Eleven - Farin Wasa

Start from the beginning
                                    

Suna jin ƙarar bindiga daga bayan ana harbi domin a tsorata su. Masu garkuwan basu taɓa samun babban kamu ba kamar Naseera kuma bazasu haƙura ba sai sun damƙeta. Ran Ogansu ne yayi bala'in ɓaci akan abinda Mahfooz yayi kuma sukace zasu koya mashi darasi. Tabbas idan suka kama shi zasu yanke mashi ƙafa ɗaya daga gobe bazai sake nuna jarumta a hurumin da bana saba.

Su kuma su Dr Abdallah sunata jiran Naseera basu ganta ba. Wayanta yana hannunta sanda masu garkuwa suka damƙeta saiya faɗa kwalbatin dake gefe wajen, yasa ba'a samunta. Anan Hajia Binti ta soma tada hankali. An kira a asibiti aka tambaya inda Naseera take amma ba'a ganta ba. Gashi kuma motan ta yana parking lot.

Mai gadi yanata Gyangyaɗi sanda suka tafi da Naseera, baima san abinda ake ciki ba. Kuka Hajia ta soma saboda jikinta yaƙi kwanciya. Ita tana tsoron kada Naseera ta sake faɗawa hannun wanda zasu cuce ta.

Haka Dr Abdallah ya tashi yasa direba ya kaishi asibiti, raban sa da asibiti tun randa aka sallame shi a matsayin mai jinya. Basuda camera a asibitin balle aga meya faru. Amma tabbas masu zama a réception sunce sunyi Sallama da Naseera inda ta basu ɗari biyar su sha ruwa dashi.

Hajia Binti sai kirar wayan Doctor takeyi tanaso tasan me ake ciki, shikam kasa ɗauka yayi. Baiso yace mata baisan inda ƴarsa ta shiga ba.

Abokinsa wanda sukayi Barewa College dake Zaria tare ya kira. Shi police ne kuma yanzu ya zama babba a wajen. Dr Abdallah ya labarta mashi komai. Anan yace su bari gobe kila ta tsaya wani wajen ne. A ƙa'ida sai mutum yayi awa arba'in da hudu kafin ayi declaring ɗinsa ya ɓace.

Abin duniya yayi ma Dr Abdallah cinkoso, tun bayaso ya saka tunanin yana kawar wa har ya yarda da cewa eh fah Naseera ta ɓace. Gari yanzu ya ɓaci garkuwa da mutane ake yi ta kowane fanni. Balle yasan cewa yanada arzikin da zai sa mutane suso cutar dashi.

Gwiwa a sanyaye ya koma gida, tun da Hajia Binti taji ƙarar gate ta fita da sauri. Ganinsa shi kaɗai babu Naseera ya sake firgita ta.

"Na shiga uku ni jikar Habiba." ta faɗa tareda fashewa da kuka. Sosai takeyi babu kakkautawa.

"Kila ta tsaya wani wajen ne?" yace dakyar saboda shima tashin hankalin yake ciki.

"Wallahi wani abu ya sameta ne. Ai ba yanzu ta soma shiga cikin haka ba,"

Kallon ta Dr Abdallah yayi yana nazari, "Ban gane ba?" yace tareda kafata mata ido kur. Har lokacin basu bar parking lot ba.

"Babu komai," saita juya da sauri ta shiga ciki. Bai ce komai ba yabi bayanta suka shiga. Kitchen ta wuce tana kuka. Bataso ta gayama Dr abinda ya faru da Naseera, kafin zuciyar sa ya buga ta rasa shi gashi babu Naseera da zata ɗanji sanyi.

Tsaye yake a bayanta yana kallonta, kokarin gane ma'anar maganar datayi ɗazu yakeyi. Shi a nashi sanin Naseera bata taɓa shiga wani mugun tashin hankali ba. Amma kuma kila sanda yake ciwo abu ya faru basu sanar dashi ba.

Anan ne tunanin yazo masa, tabbas abu zai faru kuma ayi mashi ƙememe.

"Binti," yace cikin ƙaramin murya.

Bata tanka ba, illa jan majina tana kokarin saisaita kanta. Hannunta tasa tana share hawayen da suke zuban mata kamar famfo.

"Binti," ya sake maimaitawa, "Maman Naseera," ya kuma faɗa. Anan kuma ta barke da sabon kuka. Kawai tunani takeyi kada masu garkuwa da mutane ne. Makon daya gabata sun shiga sun ɗauki wani Alhaji a layin. Batasan ya zatayi da rashin Naseera ba, sun bala'in shakuwa. Tasan duka al'amuran ta. Naseera bamai shige shige bane yasa tasan bataje gidan kawaye ba.

Sai Naseera tayi shekara 2 batayi baƙuwa ba a matsayin ƙawa. Yasa yanzu duk ta rude. Dr Abdallah ne ya ƙarasa inda take tsaye. Riƙeta yayi yana dukan mata baya a hankali alamar tayi shiru, saida yaga ta tsagaita saiya soma magana.

DIYAR DR ABDALLAH Where stories live. Discover now