17.

417 60 32
                                    



Assālamu ʿalaykum wa raḥmatu-llāhi wa barakātuh.

Kwana da yawa!🤭 Na yi kewar ku sosai na yi kewar yar mitsilan Abba.

hajjoabukur ce ta dauki nauyin wannan babin💃🏻 ku garzaya domin karanta littafinta da ke nan wattpad.

Oops! This image does not follow our content guidelines. To continue publishing, please remove it or upload a different image.

Tana tafiya kawai ta ji an rufe mata ido ta baya

Oops! This image does not follow our content guidelines. To continue publishing, please remove it or upload a different image.








Tana tafiya kawai ta ji an rufe mata ido ta baya. A firgice ta juya zuciyarta kaman zata faɗo. Lumfashi ta sauke ganin waye.

"Ƙawata Maryam!"

Maryam ta harareta tana maida lumfashi. "Zubaida kin bani tsoro."

"Yi haƙuri. Ina ta kiran ki ba ki ji ba. Ko duk fargaban exams dinne ya kama ki tun yanzu?"

"Ayyah ban ji ba." Juyawa ta yi ta ci gaba da tafiya Zuby na gefenta. "Exams kuma da yardan Allah za mu yi passing so babu wani fargaba."

"Allah Ya bamu sa'a."

Tare su ka isa ajin inda su ka same shi cike da mutane. Wasu zaune a ƙasa wasu a tsaye, wasu zaune kan kujerun theatre din. A gaban kujerun ita da Zubaida suka zauna. Mintin su ashirin suna jiran malamin. Sai da lokacin shi ya kusa ƙarewa sai gashi ya zo. Kuma bai wani daɗe ba ya tafi. Da yake jarabawa nata matsowa duk yawancin malamin sun gama courses ɗin su daidai ne ke aji yanzu.

"Ki zo muje ɗaki na kafin next class." Zubaida ta ce wa Maryam.

Tunda su ka dawo hutun mid-semester Zuby ta dawo kaman yanda ta ke da. Har haƙuri ta ba Maryam a kan shareta da ta yi, kuma ta faɗa mata dalilinta na yin haka.

"Lokacin wani tashin hankali ya faru a gida amma yanzu an warware komai Alhamdulillah."

Maryam ta daɗe da sanin rayuwar Zuby ya banbanta da nata, duk da kuwa dukan su sun rasa mahaifi.
Bayan rasuwar Abba rayuwar su tabbas ta chanza amma chanjin ba chan-chan.

Ba haka ta kasance da Zuby ba.

Gaba ɗaya rayuwarta ta chanza daga inda ta santa. A nan Zaria suna gidan dan uwan mahaifin su ne, bayan rasuwar baban su maman su ta koma Yobe da zama. Dama su asalin ʼyan chan ne. Sam zaman gidan dan uwan baban su baya masu daɗi. Ita da ƙaninta ne suke zaune a nan saboda makaranta. Sauran ƙannenta su uku suna wurin maman tunda su ƙanane. Babban cikin su shekarar ta shida.

You've reached the end of published parts.

⏰ Last updated: May 09 ⏰

Add this story to your Library to get notified about new parts!

Lokaci NeWhere stories live. Discover now