Part 14/15

339 24 0
                                    

🐲🐲🐲
UQUBAR UWAR MIJINA
🐲🐲🐲
(Based on True Life Story) (Full of Sorrow)

Story Nd Written By
Khadeejaht Hydar
Young Novelist.

Dedicated to My gist patner,my abokin fad'a,my kinda hrt bro.
HAMZA.Tnx 4 d du'a,nd idea.

https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*

*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*

(14)&(15)

Haka na zauna ina rainon cikina Wanda yanzu yake da wata hud'u,kuma koda yayana yasani yaji babu dad'i amma yad'auki hakan amatsayin kaddara saboda lokacin dayafara min fad'a da Cewar saina fad'i Wanda yamin cikin.

Ganin yadda nake kuka nakasa maganane yasashi sassauta murya, cikin lallashi yace"...Y'ar uwata fad'amin waya miki wannan abun don nasan ba halinki bane."

Nan na sanar masa abunda yafaru,hak'ik'a yaji bak'incikin faruwar hakan amma yace"...badamuwa haka Allah yaso zan fahimtar dasu Baba,kuma nasan zasu fahimceni."

Ina kuka nace"....Dan Allah karka sanar dasu ,yace"....to Fatima inban sanar dasu ba haka kawai saisu ganki da yaro ko yarinya?, A'a baze iyuba karki damu zanyi k'ok'arin naga sun fahimta."

Nace"...to yaya nagode,daganan kuma nacigaba da rainon cikina kuma a lokacin nad'auki d'amarar haifar abinda ke cikina kuma na rungumesa hannu biyu."

Da yayana yasanar da iyayena sun kad'u matuk'a,amma haka suna danganawa Allah komai kuma suka k'ara jaddadamin nakula dakaina kuma narik'e mutuncin kaina nasan darajar kaina kada na na kuskura nasake tafka kuskure irin wannan.

Toh hak'ik'a ina cikeda danasani dukda nima bansan tayaya hakan yafaru ba,kuma har lokacin yakan zo gidan danake yakawomim abubuwan buk'ata harda kud'in zuwa asibiti da komai.

Kuma har yanzu munason juna amma dayamin maganar aure zan nuna Sam banyardaba,dukda nima wani gamin abun yana raina.

To yau cikina yakama wata 7 inda cikin yayi girma sosai kamar wacce zan haifi Y'an uku,gashi bana shan wata wahala sab'anin haihuwar Ilham.

Wani gamin nakan zauna ina tuna rayuwata ta da,sai na dinga cewa anya nice kuwa saboda nima ina ganin canji acikin rayuwata,amma nakasa gane hakan.


To wata rana muna zaune sai naji duk bayana yana ciwo,saboda dama tun safe nakejin ciwon Mara da baya amma nayi shiru aganina ai cikina bekai watan haihuwa ba.

Da safe natafi kauyen danginmu don kai musu ziyara duk da inajin ciwo anma bankai cewa haihuwa bace,ina zuwa na kwanta don hutawa.

ABINDA YA FARU KAFIN RABUWA TA DA KHAMIS SHINE.

Wata rana ina kwance sai nayi mafarkin ga wata bafulatana tana d'ebo zinare a kwarya tana zubawa ajikin gidan Khamis,tohm a lokacinne arzikin Khamis yaketa bunk'asa,ganin hakanne yasa mahaifiyarsa cin alwashin rabamu saboda tun farko bani taso ya auraba Y'ar aminiyarta taso ta bashi to hakanne yasa tace saita raba aurenmu kuma ta lalatamin rayuwa.

Hattara mata muguji zuwa gun bokaye da malamai,komai na Allah ne tana iyuwa kayi mugunta kuma ta koma kanka ko zuri'arka Ku biyoni donjin yadda rayuwar Khamis ta tagargaje sakamakon aikin uwarsa.

Da cikin Ilham ina kwance saiga wata baiwar Allah da Hijab d'inta fari har k'asa,tace"....Ki tashi kige gun Malam Ibrahim kice masa ya taimaka ya warware abinda ya miki,kuma ta nunamim kamannin Malamin da inda yake."

Muje zuwa .
Taku a Kullum Khadeejaht.

🐎🐎🐎🐎🐎🐎🐎?
Royal Blood Typing
🐎🐎🐎🐎🐎🐎🐎🐎

UQUBAR UWAR MIJINAWhere stories live. Discover now