WUTA A MASAƘA

Από Ayshercool7724

28.4K 1.7K 154

labari akan wata yarinya me rawar kai da rashin jin magana sam, labari akan taɓarɓarewar zumunci, tarbiyya da... Περισσότερα

WUTA A MASAƘA
WUTA A MASAƘA 2
3
WUTA A MASAƘA 4
CHAPTER 5_6
7_8
9_10
11_12
WITA A MASAƘA 15_16
WUTA A MASAƘA 17_18
WUTA A MASAƘA 19_20
WUTA A MASAƘA 21_22
WUTA A MASAƘA 23-24
WUTA A MASAƘA 23_24
WUTA A MASAƘA 27_28
WUTA A MASAƘA 29_30
WUTA A MASAƘA 31_32
33_34
35_36
37_38
37_38
39_40
41_42
43_44
45_46
47_48
47_48
49_50
51-52
53_54

WUTA A MASAƘA 13_14

845 60 8
Από Ayshercool7724

🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥

WUTA A MASAƘA

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA)
*BAƘIN TABO (Labarin gasa)
*AƘIDATA (Paid Book)
* WUTA A MASAƘA

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in

❌❌❌
Ƙirƙirarren labari ne, ban yadda ayi amfani da kowane sashi na labarin ba ba tare da izinina ba.

Afuwan banyi Editing ba

KAMAR YADDA NA FAƊA TUNDA FARI, BA LALLAI IN DINGA SAMUN YIN POSTING KULLUM BA, IDAN AN GA BAN POSTING BA AMIN HAƘURI

13_14

Abba yai shiru yana nazarin
maganganun Alhaji Hashim sannan yace
"banƙi maganar ka ba Hashim, amma duk da ni na haifi Imran, idan na tursasa masa ya auri Amira, kamar ban masa adalci ba, da ita yarinyar daze aura da fari ba, kuma ina gudun ya wahalar da ita tunda ba sonta yake ba"

"Eh to, da wannan dan wannan, amma ka sani, da kai da kaya mallakar wuyane, zaka iya tursasa shibya kyautata mata, kuma koba komai ka isa dashi, saɓanin ka aurawa bare ita, wanda baka isa dashi ba, ni da ina da ɗa babba wanda ya isa aure, ba abunda ze hana in sa ya auri Amira, hakan Jijadi ne se Allah yai maka Rahama, ya goge maka laifin watsi da zumunci da kayi a sanadin hakan"

Alhaji Ali yace "hakane maganarka, amma yadda zan tunkari Imran da wannan maganar nake tunani, da kuma mahaifiyarsa, kasan Yarinyar daze aura ɗin yarinyar ƙawartace, kar inje shiya amince, su kuma su ɗagamin hankali"

"Da ita da ɗanta a ƙarƙashinka suke, dan haka ka tunkare shi da maganar kaji me zece, nasan baze baka kunya bama"

Alhaji Ali yai ajiyar zuciya yace "shikenan Ubangiji Allah ya wuce mana gaba"

"Ameen"

Ammi na zaune suna hira da Minal, akan yadda Abba ya fita harkarta shima, gashi bata san meyake shiryawa game da Amira ba, tana ta mita tana wassafawa Minal, wayarta ta fara ringing, Minal ta ɗakko wayar ta miƙa mata.

Maman Ilham ce take kiranta, ta karɓi wayar ta ɗaga "Hajiya Jamila, maganar kajin nan nayi magana da me kajin, yace 50 pieces zamu samu kawai a gurinsa"

"Maman Ihsan a sake dubawa, mu samu su cika ɗari mana, bana son muyi bikin da za'a tafi damu a baki, sonake ayi biki na kece raini, naji Babansa ma ze sai mana sa, wanda za'a saka a Abinci, wannan kaji na dinner ne, ina son sake masa magana, amma kwana biyun nan bama jituwa, shiyasa na ƙyaleshi, amma tun yanzu yakamata a sai san a ajiye"

Maman Ihsan tace "Subhanallah, lafiya dai ko?"

"Barni kawai Laɗifa, Magana ce akan wata Yarinya, 'yar ƙanwarsa, ƙanwar fa ta mutu yace ze ɗakkota in riƙe nace bazan iya ba, shine yanzu ta girma yarinyar ta zama fitinanniya shine yaketa take taken, wai ze kawomin ita gida, gani da yarinya mace, salon ta ɓatamin ita, shiyasa na ɗauke masa wuta inga iya gudun ruwansa"

Maman Ihsan tace "gaskiya idan yayi haka be miki adalci ba, ya zaki zauna da ƙatuwar budurwa karuwa a gida, kina mata kallon biri tana miki na Ayaba, gasky idan yai haka be kyauta ba, amma gara ki lallaɓashi ayi auren yaran nan ba Tare da wata matsala ba"

"Shikenan, zan san yadda za'ayi, zan tuntuɓeshi ki gaida Ihsan ɗin".

"To shikenan zataji, seda Safe"

Ihsan data shigo tun ɗazu ta tsaya tana jiran Mummy ta gama waya, ta kalleta tace "Mummy da Ammi kike waya ko?"

"Eh da ita ne har Imran ɗin ya tafi ne?"

"Eh ya tafi" ta samu Guri ta zauna Sannan ta kuma cewa "Mummy, naji kamar tana ce miki wai wannan ƙanwar tasa zata dawo gidansu ne ko?"

"Kai Ihsan, yanzu dama kasa kunne kikayi kina jin abunda nake faɗa?"

Ihsan ta girgiza kai tace "ba haka bane Mummy, Imran ya bani labarin yarinyar, sedai a duk lokacin da za'ay zancenta se inji gabana yana faɗuwa, sama bana ƙaunar maganarta, gashi Yanzu ana zancen zata dawo gidansu"

"To ke meye haɗinki da ita da zaki damu kanki akanta? Inma gidansu zata dawo da zama akanki zata zauna? Ina gidanki daban?"

"Mummy, Yarinyar cousin ɗinsa ce kuma kamar yana nuna damuwa akanta fa" tai maganar cike da karaya.

Mummy ta riƙo hannunta tace "haba Autan Mummy, tun kan ki shiga gidan Aure kin fara da karaya haka? Ki kwantar da hankalinki sekin so wata zata raɓi mijinki, kuma yarinyar da take yawon banza ina zatayi kima a idon Imran bayan gaki" tai maganar tana murmushi.

Ihsan tace "hakane Mummy, amma kin san mazan yanzu ba'a iya musu fa"

"Ke dallcan, don't put that in your mind Baby, ba ruwanki da wata kanki kawai zaki kafa, kuma Imran yana sonki sosai baze yi abunda ze saki damuwa ba"

Ihsan tai ajiyar zuciya tace "Shikenan Mummy, na dena damuwa insha Allah"

Shikuwa Imran kamar kullum sannu a hankali yake tu(insa harya shigo layinsu, wani matashine tsaye a jikin wata Mota yana danna waya, Imran ya ƙara gudun motar ya tafi yai kan matashin kamar ze bigeshi sannan yai wani wawan birki.

Matashin seda ya ja da baya, Imran ya fito daga motar yace "kai yaushe ka dira ba labari?".

Matashin yace "ban sani ba, takeni da mota dan ubanka, kayi jinyata a Asibiti, sedai kaci amarcin a nan Asibitin gurin jinyata"

Imran ya kwashe da dariya yace "kaifa ₦an iska ne wasu lokutan, to ya? Ya ake ciki ne ka diro ashe?"

"Ba dole in diro ba, tunda ka addabeni in dawo gani na dawo, ka bani uwar da zaka bani"

Imran yace "wace uwar zan baka kuwa? Kawai dama danka dawone ka tayani hidimar bikina'

"Ɗan rainin hankali, nima ina hanya na samo wata zazzafa, kuma insha Allah wuf zan da ita"

"Karma dai kayi, ka zauna kaita ruwan ido"

"Ai nayi mamakin lokacin da ka fara soyayya, har kake shirin Aure ka barni, dole in zuciya Yaseen, kamarni Khalid ace Imran ya rigani Aure, gaskiya wannan ci bayane a gareni".

Imran yai dariya yace "wai yaushe ka shigo ne?"

Khalid yace "da magaribar nan ne, nake gidanku Ammi tace min baka nan, shine naje nai Salla sekuma gaka ka dawo"

"Fatan ka dawo lafiya, ya hanya?"

"Alhamdilillah, mushiga cikin gidan se muci Abinci mucigaba da tattaunawa"

Daga nan suka shiga gidansu Khalid.

Hajiya Amira kuwa, tunda ta lalata musu ɗan wake tasa ƙafa ta bar gidan nan, ta tafi nata garari a gari da wannan magaribar, sedai duk inda ta wuce wasu na nunata, ana cewa itace wadda aka baiwa mota, wadda zata fito a videon raye raye, ita kam ko a jikinta hakan sam be dameta ba, sabgar gabanta kawai takeyi.

Se wajen sha ɗaya saura na dare se gata ta dawo Gidan, kamar kullum yauma da Sallamar ta ta shiga gidan, sedai ba wanda ya amsa mata, saboda a ƙule suke da ita.

Ta turo ɗaurin ɗan kwalinta gaban goshi, alamun itama daidai take da kowa, duk wanda ya kawo mata rainin tana daidai da shi ta wuce ɗakinsu, su Amina na zazzaune kamar marayu, sedai sun cika sunyi fam se harare harare sukeyi, ta share su ta ajiye 'yar ƙaramar jakarta da ledar hannunta.

Yadikko ta fito daga banɗaki, ta nufo ɗakin su Amira, ta ɗaga labule ta kalli Amira tace "tauraruwa me wutsiya ganinki ba Alkhairi ba"

Amira tace "yau kuma kirarin da zakimin kenan? Naji na karɓa kuma nagode sosai"

"Yanzu banda rashin imani da tausayi, Abincin da zamuci ki ɓata kika jiƙe murhun da itacen, saboda rashin tsoron Allah, Amira kina son ki gama da duniya lafiya kuwa? Ke kwata kwata bakya neman Albarka kullum cikin kalen jaraba kike"

"Yadikko, idan nazo gamawa da duniya lafiya ki hana, idan ke zaki saka in gama da duniyar lafiya ki hana dan Allah, ni kuna so ku gama da duniyar lafiya kuka zauna kuka dinga kwashemin Albarka kuna zagina jiya, duk cikinku aka rasa me cewa Allah ya shiryi Amira, se masu kiramuk watsewa da kwaso cuta, dan nayi hoto da mutum shikenan Iskanci nake dashi? Ƙaddarama hakanne idan su Amina ne haka zaki zauna kina kwashe musu Albarka kokuma Addu'a zakiyi musu?"

Amina tace "ke saurara, karki kuksakura ki kuma gwada misalin rayuwar da kike akanmu, muba irinki bane kike can kiyi abunki Amma ki dena misali damu"

Yadikko tace "gaya mata dai, ai ba kowane irinki ba, babu yadda za'ayi su Amina suyi abunda kikeyi, ban sani ba ko a can tsatonku ne da irin haka, shine kema kika tsotso a nono aka barmana masif......

"Ya isheki haka Yadikko!

Amira ta faɗa cikin tsawa "wasa yayi wasa Amma banda zungurin uwar miji da taɓarya, karki sake ki zagarmin iyaye, gaba ɗaya ba wanda yake raye sun mutu, iyaye da kakkannina, kuma ke kin san a tsatsonsu Babu wanda yai karuwanci, karki ƙara sako su a ƙazamar maganarki, in ba haka ba zan ɗau mataki, ni ɗin dai da kika saba yiwa kiyi tayi, Amma ban yadda ki taɓa iyayena ba tunda basa raye, ba abunda sukayi miki dan haka baki da hujjar da zaki dinga danganta abunda nake dasu"

Yadikko ta hangame baki jin yadda Amira ke tatala mata rashin mutunci, saɗara saɗara.

"Yanzu Amira ni kike gayawa wannan maganar haka?"

"Na gayamiki ɗin, kika kuma zagin iyayena ko kakata wallahi sena miki rashin mutunci, nagaji wallahi"

Yadikko ta fashe da kuka, tana "Innalillahi wa innalillahi raji'un, yau na shiga Uku, 'ya'yana da jikokina babu wanda ya taɓa sani kuka, babu wanda ya taɓa sani magana seke, daga taimako na riƙeki kin zame min bala'i, tir da halinki Amira, Allah ya kwashe miki albarka mara mutunci mara imani, da ikon Allah Se karuwanci ya zama silar jefaki cikin bala'in da bazaki iya fita ba"

Jikin Amira ne ya fara tsuma, hawaye na bin fuskarta, ta tabatta da Yadikko ta haifi iyayenta babu yadda za'ai tai mata wannan fatan, kullum burinta taga Amira ta tozarta, tai tayi mata miyagun Addu'oi da jan alkaba'i.

Su Sadiya ne suka shiga rarrashin Yadikko, suna bata haƙuri, jin kukan Yadikko yasa su Usaman suka shigo gidan suna tambayar ba'asin kukan Yadikkon.

Cikin kukan take cewa "waze sani kuka idan ba wannan makirar Yarinyar ba? Kullum burinta taci mutuncina da tsufana da komai, nasan da kakarta ce ni ba zata mata haka ba, ta kalli tsabar idona ta zageni tsaf taimin wankin babban bargo, ko tsufana bata duba ba, yarinyar nan bata da mutunci, bata san darajar furfira ba sam.

Kalaman Yadikko sunyi tsauri kuma sun tsaya a zuciyar Amira, tamkar ta haɗiyi ƙayar kifi me dafin gaske haka take ji a ƙirjinta, Yadikko makirar tsohuwace ta gaske, ta iya shirya kalamai da Magana, ƙarya da ƙarairayi ba wanda bata iya ba, gata da daɗin baki da fuska biyu dan haka babu wuya ta ƙulla maka sharri.

Amira ta buɗe akwatinta ta shiga gyara kayan ciki, yayinda Hawaye ke zuba ba ƙaƙƙautawa a cikin idonta, tana jik zafin addu'oin da Yadikko take mata, ba tayi yunƙurin kare kanta akan abunda Yadikko ta faɗa ba, saboda a gurin Amira basu isa ta tsaya tana gaya musu abunda ya faru ba.

Sadiya tace "ji munafuka, wai itama kukan take Jahila wadda bata san darajar furfura ba"

"Furfura me daraja, ita ta cancanci girmamawa, ba furfurar banza ba me son zuciya"

Amira ta bawa Sadiya amsa.

"Ke dan uwarki Yadikko ce me furfurar banza? Baki da mutunci Amira?" Zailani yai maganar yana kallonta.

Ko kallon inda yake Amira ba tayi ba, ta cigaba da kukanta, Zailani ya ƙule ya fita tsakar gida ya ɗakko ice, Yadikko cewa take rafkawa shegiya a muƙamiƙinta, tunda bata da mutunci.

Yana shiga ɗakin yai kan Amira ya soma sauke mata icen nan, ji tayi kamar kafaɗarta ta cire, take Amira ta ciro ƙaramar wuƙa a rigarta, tana kuka tace "wallahi ka kuma dukana da icen nan, sena yanke ka da wuƙar nan, sena maka kaciya da ita ince fyaɗe zakamin.

Da sauri Yadikko tace "ƙyale shegiya Zailani, karta maka halin karuwan, dama ta saba ganin tsiraicin maza, tunda ba abunda ta hango seyi maka kaciya, karta kassaraka dan idan tayi maka kaciya da wuƙa ta kashe ka kuma bata da Asara"

"Ni zaki kalla kice zaki yiwa kaciya? 'yar daba kika koma bayan karuwanci?"

"Nace ka ƙyaleta kar tayi maka illa a banza"

Sukai waje, Amira kuwa ta zauna a gurin ta cigaba da rusa kuka kamar an mata mutuwa, ga zafin dukan data sha, ga zafin irin rayuwar da ake mata, me cike da ƙalubale da cin zarafi.

Imran se bayan goma na dare ya ƙarasa gida, dama ya riga yayi dama, yana zuwa wanka kawai yayi ya hau kam gadonsa ya janyo waya, ya kira Ihsan suka cigaba da waya da, kamar zasu cinye juna, kowannen yana nunawa ɗan uwansa irin yadda yake ƙaunar ɗan uwansa.

Abba kuwa ya rasa yadda ze tunkari Imran da wannan maganar, saboda gani yake idan yayi haka kamar bewa Imran ɗin adalci ba, da ita kanta yarinyar daze aura ɗin, Amma yayi tunanin yayi tunanin ya rasa ina mafita akan lamarin banda wanda Hashim ya gaya masa, gashi sam shima ya fita sabgar Ammi, dan yasan idan taji maganar nan za'ayi tashin hankali ba kaɗan ba.

Amira kuwa yau kusan kwana tayi ba tayi bacci ba, ta sha kuka ta sha kuka, kamar ta shiɗe, ta dinga tunani daban daban, ji take kamar ta gudu ta bar gidan nan, amma idan ta gudu ina zata?

Haka taita wannan tunani har Asuba tayi.

Gari na fara haske Amira ta kintsa tai ficewarta, ta tafi gidan Anty Fa'iza, can ma da taje bata kula kowa ba, ta samu guri tai kwanciyarta, zuciyarta na mata raɗaɗi akan irin rayuwa da takeyi.

Imran ya fara zama busy, saboda hada hadar shirin bikinsa, dan an shiga satin biki, amma Abba yana jin nauyin gayawa Imran matakin daya ɗauka a game da Aurensa da Amira.

Abba yana shirin fita, sega kiran Alhaji Hashim, Abba ya ɗaga suka gaisa Sannan yace "Alhji Ali ya ake ciki ne? Ka sanarwa da yaron kuwa?, Zuwa yanzu yakamata ace an tsare yarinyar nan ta fara istubra'i fa"

"Hashim na kasa sanar masa, ba dan ina shakkarsa ba, ba kuma dan baze abunda nake so ba, sedai ina tunanin ita kanta mahaifiyarsa yadda zata ɗau maganar"

"Aikuwa idan baka faɗa musu yanzu ba, komai ze kacame maka, ko kana nufin se ranar ɗaurin Auren zega an ɗaura masa aure haka ba saninsa, an shiga satin biki, ita kanta yarinyar daze aura ɗin akwai buƙatar ka samu aje a sanar da magabatan yarinyar nan suma su sani"

Abba yace "to shikenan, zan san yadda zanyi Insha Allah"

Alhaji Hashim yace "to babu laifi, nima zanyiwa Meɗakina Magana, seta zauna a gurinmu, har gwaje gwajen da yakamata se ayi mata"

"Nagode sosai Hashim, Allah ya bar zumunci"

Abba ya ajiye wayar, ya ɗanyi shiru Sannan ya fito, ɗakin Imran ya nufa, yana zuwa yai knocking, Sannan ya buɗe ya shiga.

Imran ya shirya cikin dogayen kaya, da alama fita zeyi, yana ganin Abba yace "Abba da kanka, da ka kirani ai se inzo da kaina"

"Ni na kira ango, ai gara inyi tattaki inzo da kaina"

Imran yai murmushi cikin jin kunya ya sunkunyar da kai.

Abba yace "Imran magana nazo muyi"

Imran yace to Abba.

Suka zauna Abba na kan kujera, Imran yana zaune akan carfet.

"Imran wata alfarma nazo na nema a gurinka, sedai ban san yadda zaka kalli abunba"

Imran yace "Abba wannan wace irin alfarma ce haka? Wadda kake tunanin bazan iyayi maka ba? Ba abunda baka mana ba a rayuwa, mezesa in kasa maka wani abu da ka buƙata a gurina?"

"Imran bana son kaga dan ni na haifeka zan maka dole ko in cutar da kai, shiyasa na kira abun da alfarma, ba dole zan maka ba, alfarma ce zan nema idan kaga zaka cutu base kayi ba, ba zan maka dole ba"

"Abba dan Allah ka dena kiran alfarmar nan, amma me kake so inyi maka haka?"

"Imran, munyi magana da Alhaji Hashim ne akan wannan yarinyar Amira, kuma muka cinma matsaya aurar da ita, ko hakan zesa ta nutsu, sedai mun duba babu wanda ze iya riƙeta da mutunci da amana idan ba kai ba, kaine ɗan uwanta zaka iya rufa mata Asirin abinda tayi a baya, saɓanin idan ta auri bare, a taƙaice dai ina son zaka auri Amira ne, ka haɗa ta da Ihsan, amma ba dole zan maka ba, Kamar yadda na gaya maka a fari, amma hakan kamar jihadi ne, da ceto rayuwar yarinyar daga tarwatsewa gaba ɗaya, ban yanke wannan hukuncin dan in cutar da rayuwarka ba, amma me kace?"

Wani irin gumi ne ya shiga ratsa Imran, duk da sanyin AC daya cika ɗakin, amma wata irin zufa yake, tabbas ya shiga tsaka me wuya, dan sam ba shi da ra'ayin zama da mata biyu, saboda baya son fitina da damuwa, kuma ga wadda ake so ya aura, fitinanniya lamba ɗaya, wadda a zahiri ma shi ƙyamarta yake yi, amma ance ya aureta ya haɗa da Ihsan, anya kuwa ze iya? Can wata zuciyar tace 'kai har akwai alfarmar da Abbansa ze nema a gurinka ka kasa yi masa? Bayan haihuwarka da yayi ya sadaukar da lokacinsa, ƙarfinsa dukiyarsa gurin gina taka rayuwar?.

"Kayi shiru ba kace komai ba Imran"

Cikin sanyin jiki Imran yace "bakomai Abba, yadda kace haka za'ayi"

Abba yai murna yace "Alhamdilillah Masha Allah, dama nasan ba zaka bani kunya ba Imran, zanje in samu magabatan Ihsan suma muyi magana dasu, Sannan za'ayiwa Amira daukkan gwaje gwajen da suka kamata, insha Allah nasan ma Babu wata matsala"

Imran kam gaba ɗaya kansa ya gama kullewa, a ransa yace ko wani gwaji za'ayi mata ba ruwana, dan bazan iya haɗa jikina da Yarinyar data gama raba jikinta ga maza a titi ba.

Bema san me Abba yake cewa ba se jin muryar Abba yai yana "Nagode, Nagode sosai Imran, Ubangiji Allah yayi maka albarka, Allah ya haɗa kanka da iyalinka, ya zaunar daku lafiya, yadda kayi min biyayya Ubangiji Allah yasa yaranka su bika haka, sannan zan canza maka gidan da zaku zauna, seku zauna a gidana na Bamako gaba ɗaya, bana son ka rarraba kan iyalinka, insha Allah baza kayi dana sani ba a rayuwarka na gode sosai my Son"

Ya shafa sumar Imran, Sannan ya tashi ya fita cike da farinciki da annashuwa a ransa.

Imran kuwa zaman daɓaro yayi yana tunani, da wani idon ze kalli Ihsan, meze fara gayamata, ba abunda ze hana tayi masa kallon mayaudari, kimarsa zata ragu a idonta, taya ze fara zama da wannan Yarinyar, mara ta ido da shegiyar fitina, Amira ta rasa qualities da yawa da ake nema a gurin mace, tabbas daba Abbane ya nemi wannan alfarmar ba, da kowaye ya nema baze yi ba, dan sam Amira ba ta dace da tsarin rayuwarsa ba.

Yana nan zaune, Khalid ya shigo ɗakin Imran, cike da mita ya kalli Imran yace "kai ka rainamin hankali gaskiya, kaje ka shanyani ina zaman jiranka, kawai kazo nan kayi zamanka kana tunani haka akeyi?"

Imran yai shiru bece komai ba, se tagumi da yayi da hannunsa bibiyu.

"Wai ba magana nake maka ba ka shareni? Ka wani yi uban tagumi kamar ance Ihsan ta mutu"

Imran ya sauke hannayensa yai ajiyar zuciya, tare da sake dafe kansa.

"Wai zaka tashi mu tafi ne kokuwa?"

"Kaga a fasa fitar nan kawai"

"Saboda me, wai kai meke damunka ne, ka wani nustu kamar marayan muzuru, ka tashi mu tafi malam lokaci yana ƙurewa"

"Kaga a fasa fitar nan kawai"

Khalid ya kalleshi da mamaki yace "Kamar ya a fasa? Ban gane ba"

Imran yace "Khalid ina cikin damuwa ne, bazan iya fitar ba".

"Damuwar me, kai da zakayi aure, ai damuwa semu gawauraye"

"Khalid mata biyu wai zan aura lokaci ɗaya"

"Kamar yaya?" Khalid ya tambaya cike da rashin fahimta.

Nan Imran ya warwarewaa Khalid komai.

Khalid yace "lallaai kana cikin tsaka me wuya mutumina, amma Allah yasa haka shine mafi Alkhairi, insha Allah zakaga sakamakon biyayya, kayi haƙuri Imran, inaji a jikina zaka samu Alkhairi a sanadin Aurenta"

Imran kawai ya tashi ya tafi ɗakinsa yaje ya kwanta, dan yama rasa abunda zeyi gaba ɗaya.

Alhaji Hashim kuwa tuni yayiwa matarsa bayani akan Amira, kuma ta bashi tabbacin ita a kawo mata Amira zata riƙe, dan gaba ɗaya yarinyar tausayi ta bata da Alhaji Hashim yayi mata bayani.

Kasancewar mahaifin Ihsan ya rasu, Alhaji Ali da waliyan Imran, a ranar sukaje suka samu wan mahaifinta akan mata biyu za'a aurawa Imran a gurin ɗaurin Aure, Ihsan da kuma 'yar uwassa, shima wan mahaifin nata be nuna fushi ko ɓacin ransa ba, sedai yace musu "komai muƙaddari ne, kuma bawa baya wuce ƙaddararsa, Allah ya basu zaman lafiya ya haɗa kansu, amma kun san halin mata, se Addu'a, dan haka karku sanar musu da zancen, ni zan sanar musu idan lokacin da yakamata yayi, idan aka gaya musu yanzu ba zasu bari ayi bikin lafiya ba"

Abba yace"Allah ya wuce mana gaba, mungode sosai da wannan karamcin naka, Allah ya albarkaci yaranmu gaba ɗaya"

Imran kam bacci ma gagararsa yayi, yana kallon Ihsan tana kiransa amma ya kasa ɗaga wayar, saboda zatonsa An sanar mata ai ita da Amira ze aura.

Amira kam ta dena shiga sabgar mutanen gidan, duk wulaƙancin da sukayi mata, amma suna ta shirye shiryen zasu bikin ɗan uwanta Kaduna, Amira kallonsu kawai takeyi, 'yan gidansu akwai son abun duniya fiye da kima, basa iya ɓoye zalamarsu sam.

Amira Ta fito tsakar gida, Sadiya nata wanke wanke, ta baje kwanuka gashi ta zubar da dagwalon ƙanzo da komai, Yadikko tazo wucewa Amira ta kauce ta bata hanya, kawai ta taka ruwan omo, santsi ya kwasheta ta faɗi ƙasa, cikin kwanuka da dagwalon wanke wanke, ta buge ƙeya da tukunyar ƙarfe.

Take ta kurma uban ihu, ta dafe kanta wai Amira ta hankaɗeta, ko takanta Amira bata biba, tai gaba abunta.

Baba ya fito ya dinga yiwa Amira tijara, yana faɗin ya gaji da wannan tashin hankalin, baza'a kashe masa uwa a banza ba, Amira seta bar musu gida.

Ko kallaonsa ba tayi ba, ta ɗauki gyalenta da jakarta ta fice ta bar musu gidan.

Da safe Imran yana kwance, yana ta tunani ranar ne za'a fara bikinsa, Amarya za tayi henna day amma baya cikin nutsuwarsa, still Ihsan tana ta kiransa amma yaƙi ɗagawa ƙarshe ma ya kashe wayarsa gaba ɗaya, dan be san meze ce mata ba.

TV dake bedroom ɗinsa na tayi ita kaɗai, can aka nuno mawaƙin nan da Amira tayi hotuna dashi a Abuja, wai ze kai ƙarar Amira kotu, sunyi yarjejeniya zata fito a waƙoƙinsa, amma tai tafiyarta bema san inda ta shiga ba, dan haka 'yan sanda suna nemanta, duk inda take.

Imran ya tashi zaune, ya dafe kansa yama rasa me Yakamata yayi.

Wai wannan itace wadda ake son ya aura, wannan watsatsiyar Yarinyar.

Ya ɗakko wayarsa ya kira Baba a waya, Baba ya ɗaga lokacin yana tsaka da banbami akan Amira.

Imran yace "Ina Amira take?"

"Ai lamarin wannan yarinyar banma san me zance ba, kwana biyun nan masifa kawai take janyo mana, ta saka ƙafa ta fice ta tafi gantalinta, shekaranjiya tayiwa Yadikko zagin cin mutunci, dan an mata magana ta ɗakko wuƙa kamar wata 'yar daba, yau kuma ta hankaɗa Yadikko cikin tukwane ta kusa suma saboda yadda ta bugu a kanta, gaskiya na gaji ba.....

Imran da maganganun Baba ke sake kunnashi yace "kaga ba kira nayi ka wassafamin wannan takicin ba, duk inda take ku nemota, koku turomin lambarta inyi tracking ɗinta, zan shigo Kano anjima, idan ba haka ba ta gangamo wata rigimar, wadda ba iya kanta zata tsaya ba harku zata shafa, dan haka duk inda zaku samo labarta ku nemo ku turomin, zanyi tracking in nemota, tun kafin abun data janyo ya zama out of control"

Imran ya katse wayar yai jifa da ita akan gadonsa ya furta "Oh My God, Allah ka dubeni wai wannan ce zata zama matata, wannan yarinyar yasalam, am Sorry My Ihsan, baki cancanci haka daga gareni ba, amma dole inje in ɗakko Yarinyar nan kan 'yan sanda su kamata, abun kunyar zemin yawa, ace matar da Imran ze aura a hannun 'yan sanda, Sunan Abba ze ɓaci nima mutuncina ya zube"

Ya ɗau wayarsa ya kira Khalid, Khalid ya ɗaga, Imran yace "Khalid ka shirya zaka rakani Kano yanzu Please!"

(Oga Imran za'aje a ɗakko mana amarya 😂😂😂)

Share, Share, And share as much as you can please, masu nema daga farko yana nan a watpad a account ɗina
Ayshercool 7724
Ayi vote, ai following please

Masu san what's app group kuma ga link nan, mata kawai banda maza Please, Sannan akwai dokoki a group ɗin, in kina ɗaya daga groups ɗina karki joining please

https://chat.whatsapp.com/EAYHhAEJQPk8uGg2IeCQhX

Συνέχεια Ανάγνωσης

Θα σας αρέσει επίσης

72.1K 2.5K 7
This book is from my What-if's, The story starts during the class poll exam where the Class-C students would need to expel someone, but instead of Y...
AUREN SIRRI Από Asmau Abba Hudu

Μικρού Μήκους

8.7K 568 35
Labari ne daya kunshi soyayya da yanda taja akai AURE anma na SIRRI daga karshe sharri ya shigo ciki sanadiyyar kishi hartakai ga soyayyar da aka gin...
161K 335 20
just some of my horny thoughts;) men dni
105K 4.4K 30
Labari ne akan 'yan mata 3 wad'anda suka sha gwagwarmayar duniya suka ga bala'i a rayuwar su kala-kala, labarin ya gino ne akan makirci, yaudara, cin...