Amran ka tashi ka karya mana" tai Maganar tana shafa gefen fuskarsa.

Ya buɗe ido a hankali ya kalle ta, yai murmushi yace "You look so cute"

Wani irin fari tai masa sannan ta kashe masa ido tace "dama dan ka yaba nai kwalliyar, tun da ka yaba kwalliya ta biya kuɗin sabulu"

Murmushi yai ya shafa gashinta yace "Amira Amma wannan gashin ki ne ko?"

Ta jinjija masa kai alamar eh.

"Ka tashi muje ka karya, bana son ulcer ta kama min kai fa"

"Duk yadda kike kula dani ɗin nan, ina ulcer zata ganni, kiss me se in tashi"

Tashi tai daga jikinsa tace "naƙi wayon"

Wayarsa ce ta fara ringing, Amira ta ɗakko za ta bashi, amma taga my wife a kai, ai kuwa ta haɗe rai tai rejecting ɗin kiran.

"Amira ya haka?"

"Nifa gaskiya na fara gajiya da halin matar nan, ta barni in sarara Nima, Lokacin da kuka tafi kuka barni ni kirana kake? Ya za tabi ta addabeni wallahi ba zaka ɗaga wayar nan ba"

Ta kashe wayar gaba ɗaya, Imran yai ajiyar zuciya yace "muje inci Abincin"
Yasan dai rigimace Amira ta janyo masa tashin hankali a gurin Ihsan.

Bayan Imran ya karya, har bayan azahar yana gida, se wajen la'asar sanan ya fita, bayan fitarsa ya duba wayarsa, yaga missed calls ɗin Ihsan rututu da na Ammi.

A kiɗime ya kira layin Ammi, dan yasan da ƙyar in ba ƙararsa Ihsan ta kaiwa Ammin ba.

Aikuwa yana kira ta ɗaga, "Sannu mara mutunci sallamamme"

Imran yace "Subhanallah, Ammi meyafaru?"

"Dole ka tambayeni meyafaru mana, kira nawa nai maka baka ɗauka ba? Ihsan ta kiraka kai rejecting kaƙi ɗagawa, nima na kira kaƙi amsawa saboda tsabar wulaƙanci da rashin mutunci ko? Wato kana tare da Karuwa Imran ka tsallake maganata kenan ko?"

"Yasalam, Ammi ba haka bane ba, ina tare da oganane, meeting akayi ba damar in ɗaga waya shine dalilin, amma banda haka ba abunda ze sa in ƙi ɗaga wayarki, ko in bijirewa maganarki"

"Hmm ai na zata ka fara biyewa waccan watsatsiyar ne, gaba ɗaya Ihsan ta tashi hankalinta, duk yadda za kai kayi ka dawo gida ka kula da matarka"

"Ammi ba za'a bani pass Yanzu ba"

"Be dameni ba, ka dawo gida kawai ni ban yadda da zamanka da wannan Yarinya a guri ɗaya ba, kome kake ka baro kazo ka kula da matarka"

"Shikenan Ammi, zan va yadda za'ayi, amma ko ta biyo jirgi ta taho nan ɗin?"

'ban yadda ba, ka dawo shine Umarnin da na baka"

"Shikenan, zan dawo insha Allah"

Ba ta kuma magana ba, ta katse wayar, Imran ya dafe kansa yai shiruu ya rasa abunyi gaba ɗaya, Ihsan ta fara sire masa da abubuwan da take masa sun fara ƙular dashi.

Yadda Imran ya fita ba haka ya dawo ba, hakan yasa Amira ta fuskanci Imran ɗin yana cikin damuwa, dan haka tace "Amran"

Ya kalleta yace "Nifa na kasa gane ma'anar Amran ɗin nan"

Tai murmushi tace "Amira_Imran shine Amran"

"Wow, sunan yayi kyau sosai my dear"

Ta jinjina kai tace "meke faruwa ne?"

"Wai Ihsan ba lafiya, Ammi ta matsa in koma gids, zan karɓi pass mu koma"

"Allah ya bata lafiya, wataƙila mun kusa ɗaukar baby ne"

Kallonta Imran yai, koma har zuci ta faɗi maganar ba, tayi ƙoƙari ƙwarai gurin ɓoye damuwarta.

Watan su Ɗaya da sati biyu cif a Lagos, Amira ta sha kula da taraiya, kamar yadda Imran ya samu kyakkyawar kulawa daga Amiran, gaba ɗaya sunyi ƙiba kai kace yanzu yai Aure.

Amira ma tau wani fresh kamar ba ita ba, ta ƙara kyau da nutsuwa sosai.

Abun takaici da suka isa gidan Ihsan bata nan, Amira ta wuce sashenta ta shiga gyagygyarawa.

Imran yace "Amira bari inje guda gurin Ammi"

"Shikenan, kace ina gishesu"

Bayan fitar Imran, seda ta gyara ko ina ta ɗora girki, sannan ta kira Anty a waya.

Anty ta ɗaga tare da sallama.

Amira ta amsa tace "Uwata ta kaina"

"Na'am 'yar albarka, ya kike ya Lagos?"

"Ai mun dawo Anty".

"Ahh haba yaushe kuka dawo?"

"Ɗazun nan muka dawo"

"Meyasa baki gayamin ba, ai da nasa an muku girki"

'bakomai Anty, ina Yayata, koda yake ita jiya munyi chatting da ita"..

"Tana nan ta tafi school, ina fatan dai komai lafiya ko?"

"Lafiya ƙalau Anty"

"To shikenan, dan Allah ban da rigima, ku zauna lafiya ki kula da mijinki yadda ya kamata"

"Insha Allah Anty, Nagode"

"Yawwa se anjima"

Ta ajiye wayar ta fito, fitowarta ba daɗewa sega Ihsan ta dawo, kamar waa korarriya duk tayi rama tai wani iri.

Murmushi Amira tai mata tace 'Sannu da zuwa Ihsan"

Kallon banza Ihsan ɗin tai mata taj uban tsaki ta shige.

Amira tai murmushi tace "Iska na wahalar da me kayan kara"

Imran kuwa yana zuwa gida a Falo ya tarar da Ammi, tana ganinsa annurin fuskarta ya ɗauke gaba ɗaya, ta haɗw rai ya durƙusa ya gaisheta ta amsa da ƙyar tace "ka g damar dawowa kenan?"

"A'a Ammi, pass ne ban samu da wuri ba"

"Rufemin baki da zancen wani pass, 'yar mutane ta na ta fama da rashin lafiya amma ko a jikinka, kaje kai zamankansabida kaka tare da Karuwa ko? Imran idan ka kuksakura na samu labarin wani abu a tsakanin ka da Yarinyar nan se nayi mummunan ɓata maka rai, wanda baka taɓa zata ba, bna son Yarinyar bana ƙaunarta, kuma ba zata cigaba da zama a cikin zuriyata ba balle a samu iri daga garera ba, sam bazan marba da ɗa daga Karuwa ba"

Gumi ne ya shiga tsatstafowa Imran, dan yasan aikin gama ya riga gama, inma cikinne wataƙila Amira ta samu, dan baya nacewa Ihsan ma kamar yadda yakewa Amira, kuma baya jin ze iya sake yadda ya nesanta kasan da ita, mussaman zamansu ɗin nan, da suka samu wata irin shaƙuwa da soyayya a tsakanin su.

"Ammi dan Allah kiyi haƙuri, kinga Amira idan lalacewar da tayi da halinta wani abun mun bada gudunmawa, ƙil da kin riƙeta ta samu kulawa ba lallai haka ta sameta ba"

"Karuwa tafi uwarka kenan da kake gayamin magana ko? To ban riƙe ɗinba kuma bazan riƙe ba, kaima kuma ba zaka riƙe ba, ina daf da datse wannan Auren dan ba sonshi nake ba"

Imran da ya sunkuyar da kai yai shiru, tai ta zazzaga masa masifa, seda tai ta gaji, sannan ya tashi ya tafi ransa a mummunan ɓace.

Da ya koma gida ya tarar da parr ɗin Ihsan a buɗe alamar ta dawo, bega Amira a falo ba, dan haka ya shiga paer ɗin Ihsan, ya sameta tana sallar la'asar, ya zauna ya jira ta idar, ta tashi ta naɗe sallayarta, ta ajiye.

"Ihsan baki ga na dawo bane?"

"Na gani mana me kake so in maka?"

Ya jinjina kai yace "ya jikin naki?"

"Ai da ka damu da jikina da baka kai wannan lokacin ba ka dawo ba, da ka dawo lokacin da nake jin zuciyata na daf da tarwatsewa, takaici da baƙinciki suka kwantar dani, amma har in kiraka a waya ka dinga rejecting, hakan ya tabattarmin da kaci amanata saboda waccan Karuwar, ka gaza cika alƙawarin da kaimin, in ba haka ba, ya za'ai in kiraka kai rejecting call ɗina, in maka magiya kaƙi dawowa?"

"Yanzu Ihsan irin wannan karɓar yakamata ki min? Wata guda da sati guda bama tare, ai idan ma laifin nayi miki kya bari ki min sannu da zuwa hakalina ya kwanta, seki min duk abunda zakimin ko, irin abunda yake haɗani dake kenan, ke ba kya uzuri, ba kya tunanin komai abunda zuciyarki ta raya miki shi kikeyi"

"Eh abunda zuciyata ta rayamin shi nakeyin, meyasa kamin alƙawarin da ba zaka iya cikawa ba? Ka dena sona kake na barwa karuwa kai"

"Karki kuma ce mata karuwa, bana son tahsin hankali daga dawowata"

"Na faɗa, ba karuwar bace, karuwa na faɗa na ƙara"

Idan Imran ya cigaba da tsaiwa, zuciya zata iya ingiza shi, yaiwa Ihsan lahani, dan haka ya fito daga part ɗinta, zuciyarsa na tafasa.

A falo yai karo da Amira, tana masa Magana amma idonsa ya rufe yai waje da sauri.

Hakan ya tabattar mata da Faɗa sukayi da Ihsan, Amira tace 'cigaba da wulaƙantashi, ke da gatanki da mahaifiyarki amma ni da nake marainiya ai dole in rungume shi hannu bibbiyu.

Amira ta zauna a falon, tana cin Abinci, Ihsan ta fito kamar wadda aka watso, ta kalli Amira tace "aikin banza jaka ƙazamar bariki"

Amira tace "naji nagode"

'jahila daƙiƙiya me bin maza a kwararo, wallahi se nayi maganinki zaki ga abunda zan miki, sena miki abunda ba zaki taɓa mantawa ba, idan ma wani Asirin ki kai masa idonsa ya fara rufewa ki saurari abunda zan miki"

"Alhamdilillah da kika fara ɗanɗan abunda kika min a baya, kuma wannan baƙin cikin yanzu kika fara shi, idan kin so zamu zauna lafiya, zamu Zauna lafiya ƙalau dake, amma idan akasin haka kika zaɓa na shirya, ina daidai dake wallahi, karya kawai"

"Uwar ki ce karya bani ba"

Amira tace "kin biya babarki ladan haihuwa, ita ki kaiwa wannan zagin"

Ihsan ta kawao iya wuya tace "Karuwa kawai"

"Suna ne, Karuwar Imran ba"

Ihsan taga alama kamar kalmar karuwan ta dena ɓatawa Amira rai, ra dena jin haushi sam idam ta gaya mata, taji Tamkar ta zuba ihu ko taji sauƙi a zuciyarta.

Imran se wajen ƙarfe tara na dare sannan ya koma gidan, Ihsan ta rufe ƙofar ɗakinta, ya shiga nasa ɗakin dake part ɗinta, ga wata yunwa da take damunsa, ya dawo falo ya zauna ya dafe kansa.

Amira idonta biyu dama, ta fito da wata shu'umar riga a jikinta, ta zauna kusa da Imran tace "Babyna kaci Abinci kuwa? Meya ɓata maka raine?"

Girgiza kai kawai yayi ba tare da yayi Magana ba.

"Dan Allah koma meye kayi haƙuri, in kawo maka Abinci zaka ci?"

"No bana jin yunwa"

"Haba major, kalli cikinka meka ci tyn da muka dawo? Gaskiya se kaci Abinci bari in kawo maka"

Ta tashi ta zubo Abinci ta kawo masa, da kanta ta dinga bashi a baki yana ci, daga ƙarshe kuma ta lallaɓa ta janye shi zuwa part ɗinta.

Se da Amira ta tabattar ta mantar dashi wata Ihsan, Suka kwana tare seda Asuba ya bar part ɗinta ya tafi masallaci.

Wasa2 kusan sati guda da dawowar su Amira, amma kullum se Ihsan sunyi rigima da Imran, ita kuma Amira na ta sake lallaɓa kayanta.

A haka Imran ya bawa Amira dubu ɗari uku na kayan lefe da be mata ba.

Suna kan sati na biyu da dawowa, su Yadikko suka zo gidan, da su Amina da Sadiya da Anty Fa'iza, sunyi mamakin yadda suka ga Amiran ta canzan, ta ƙara ƙiba tai shar da ita.

Ɗan uwa ɗan uwane, duk lalacewarsa Amira tai murnar ganinsu a gidnta, ta dinga farinciki ta rasa inda zata tsoma ranta dan daɗi.

Ihsan na gurin aiki, Imran ma baya nan amma yasan da zuwansu.

Yadikko tace "yanzu Amira kece a wannan danƙareren gida haka Amira?"

"Wallahi kuwa Yadikko, haka lamarin Ubangiji yake ai, ya kuke ya gida yasu Yaya Usman"

Fa'IZA tace "dui suna lafiya, yau Allah ya nufa Yadikko ta zo ɗakin Amira hankali ya kwanta"

Su Amina anata yaƙe, amma ƙasan zuciyarsu baƙin ciki ne fal, kamar su fitar da Amira daga gidan, suna can sun tsaa ruwan ido sun kasa fidda miji, saboda babu wani me ɗan abun hannu da yazo.

Nan da nan Amira ta shiga gabatar musu da Abinci, da yake tun kan suzo ta ɗora musu girki, ta gabatar musu da Abinci yaji nama, ga lemuka suka ware ciki suna zubawa, ƙasan zukatansu baƙin ciki kamar ya kashe su, sam ba haka Yadikko tai zaton tararwa ba, saboda ta zaci zata tarar da Amira a tagayyare a wahala, amma ta ganta a nutse cikin kwanciyar hankali.

Imran ne ya fara dawowa, Amira ta tsareshi tun a falo, tace "Sweet Amran, su Yadikkon sunzo"

"Ok muje ciki mu gaisa"

Suka jero zuwa falon tare, gwanin sha'awa, ganinsu tare seda Sadiya ta ƙware dan haushi.

Imran yace "Ashe mayan baƙin namu sun ƙaraso, Fa'iza ya hanya Sannu Yadikko"

Fa"iza tace "Alhamdilillah, mun sha hanya kam"

"Ya megidanki kuwa?"

"Wallahi yana nan lafiya duk yana gaisheku"

Yadikko tace "Sannu Imrna"

Yace "Yawwa ya hanya, an saki doguwar tafiya ga jikin girma"

"Ai wannan bakomai, ya haƙuri ya fama da halinta"?

Imran yace "Alhamdilillah, halinta na kirki ba"

"A'a, ai kasan abunne se a hankali dole se ana tambaya, kasan me hali wasu lokutan ba fasa halinsa yake ba, se ana bibiya ana saka ido tukuna, eh ai naga ƙoƙarin ka da na Mahaifinka da yasa ka Aureta, duk da kun san hali irin wannan se ka dinga taka tsantsan kana sa ido, mussaman da akace tafiye tafiye kakeyi, ka dinga saka nata ido sosai da sosai, kasan irin wannan ba denawa suke ta daɗin rai ba, idan yarinya ta saba yawon banza dariƙe kuɗi a hannunta...

Fa'iza a fusace tace "haba Yadikko meye hakane wai? Wannan wace irin magana ce?"

Duk da Imran yasan Amira ba karuwa bace, Amma abunda Yadikkon tai ya baƙanta mata rai, kuma dan cin fuska a gabanta.

Yadikko tace "barni in faɗa, ai da ba tai ba ba za'a faɗa ba, ba yadda ba'ayi akam ta dena harkar bin maza ba...

Tuni mutuncin tsohuwar nan ta gama zubewa a idon Imran, mussaman da Amira ta bashi labarin rayuwar da tayi a hannunta, da alama itace karuwar tsohuwa me fuska biyu.

Imran ba kunya yace "dan Allah bana son kuma jin wannan maganar, ya riga ya wuce, kuma ni na yarda da Amira ɗari bisa ɗari, saboda nasan ba karuwa bace, ni ne mijinta ni zan tabattar da haka, ana ta cemin Karuwa ce, ni ba haka na tararar ba, dan haka wannan maganar ta wuce, bana son in sake jinta, kar a kuma jifarmin mata da wannan mummunar kalmar dan Allah, in aka ci mutuncin ta mutuncina aka taɓa, nikuma ba zan lamunci cin zarafinta ba"

Hawaye ne suka shiga zubowa a idon Amira, hadda ajiyar zuciya, kawai ta rungume Imran tana kuka, Yadikko ta fusƙi da kai, cike da borin Kunya, Imran yaja Amira Zuwa bedroom ɗinta, ya janyota jikinsa yace "meyasa kuma kike kuka? So kike su rainamin ke?"

Ta girgiza masa kai "to ki dena kuka, ai Allah sheda nima kuma sheda ne, matata budurwa na samu abata, dan haka ba zan sake lamuntar a zagarmin ita ba, ko aci mutuncinta ba, saboda ina son abata"

Rungumeshi Amira tai tace "i love You too Amran"

Rarrashin ta ya dinga yi, gashi ita ba wuya ka rarrasheta, ko faɗa sukai da ya ɗan rarrsheta ya mata kalamai shikenan ya wuce a gurinta, saɓanin Ihsan me azababben taurin kan tsiya.

Fa'iza tace "gaskiya Yadikko abun da ki kayi baki kyauta ba sam, ya za ai abu ya riga ya wuce ki dinga dawo da shi baya, anyi abun nan inma karuwarce in ma ba ita bace, shi yacw yaji ya gani, meye kuma na dawo da bara bana?"

Yadikko tace"Ke rufemin baki, bana son sakarcin banza dana wofi, na faɗa ɗin ki dakeni"

Fa'iza tace "ba haka bane Yadikko, amma dai abunda ki kai be dace ba wallahi"

Se da Imran ya tabattar da hankalinta ya kwanta, sannan suka fito, ko da suka fito ɗinma, Amira tai pretending kamar ba wani abu da Yadikkon tai mata.

Ana haka se ga Ihsan ta dawo gida, ta tarara da gidan da mutane, ga su Yadikko da Fa'iza, bata manta fuskar su ba, ta gansu a gurin Dinner bikinta.

Ko kallo basu isheta ba, Fa'iza tace "laa Yadikko ga kishiyar Amira, sannu Ihsan ko?"

Kallonsu tai sheƙeƙe tace "ba dai kishiyata ba, dan wannan kucaka ce a gurina sauran titi"

Fa'iza tace "toooo ikon Allah"

Amina tace "wai da ganin wannan kishiyar Amiran a tsaye take, ita ce dai dai da ita ai"

Fa'iza ta tashi tabi Amira kitchen inda take wanke kwanukan da suka ci Abinci tace "Amira yanzu kishiyar ki ta dawo"

Jiki a sanyaye tace 'Allah yasa kar Yadikko tai wani abu da zata zubarmin da mutunci a idonta"

"Amira ba ksa zaman lafiya da ita ne? Daga na mata Magana ta faɗan baƙar Magana"
Amira tai nannauyar ajiyar zuciya tace "ina fa zaman lafiya Anty Fa'iza, kin ganta nan kullum cikin neman tashin hankali take, abun dai se godiyar Allah, ga mahaifiyar Imran ma ta sani a gaba duk na rasa abunyi"

Fa'iza ta dafa kafaɗar Amira tace "kiyi haƙuri Amira, taki jarrabawar kenan, daga wannan se wannan amma ina fatan Ubangiji Allah ya kawo miki ɗauki da gaggawa"

"Ameen Anty"

Imran kuwa jin motsin dawowar Ihsan, yasa ya shiga ɗakinta yace "Ihsan kin gaisa da 'yan uwan Amira a falo kuwa?"

"Nice zan gaisa da wannan matsiyatan? Ahalin tarkace da jaraba, Irin karuwai Allah ya kiyaye"

"Ihsan da farko na roƙeki akan kiran Amira da Karuwa da kike ki dena kinƙi, to Yanzu zan gargaɗeki na gaji da abubuwan da kike min na gaji, idan kika kuma kiranta da Karuwa ko bata ɗau mataki ba ni zan ɗauka"

Kallonsa tai da mamaki tace "me kake nufi?"

"Ina nufin karki sake kiranta da Karuwa" yana gama faɗin hakan ya juya ya fice.

Nan tai turus, ta ƙara tabattarwa da kanta Amira taiwa Imran Asirine, duk kwanan da Imran yake a ɗakin Amira ba ta taɓa sani ba, ita zaton ta kawai a ɗakinsa a yake kwana.

Ya raba musu kwana amma sam bata gane hakan ba, a nata haukan be bari ta gane hakan ba.

Su Yadikko seda suka wayi gari a gidan Amira, da safe Imran yai musu Alkhairi me yawa, Haka Amira ma sannan suka tafi rakasu tasha a motar Imran.

Ihsan kuwa dama tunda ta wucesu a falo, ba ta sake fitowa ba har suka tafi.

A hanyarsu ta dawowa Amira tai shiru kamar tana tunani, Imran yace "gimbiyar meke damunki ne?"

"Bakomai, kaina ne kemin ciwo, kwana biyun nan haka nake fama"

"Amma baki gayamin ba, ko dai damuwa ce?"

"Ba wata damuwa, kawai na rasa meke damuna ne, gashi bana iya cin Abinci"

"Amma meyasa baki gayamin ba?"

"Ai naga ba wani abun damu bane"

"A'a abun damune mana, bari muje Clinic a duba min ke"

Wani Clinic suka je, aka duba Amira aka bata magunguna, suka taho gida.

Da suka je gida har ɗaki ya kai Amira yace ta kwanta ta huta, saboda likitan da ya duba ta yace akwai buƙatar ta dinga samun isasshen bacci.

Washegari lahadi ce, Amira ta tashi gata nan ga ta nan jikinta ba daɗi, ga jiri dake damunta.

Minal ta zo gidan ita da wata ƙawarta, Ihsan suka zauna suna hira.

Amira taga kwanciyar ba zata kaita ba, dan haka ta tashi ta fito.

"Ahh Minal ke ce a gidan namu yau, ya Ammi?"

Minal ta kalli Amira tace "Ji wani munafurci, meye haɗinki dani kike wani yau nice a gidan?"

"Ohh Sorry, Allah ya baki haƙuri"

Ihsan tace "haka take, shegen shishshsigin tsiya, da munafunci ita lallai se an shiga harkarta"

"Anty Ihsan waze hulɗa da Karuwa, ba gaira babu dalili yanzu ma banda ƙaddara da Abba ya ƙaƙabo mana ita, waze so haɗa kansa da wannan tsohuwar kilakin?"

"Ke Minal me kike cewa!?

Suka ji muryar Imran da ke shigowa, jikinsa sanye da farar jallabiya.

"Meye haka kuke yi ne, baki da hankali ki ke faɗar wannan maganganun akan matata, kuma 'yar uwakki?"

"Wallahi ni ba 'yar uwata bace"

"Ni kike gayawa haka?"

"To Yaya ba karuwar bace? Ai kowa yasan haka"

Ba zato ba tsammani Imran ya kwashe Minal da mari.

"Dan ubanki ni zaki dinga gaywa wannan maganar, tashi ki bar min gida"

Ai gaba ɗaya buɗe baki sukayi dan mamaki.

Nan da nan jikinsa ya hau tsuma, dan sam baya son raini.

"Imran, Minal ce fa dan me zaka mareta dan tace mata Karuwa? Ba karuwar bace?"

Imran yace "saura kema, Na dena ɗaga miki ƙafa, ya isa abunda kukewa Amira ya isa haka? Amira ba mata ta bace kawai, jinina ce kuma ba karuwa bace na tabattar da Hakan"

Amira kuwa tuni ta fara kuka, saboda tasan abunda ze biyo bayan marin da yaiwa Minal, ba ƙaramin tashin hankali bane.

Minal kam ɗaukar jakarta tai waje tana kuka.

Sedai abun takaicin, da taje gida Ammi ba ta nan.

Ta zauna ta dinga rizgar kuka ita kaɗai a gida.

Amira kuwa zama tai tana kuka, saboda tashin hankali.

Imran yace "Amran ɗina meye kuma na kukan baki da lafiya fa"

"Ka mari Minal, kasan Ammi zata zo, zamu fuskanci fushinta"

"Amira, na gaji da cigaba da jin ana jifanki da munanan kalamai, nafi kowa sanin ke ba karuwa bace, dan haka zanyi iya yina a dena kiran ki da wannan sunan"

Girgiza kai tayi tace "Amran na riga naiwa kaina tabo"

"No zan goge tabon nan da kaina insha Allah, my wife is not prostitute"

Yai maganar yana goge mata hawaye, seda ta dena kukan sannan ya ƙyaleta.

Ihsan kuwa kamar za tayi hauka, ganin Imran ya mari Minal saboda Amira, kuma gashi itama ya fara mata kashedi.

Gaba ɗaya hankalinsa ya koma kan Amira.

Abunda ya farun ya hana Amira bacci sam, ga wani zazzaɓi da ya rufeta, gaba ɗaya ta rasa meke mata daɗi, gashi a lissafinta yau ba kwananta bane, balle Imran yazo ya ɗan lallaɓata ta samu tayia bacci.

Fitowa tayi babban falo, tai sa'a Imran yana kwance yana kallon ball, aikuwa ta ƙarasa inda yake ta zube a jikinsa.

Da sauri yace "subhanallah, Amrina lafiya kuwa, wannan zazzaɓin fa?"

Shiru tayi tana juya kanta a ƙirjinsa.

"Ko mu tafi Asibiti ne?"

"No"

"Jikinki yai zafi da yawa, ko in shafa miki ruwa?"

Ta jinina masa kai alamae eh.

Ta tashi zaune, yaje ya ɗebo ruwa a wata roba, da ƙaramin towel, yazo ya zauna a kusa da ita.

Ya zare rigar jikinta, ya shiga jiƙa towel yana shafa mata a jikinta.

Ihsan kuwa yau kasa jurewa tayi, duk da haushin Imran da take ji, ta miƙe ta tafi ɗakinsa, amma baya ciki.

Da sauri ta nufo falo, tana zuwa tai tozali da baƙin gani a falon.

Take ta zunduma uban ihu, wanda yasa Imran saurin sakin Amira suna kallon Ihsan.

"Wallahi se na kasheki, ni zaki yiwa haka? Ni zaka ciwa amana, wallahi sena ga bayan ku, nafi ƙarfin aci amanata, wallahi sena miki illa"

Tayo kan Amira gadan gadan tana ihu, Imran ya tare ta, yace "wallahi ba zaki taɓata ba, me tai miki? Tunda kin watsar dani kince ba kya sona, ai ba laifi bane dan na koma gurinta, tunda Allah yasa bake kaɗai nake Aure ba"

Ranar dai babu wanda yai rintsawar kirki, saboda bala'in Ihsan ga Amira ba lafiya, haka ta dinga masifa a daren nan maƙota naji.

Da sassafe Imran ya taya Amira ta shirya ze kaita Asibiti, sedai suna zuwa falo suka tarar da Ammi ga Ihsan da Minal.

"Sannunka ɗan banza mara mutunci, yanzu Imran ni zaa kaiwa haka, ka nunamin ban isa ba? Ka fifita karuwa akan matarka da ƙanwarka, ka mararmin Minal, Imran kana tsoron Allah kuwa? Wato kasa ƙafa kai fatali da sharaɗin da na gindaya maka ko?"

"A'a Ammi ba fatali nayi da maganarki ba, dan Allah ki tsaya ki saurareni in miki bayani"

"Bayanin ubanka zakamin, ka fara bijiremin saboda 'yar iska karuwa..

Kan Ammi ta rufe bakinta, Amira ta fara sheƙa amai a gurin 😲😲😲

Domin gyara, sharhi ko Shawara
Ayshercool
07063065680

Continue Reading

You'll Also Like

18K 810 15
Labari akan wata yarinya Hafsat wacce mahaifin su ya rasu mahaimahaifiyar sy ta sake aure in da ta auri mugun miji. shine me mimijin Ummun nnasu yaii...
3K 211 22
Tunaninta da duk wata nutsuwarta sun ta'allaƙa ne akan abinda takewa kallo a matsayin MURADIN RANTA, Sedai saɓanin zuciyar ABOU HATEEM wadda take a...
216K 1.1K 33
This is a mix of different animes that have smut in them
155K 10K 40
WANNAN LABARI NE DA WASU BANGARE YA FARU A GASKE. BAN CANJA SHEKARUN YARINYAR BA KO ALAKA BA,AMMA NA CANJA SUNA, SANNAN BABU SUNAN GARI DA KUMA ANGU...