“Nawancy  kin yi kyau”

“Dan kai kadai na yi ta na gode da ka yaba”

Sai dan yi murmushi.

“Aiko ya kamata na bada tukuici ko?”

“Ka adana tukuicinka da daddadan kalamanka har sai na fada maka dalilin wannan kwaliyar tawa”

“Akwai wani daliline bayan wanda na gani?”

“Sosai ma, a wancan gani ka yi, wannan kuma ji zaka yi”

Ajiyar zuciya ya sauke yana murmushi.

“Nawancy  kina yaudarar zuciyata da yawa, da fushi na zo nan gurin, amman kin shiga kin yi nikaya kin tarwatsa duk wani damuwa da fada da na zo da su”

“Ai daman haka ya kamata ko wace amarya ta kasance gurin angonta, mai wanke danuwarsa ta shimfida farinciki a zuciyarsa”

“Ina ma da gaske Nawancy amaryar Bilal ce da yafi kowa farinciki a duniyar nan”

“Akwai wanda ya isa ya hana abunda Allah ya zo kasanewarsa tun farkon hallitar Nawwara?”

“Babu”

“Ashe ko Nawwara sai ta fi Bilal kasancewa a cikin farinciki daga ranar da aka daura aurenta da angon da ya fi ko wane ango tsada a duniyar nan”

Ya yi murmushi yana kallona tare da lumshe ido.

“Ina son ki sosai Nawancy”

“Kai so na kawai ka ke ni ko kaunar ka na ke”

Ya sauke ajiyar zuciya.

“Kamin ki kaini duniyar da ba zan iya dawowa ba, fadan min dalilinki na yi wannan kwaliyar”

“Kamin na maka albishir mai tsada ya kamata ace ka fada min abunda ya kawo ka nan”

“Yo tun yaushe kika duniyar kwakwalwa kika mantar da ni wanene ni ma, balle abunda ya kawo ni nan kuma”

“Yanzu dai rumtse idonka sai na fada maka albishir din”

“Ai kunnene yake ji ba idanuwa ba”

“Ina gudun kyawawan idanuwan nan naka su ba ni kunya ne”

Sai ya yi dariya ya lumshe idanuwasa.

“Inna ta ce na fada maka, idan ka shirya ka turo magabatanka suje can Baban gida su gana da nawa magabatan”

Da sauri ya bude idanuwansa ya kallini

“Da gaske Nawancy?”

“Na saba maka irin wannan wasan ne?”

Wani ihu ya yi ya daka tsalle ya dire, ni kuma na yo cikin gida da gudu ina dariya. Da na shigo sai na ce da Inna Bilal ya ce zai turo magabatansa amman be saka rana ba.

“Mashallah Allah ina fatar kina sonshi dan karki yi wa kanki zabi irin na baya, kuma ina son ki bawa Allah zabi a cikin lamurranki nima zan taya ki da addua idan aurenki da Bilal alheri Allah yasa ayi, idan kuma ba alheri ba ne Allah ya kawo maslaha”

“Amin Inna, inshallah Alheri ne”

Daga wannan sai fira ta biyo baya Inna na ta nanata min burinta na ganin na yi aure domin shine kwanciyar hankalinta, a daren Bilal ya yi min kira ya fi a kirga ni kuma na ki dagawa, misalin uku da rabi na dare na tashi na yi nafila na Mikawa Allah zabina akan ya zaba min dukan abunda zai fi zama alheri a rayuwata. Washe gari bayan na gama komai na shirya na nufi asibiti zuciyata cike da tunanin yanayin Jidda gabana kuma nata faduwar da ban san daliliba.

Jirbil kawai na tarar a dakin Noor baya nan, na gaisheshi cikin ladabi kamar yadda na saba masa a yanzu. Be amsa min ba sai ya matso kusa da ni yana ta kallona kamin ya risina kasa wanda hakan yasa ni ja da baya.

RAI BIYUWhere stories live. Discover now