BANKWANA

7.3K 603 132
                                    


Assalamu alaikum

I'd like to dedicate this chapter to my first readers from Al'amarin zuci, through Amaren Bana to Ke nake so

ummu

ayeesh_chuchu

mamanmus

@sadiyaumar

NajahIM

lisco_

@fatimaumar

And all of you my lovelies, you all are important. I feel the love. It's ironical, but words can't be enough to express my gratitude to you my peeps.

*********


Bayan sun kammala karyawa ne. Abdul-Aali ya-cewa Mai-jidda. "Anjima zan kai Hamamatu gidan Sister dinta da ta haihu, zan ajiye su Ramla gidan Abba, za ki je ne, ko ki na gida?"

Ta yi shiru tana tunanin, idan suka watse, gidan zai mata shiru, don haka ta-ce. "Ba damuwa zan shirya, sai ka bar mu gidan Abban".

Suna fita gidan yar Hamamatu, suka fara zuwa ma mai haihuwa, dukan su suka shiga har da Abdul-Aali yayi mata gaisuwa. Zulfa'a tana da fara'a, kasancewar ta kan hadu da Mai-jidda a sunan yaran kanwarta, ko wata hidima, ba ta gwada mata wani canji ba.

Suka gaisa kamar koyaushe, yayin da Hamamatu take ta jin haushin yarta, wai yaya za ta washe baki, ta yi ta yiwa kishiyarta dariya.

Da suka zo tafiya ne. Mai-jidda ta bude jakarta ta fito da ledan zani, ta ba ta. "Ga wannan ba yawa ayi goyo. Allah kuma ya raya cikin addinin musulunci."

"A'a haba Anty Hauwa, kuma sai ki shiga dawainiya haka? Ki bar shi kawai, don Allah."

"A'a kar mu yi haka don Allah, ki karba, ai na riga na yi niyya."

"To shi kenan. Allah ya amfana. Allah ya bar zumunci."

"Ameen-Ameen. Mu za mu wuce kar Dadin su Mimie ya yi ta jiran mu."

Nan ta rike hannun Mimie ta daga Ramla a hannu. Hamamatu ta bi-ta da kallo. Suna fita, ta hau yiwa Zulfa'a bala'i.

"Haba ke kin faye daukar abu da zafi, tana da kirki sosai, ki ga yadda take da yaranki fa."

"Duk kinibibi ne, bari na fada miki, ke kuma dole ki fadi haka, tunda har zani aka kawo miki."

"Akan ba ni da su ko meye? Ke dadina dake rashin son gaskiya."

Ba abinda yake damun Hamamatu, illa yanzu haka Mai-jidda za ta je ta kame a gaban motar Abdul-Aali suna tafiya, suna hirar soyayya. Tamkar ta cewa Zulfa'a ta fasa wunin, don gaba daya ta kasa daina tunanin Abdul-Aali da Mai-jidda.

Sai da yamma ya dauko Hamama, suka taho gidan Abba, nan suka samu su Ramla sun sha kyau, saboda Mai-jidda zama ta yi ta rangada masu kitso, ta aika aka sayo mata Ribbons ta jera masu a kai.

"Mami kin ga kitson mu. Anty Hauwa tayi mana, kuma ba zafi".

Ganin Abdul-Aali a wurin, ba ta son ta nuna haushinta ta-ce. "Lallai kun ji dadinku, sannu Anty Hauwa, kun ce mata thank you?"

KE NAKE SOWhere stories live. Discover now