Part 8/9

396 27 0
                                    

🐎🐎🐎🐎🐎🐎🐎🐎
🐲🐲🐲
         UQUBAR UWAR MIJINA
🐲🐲🐲
(Based on true life story) (full of sorrow)

Story Nd Written By
Khadeejaht Hydar
Young Novelist

Dedicated to  Granny May Allah s.w.t Continue to shower his mercy nd glory upun ur grief.I miss u Granny.Aliyu Muhammad Arab.Za Royal Hignezz.

This story is not dah Long so just Bear wit me,I saw ur msges fans tnx a lot,Alhamduliilah group dinmu na fb Zama Na Amana ya gyaru don haka aci gaba da gashi,kuna comment ina binku da ruwan typing loll.Tnx once again.

(8)&(9)
🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥
No matter how d circumstances,always Be prayerful.

Toh haka muka kwana raina ajagule donma mijina yana bani hak'uri da kwanciyar min da hankali, washe gari ma haka yafita  babu sallama se kud'i daya ajiye.

Alokacin ne nafara zargin kode girman laifin Dana masa ne yasa yake min hukunci batare da ya fad'aminba,amma nayi niyyar tunkararsa inya dawo yau.

Bayan nagama ayyukana da yamma nashirya cikin shadda pink mai kyau nayi kwalliya,bank'arasaba naji horn d'in motarsa bayan ya shigo namsa  sannu da zuwa.

Hak'ik'a kwalliya ta tamasa kyau amma ya kasa cewa nayi kyau ,ko ze fad'a se yaji kamar an hanasa,jiki a sanyaye nagabatarme da ruwa mai sanyi.

Bayan yasha na basa abinci har ya gama,bayan ya gama ne nak'ira sunansa dacewa Abban Ilham wai meke faruwa ne?.

Yace".....game dame ba,nace".....naga duk ka canza da safe saika fita batare da ka  nememu ba,ka dena kwana tare damu,kadaina cin abincina in laifi na maka kafad'amin se na gyara.

Kallona yayi na tsawon minti biyar amma ya kasa magana sema rungumeni da yayi ajikinsa still shiru,kamar kuma an tsikareshi saiya tashi da sauri yace".....nima bansan meke faruwa dani ba kinamin addu'a kawai."

Nace"...insha Allah zannayi maka addu'a kuma daman inayi."


To munkai wata uku a haka kullum abu sai dad'a gaba yake, babu sauk'i yanzu some times ma baya kwana a gida.

WATARANA Ranar da bazan tab'a mantawa a rayuwa taba,ranar da shima Khamis tazame masa ranar k'unci da duhu.


Zaune muke Bayan ya dawo daga inda yake Wanda seda ya kwashi kwana biyar tukun ya dawo,abinci yakeci muna fira don yau kam nagansa ba laifi.

Hannuna ya kama yace".....muje kitayani wanka nagaji yau fa,cikin jin dad'in ganin yafara dawowa yadda yake da nayi,da hanzarina na tashi  ina gaba yana bina abaya Ilham kuma tanagun Mama.

Bayan nataimaka masa munyi wanka,ya nemi ya raya sunnar manzo, wanka muka sake sannan muka shirya cikin kaya iri d'aya, kana ganinmu zakasan muna cikin farinciki.

Zama mukayi a parlour muna wasa,kawai se mukaji anbugo k'ofa da k'arfi,saurin sauka a jikinsa nayi ina gaidata.

Wani mugun kallo tabini dashi,sannan tace".....kai Khamisu yau base gobe ba,yanzu base anjuma ba kasaki yarinyarnan inba hakaba wallahi saina tsinemaka albarka."

Jiki na rawa yace"......Dan Allah Hajiya kiyimin rai kibarni da Matata,wani uban ashar ta yanko tace".... Allah ya......"


Da sauri yace".....Dan Allah kiyi hak'uri zan saketa karkimin baki,a hankali yakai dubansa kaina hawaye yakebin kumatuna."


Yace"....kiyi hak'uri Fatima ina sonki,nace".....bakomai Khamis nima ina sonka kabi umarnin Hajiya Allah yana tare dakai."


To in angama barikancin ina jira abarmin gidan d'ana,wucewa nayi ciki don d'akko hijabina,har ze bini tace"....ina zaka?,yace".....takarda da Biro zan d'akko,batayi magana ba illa kwafa datayi."


Hijab na d'auka ina hawaye,a bakin k'ofa mukayi karo dashi,rungumeni yayi ya fashe da kuka nima Inayi.

Yace".....banason rabuwa dake,nace".....dole mu rabu Khamis ka sakeni kar mama tayiwa rayuwarka illa,ni nayafemaka nasan ba'ason ranka bane.

A hankali yace".... Nasakeki saki d'aya, wani kuka ne y kufcemin a zuciyata nace"....daman haka saki yake,amma wasu matan sukeson asakesu.


Shigowa tayi tace"...kasa keta nace yanzunnan,yace"... Nasaketa tace"...wlh baka isaba saki uku zaka mata ba d'aya ko biyu ba."

Hankali a tashe yace"....Dan Allah Mama kiyi hak'uiri bazan iyaba,wani wawan mari takai masa tace"....kasaketa yanzu nace!!!,haka inaji inagani tarabani da Khamis yana kuka ina kuka yace ".....na sakeki saki uku amma kisani inasonki har k'arshen rayuwa ta."

Hannu ta tafa tace"....to Y'ar mayu se ki tattara kibarmin gidan d'ana na huta,Uhm da kinsan abun ba ita kad' ai ze shafa ba da baki rabasu ba.

Muje Zuwa fans.

Gida nakoma nasanar da iyayena,dukda sunji ba dad'i amma hakan be hanasu kwantar min da hankali ba,anan naci gaba da iddata Ilham na guna.

Bayan na gama idda ne aka kaiwa Khamis Y'ar sa,amma Mahaifiyarsa tace"....a maidota d'anta beda wata y'a.".

Haka aka maidota Wanda hakan yayi min dai-dai,saboda daman ina tunanin yadda zata rayu agunta cikin uquba da azaba.

Bayan nagama idda ne na koma gidan yayana,inda a wannan lokacin ne rayuwata ta tabarbare na koma wata kala kamar baniba,hankali kwata kwata baya jikina banma san wacece niba.kullum haka nake kamar wacce ake bawa umarni.

Bayan na barmata d'anta bata kyale niba taci gaba da bibiyar rayuwata saboda kawai burinta be wuce inta gayyaraba.

Aikin da tayi na k'arshe akaina gun wani malamine a nan garinmu,inda tasa yamin aikin da zan shiga duniya na ringa asarar,duk abinda nasakawa hannu ya lalace kuma inda k'arbar kud'in jama'a yana lalacewa aguna.

Uhm Wata shari'ar se lahira,,

Kuma gashi tamin asirin ko aure bazan sakeyiba.

A wannan lokacin ne na had'u da wani mutum Wanda me kud'i ne sosai,kuma ya nuna yana sona amma hakan besa nabasa fuska ba.

Ilham kuma tana gun Mama tana samun kulawa Alhamduliilah, Nikuma ina gun wani kawu na babu abinda nakeyi kawai naji unguwarmu ta fitarmin arai.

Muje zuwa

Ku kasance TARE DA YOUNG NOVELIST.

Vote.
Share.
Comment.

🐎🐎🐎🐎🐎🐎🐎🐎
ROYAL BLOOD TYPING
🐎🐎🐎🐎🐎🐎🐎🐎

Alk'alamin Auta.

Ku biyoni don jin sabuwar rayuwar FATEEMA BAIWAR ALLAH.

Allah ka karemu daga sharrin duk abin k'i,Amin S Amin.

Pray 4 me Am sick,just type 4 ur calls nd msge

UQUBAR UWAR MIJINAWhere stories live. Discover now