KARSHEN TUKATIKI...

7.4K 689 257
                                    

This is for the silent readers, I hope this chapter will make you comment and vote after reading

Oops! This image does not follow our content guidelines. To continue publishing, please remove it or upload a different image.

This is for the silent readers, I hope this chapter will make you comment and vote after reading.

Love you all for your unwavering support throughout.

And guess what???

Ke Nake So is going strong at number 14 in romance 💃🏼 , it's all possible because of you my peeps.

And because of that here is a long update for today, maybe even double updates if I see lots of comments. So silent readers uhm ehm uhm *clears throat*

Happy Reading.😉

*********

Tun randa Alhaji Yusuf ya bar gidan su, ba ta sake zuwa wurin aiki ba, hakan ya sa ran laraba da yamma, sai ga Walida ta zo.

"Mai-jidda lafiya kuwa kwana biyu muka jiki shiru?"

"Ke dai kin faye damuwa. Yaya Mai-gidan? Ina Dan hutawa ne, ko ke ma za ki shiga layi?"

"Lafiya kalau. Maganar gaskiya na ke miki, me ya faru?"

Nan ne Mai-jidda ta fada mata duk abin da ake ciki.

"To don kin rabu da Alhaji Yusuf, shi ne za ki daina zuwa aiki, mu ma ki watsar da mu? Aikin ki fa wa ki ka barwa? Kin san dai ni ba zan miki ba, don haka ki shirya gobe, daman ki dawo".

"Me zan dawo na yi? Oh na manta kin san ran Asabar daurin aurena?"

Walida ta dubi Mai-jidda, sannan ta dafa kafadarta cikin kulawa. "Ki kwantar da hanakalinki, tunda dai ana addu'a. Insha-Allahu alkhairi ne."

"Yaya na iya idan ban kwantar da hankalina ba? Jiya suka kawo lefe, ga shi can a dakin Umma, ya dauka wani abin sa zai burgeni, bayan na san duk karya ne ya tsane ni".

"Allah ya ganar dake kawai, zan iya cewa, ni tashi mu je ki nuna min na gani."

"Wa ni? Allah ya sawwaka ko kalan akwatunan, ban sani ba, ki yi sallama dakin Umma ki duba."

"Tunda na zo kam, ai sai mu kalla tare idan kunyan su Umma ki ke ji."

****

Ranar Juma'a sai ga Yaya Maryam da yaranta su, a dole sun zo aure, kallon su kawai take yi, don duk abinda ake yi tana kwance. Sai sallah ke tada ita. A daki ta shigo ta sameta.

"Wai ke Mai-jidda me yake damunki ne haka? Ace mutum ya rinka daukar zafi da rayuwa haka idan za ki warware ki shiga jama'a gwamma kin shiga, me ki ke son mutane su yi tunani idan suka ga wannen bakin halin da ki ke yi?"

"Yaya Maryam me za su yi tunani kuwa, banda ina alhinin rashin mijina da ya rasu, wanda kuma hakan ne."

Yaya Maryam ta zauna a gefen gadon Mai-jidda, sannan ta-ce. "Ni da ke mun san cewa wannan ba shi da sauran amfani a wajenki, kwarai ba zan hana ki tunanin Dokta ba, amma ya kamata ki rinka boye damuwarki, sabuwar rayuwa za ki soma.

KE NAKE SOWhere stories live. Discover now