Twenty-eight - To Be Tainted

Start from the beginning
                                    

“Son, menene?”

Baiji ba saboda yayi zurfi cikin tunani. Tafa hannayenta tayi wanda ya dawo dashi daga kogin tunani. Saiya wayance ya share gemunsa tareda sunkuyar da kai.

“Ina wuni Mommy?” yace ƙasa ƙasa.
“Ango kaine tafe, ya kake?”
“Lafiya lau Mommy.” daga nan bai sake cewa komai ba. Haka sukayi shiru.

Shan kayan marmarin ta somayi abinta, saida takai rabi ta tura mashi gabansa.

“Ungo,”

Da yaso yayi gardama amma ya karɓa, he needs the motherly love. Haka ya shanye tas wanda yayi mashi daɗi sosai.

“Ina jinka....” ta ce mashi.

Dagowa yayi ya kalleta, fuskansa tsantsan damuwa ke ciki. Duk ya faɗa ya rame. Ana kiransa ango ne amma duk a takure yake kamar anyi renditing ɗinsa. Ji yakeyi kamar an kamashi da ƙarfin tsiya an kulle a kurkuku sannan an jefar da mukullin cikin ƙasan teku. Daga nan kuma aka soma ɗanɗasa mashi azaba.

Dogon numfashi yaja amma baice komai ba, saiya fito da harshen sa ya lashe leɓansa. Kallon Mommy yayi sau ɗaya saiya mayar da idonsa kan tiles yana kallo. Har lokacin raɗadi yake ji cikin ransa. Itama Mommy ta lura abu ɗaya zai saka shi firgici da tashin hankali haka. Watau auren sa.

“Mahfoozz...”

“Mahfooz ɗina,” ta sake faɗi.

“Mahfooz ka sani cewa a rayuwa dukkan mu munada sirrin da bazamu iya faɗi ba, munada kuma nadamar da ke hanamu barci gashi bazamu iya faɗin ma kowa ba, da kuma burin da duk ya muka so bazamu iya cin masa ba,” ajiyar zuciya tayi saita cigaba da magana, “Sannan munada soyayyar da bazamu iya mantawa dashi ba. Mahfooz komai na duniya mai wucewa ne, duk yadda kake ganin rayuwar ka yayi baki bakada wani mafita, ina kyautata zaton akwai wanda zasu so dama ace naka matsalar shine nasu....”

“Anya Mommy!” ya katse ta cikin murya mai rawa.

“Kwarai da gaske Son. Akwai wanda matsalarka nafila ne a wajen su...”

“M-mommy, bazaki fahimci abinda yake faruwa dani ba. Bazaki gane duhun dake cikin rayuwata ba. Mommy it's so dark and twisted, Idan da zan juya hannun agogo baya. Zanyi wasu abubuwan daban... Mommy ni mai laifi ne... Nayi laifi babba. Na zalunce mutane....” sai yayi shiru. Tuna ranar daya fara ganin Naseera yayi, yadda ake janyeta cikin ɗaki kuma baiyi komai. Anan ya lura wannan abun ne gagarumin kuskuren daya tabka.

“Mommy bana san auren nan....” yace ƙasa ƙasa yana dabda zubar da hawaye.

Shiru Hajia Fati tayi batace komai ba, itama karin kanta batasan Rumasa'u. Amma wannan abin yafi karfinta. Bata sake magana ba saboda batasan abinda zatace ba domin yaji dama dama.

“Mommy nace bana san auren...”

“Mahfooz dan Allah ka rufa min asiri.” Ta katse shi cikin masifa, “Naji sanda ka faɗa da farko. Kada wani yaji ko Daddyn ku yace nike daure maku gindi kuna abinda kuke so.”

“Mommyyy!”

Hawaye ya soma gangaro mashi daga idanu, a inda yake yanzu yayi mugun karaya daga dokin ƙarfen daya hau. Idan ƙasa zata buɗe ta haɗiye shi a wannan lokacin zai bala'in gode mata. Komai ya cunkushe mashi kwakwalwar sa sai tafasa yakeyi. Da bayan hannunsa ya soma goge idansa, yana jin wani rami a rayuwarsa wanda ya rasa yanda zai cika shi.

“Mommy!” Faash ya shiga ɗakin kai tsaye.

Anan ya sandare daga ganin Mahfooz, rabon da su haɗu tun sanda yace zai aure Rumasa'u. Baisan meke damun Mahfooz ba amma ya bashi tausayi, saidai har yanzu yana fushi dashi.

DIYAR DR ABDALLAH Where stories live. Discover now