2.

403 87 8
                                    
















Ranar ta kasance assabar babu makaranta. Maryam da wuri ta tashi ta taya Umma wankin wake, Idris kuma ya kai niƙa.

"Safiya idan ba ki shiga kin yi wanka ba sai na gamu da ke. Yarinya sai ƙazanta." Inji Umma. Safiya na ƙunƙuni ta dauko bokiti ta nufa ɗaki. "Saura kuma kada ki yi wankann da kyau ki shiga ki watsa ruwa kawai ki fito.

Maryam ta gimtse dariyarta dan yanzu za su yi faɗa in Safiya ta ganta tana yi mata dariya. Tun ɗazu Umman ke bin kanta har ƙarfe uku ta yi.

Sallamar Abba ya sa ta ɗaga kanta daga inda ta ke zaune kan tabarma tana wasa da kayan kicin ɗinta. Ta yi mai sannu da zuwa, ya ce ta kawo mai ruwa.

Abba a gajiye ya ke, dawowar shi kenan daga tudun wada inda gidan mahaifiyar shi ya ke. Sam bai ji daɗin halin da ya samu mahaifiyarsa a ciki ba. Zama kan kujera ya yi zuciyarsa a cunkushe. Bai ji shigowar Maryam ba sai da ta taɓa shi.

"Abba ga ruwan."

Ya karɓa kofin ya kurɓi kaɗan ya maida mata. "Ina Umman ku?"

Maryam ta kalli ƙofar ɗakin Umma. "Inaga ta shiga bayi, in kirata ne?"

"A'a kyaleta. Mai ku ka dafa?"

"Shinkafa da miya sai salak da aka yanka."

Fuska Abba ya yamutsa. "Kawo mun salad ɗin kawai, idan akwai lemun tsami ki kawo mun."

Umma ta fito sanda Abba ke ba Maryam umarni. Gefen shi ta zauna kan kujera. "Lafiya ba za ka ci abinci ba? Ko baka jin dadi ne?" Ta tambaya  saboda yanayin shi ya nuna babu lafiya.

Arc. Ahmad ya karkata kai ya kalleta kan shi har yanzu jingine jikin kujera. "Yaushe rabon da ki ga Inna a asibiti?"

Umma ta ɗan yi jim tana tunani. "Gaskiya an kwana biyu."

Ido Arc. Ahmad ya runtse, fuskar shi ta nuna ba amsar da ya so ta bada ba kenan. "Sa'adah, akwai matsala. Musa baya kai Inna asibiti."

Gaban Umma ya faɗi. "Me yasa ka ce haka?"

"Gashi ba kya ganin su, ce mun ya yi fa duk sati likita ya ce su riƙa komawa check up. Da suna zuwa ko yane ai zaki gan su. Allah na tuba, kuma yanayin jikinta ya nuna, da tana samun kulawan da ya kamata da tafi haka lafiya. Sa'adah na yi sakaci."

Umma ta kamo hannunsa kenan Maryam ta shigo. Itama ta ji a jikinta kaman ta katse wata muhimmiyar magana. Da sauri ta ajiye kwanon salad ɗin ta koma. Umma ta sake kamo hannun mijinta.

"Ban taɓa zaton haka daga Musa ba," Abba ya ce yana girgiza kai. "Lokacin da na ce zan dawo da Inna nan shi ya ƙiƙiye ya ce in barta a chan saboda iyalin shi na kusa, za su kula da ita, har 'yar shi ta koma gidan duk dan in yarda. Na ce to ba zai yi komai shi kadai ba,  duk wani abu da ya shafi ci da sha, da asibiti duka ni zan kula da shi. Duk wata na ke tura mai kuɗi, idan bai isa ba zai sanar da ni in ƙara. Ashe dama ba dan neman albarka ya ke yi ba, da wata manufar a ran shi."

Magana Arc.Ahmad ya ke ran shi na ƙuna. Babu abunda ya fi ciwo ka gano mutumin da ka yarda da shi yana munafuntar ka, mutumin ma ɗan uwan ka da kuka fito ciki ɗaya wanda baka taɓa haɗa shi da kowa ba.

Su uku mahaifiyar su ta haifa. Shi ne babba, sai ƙanwarsa Badawiya da Allah Ya yi wa rasuwa da ɗaɗewa, ɗan ko aure bata yi ba, sai Musa. Inna ta haifi yara da dama kafin Ahmad sai dai duka basu yi tsawon rai ba. Allah Ya ƙaddara shi da sauran suna da tsawon rai har su ka kai haka. Akwai sauran ƴan uwa da suka haɗa uba amma tun bayan rasuwar mahaifin su shekaru goma da su ka wuce zumuncin su ya lalace. Dama zama ne a ke yi mara daɗi, wanda ya haɗa alakar na barin duniya kowa ya kama gabansa.

Lokaci NeWhere stories live. Discover now