AURE NAKESO 💞💞💞💞💞💞

Mulai dari awal
                                        

*********dr yace yes snipper ne saboda shine yake kashi nan take, khalifa yace alright thank you so much, cen ya baro gawar karen nasa, ya dawo gida amma ina ya kasa samun natsuwa da sukuni, yana karasowa baiyi birki ko ina ba sai cikin kitchen dinsa nan ya nufi inda ake zuba shara ya dauko basket din ya zube tsakiyar kitchen din, shara ce sosai, nan yasa hannu tamkar wani mai sabuwar hauka sai tona sharan yakeyi, nan yaci karo da yar karamar bottle wacce aka rubutawa snipper poison, jikinsa yana rawa yake kallan bottle din, dakyar yake hadiye yawun bakinsa, nan yayi saurin wanke bayan bottle din ya zura a aljihun wandonsa, ya kwashe sharan tamkar ba abunda ya faru, ya wanke hannunsa sosai da dettol da kuma sauran sanitizers na hannu, bayan ya kammala ya fito ya zauna dinning yana breakfast dinsa, yi yake amma sai tambayar kansa yake, wayake kokarin kasheman iyali? ahaka dai ya karasa breakfast dinsa ya fito, ya nufi motarsa har ya bude kana ya Kira gateman dinsa cikin hanzari ya karoso yana fadin gani yallabai, khalifa yace shekaran jiya dawa dawa ya shigo gidan nan? gateman din yayi shuru alamun mai nazari kana ya girgiza kansa yace gaskiya ba wanda ya shigo bayan uwargida da ta fita da sanyin safiya kuma bata jima ba ta dawo, khalifa yace ka tabbata? yace sosai yallabai, khalifa yace toh idan na fita yanzu make sure babu wanda ya shigo babu kuma wanda ya fita, gateman din yace harda hajia? Cikin bacin rai khalifa yace har uban hajiar, hakan yasa gateman din ya tsorata, jiki na rawa ya juya dan budewa khalifa gate din

**********bayan fitarsa baiyi birki ko ina ba sai office dinsa, nan ya shiga rai bace sai gaida shi ake amma ko ta kansu ba yayi, sai mamakin shigowarsa suke saboda daka gansa kasan ba shirin zuwa office bane, safa da marwa ya shiga yi tsakiyar office dinsa, ransa abace sai cizon down lips dinsa yake, ahankali ya saka hannunsa a aljihun wandonsa ya fito da bottle din snipper din ha shiga juyata left nd right, up nd down, daidai wannan lokacin ya aje bottle din akan table din tare da lumshe idanuwansa, bayan wasu yan second ya bude idanuwansa ya koma ya zauna, sai juyi yake akan kujeran, azuciyarsa kuwa sai cewa yake could six b zaynab's hand work? amma zaynab da nasani da shegen tsoro bana tunanin zata iya kashe koda kwaro ne balantana ta zubawa mutun guba a abinci, kasa hakurin hakan yayi dole ya dannawa dr Mahmoud kira, bayan sun gaisa yace alaji zo office dan Allah inasan ganinka, dr yace okay toh ba matsala

***********hanan tace kai samira nifah banasan takura gaskiya, na gayamaki dix guy ya wuce inda kike tunani, samira dake tsaye bayan kujeran da hanan take zaune tace duk abunda zakice kice nidai kawai ki tashi mu tafi, hanan ta mike tsaye dama shirye take cikin jallabiya black tayi rolling da red veil, ta dauki car key dinta ta fice fuuuuuu, samira tana murmushi ta take mata baya

*************dr Mahmoud ne zaune yace tunda na shigo ka kasa cewa komai khalifa, talk to me mana, khalifa ya gyara zamansa ya maida dubansa kan dr yace taya zan iya magana dr, wallahi ina cikin tashin hankali yanzu, na rasa inda zansa kaina, dr Mahmoud yace problem shared is problem solved dan haka talk, nan take khalifa ya kwashe komai ya gayawa dr Mahmoud, dr Mahmoud ya jinjina kansa kana ya huro iska mai zafi daga bakinsa yace taya akayi poison din yakai cikin gidan ka har yakai ga abinci? khalifa ya tsare shi da idanuwa kana yace nima shine bansani ba, dr Mahmoud yace lallai wannan ba karamin tashin hankali bane, yanzu kenan kana nufin ka rasa yanda akayi,bayan matarka aisha wa zai shigo gidan ka? sannan bayan yan uwanka da nata wa yake shigowa? khalifa yace matana biyu dan haka komai mai iya faruwa ne, dakyar dr ya iya hadiye yawun bakinsa yace bangane mata biyu ba, yaushe kayi ta biyu din? khalifa yayi ya kara sunkuyar da kanshi kana yace uhmmmm ayyi aisha itace matata ta biyu, zaynab kuma itace matata ta farko, dr Mahmoud yace lallai dole ka shiga rudani, amma tunda har kana da mata biyu ayyi kamata yayi ka saka yan sanda aciki saboda ayi investigation mai kyau irin wanda ya dace, khalifa yace no ayyi bana bukatan police aciki, shiyasa nakesan shawaranka , yanzu mekake tunanin yakamata nayi?

*******dr Mahmoud yace yanzu kai zaka yankewa kanka hukunci, ka tuna irin zaman da matanka biyu sukeyi, na tabbatar akwai wacce batasan daya, ko kuma ace duka basa so, saidai inada tabbacin cewa daya kishi ne kawai daya  kuma hauka ce in d name of kishi, amma indai har kayi bincike aka tabbatar maka da ranar da abun ya faru babu wanda ya shigo ko ya fita then tabbas dayan matanka is responsible for dix, na tabbatar ita wannan da ke kwance bazataci poison just to frame d other one ba, khalifa yayi shuru nadan lokaci kana yace kayi gaskiya dr, sannan am pretty sure zaynab is responsible for dix saboda zaynab a fili ta nunawa aisha batasan ta, amma no wahala zanyi handling case din yanda ya dace

AURE NAKESO 💔💔💔💔💔Tempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang