Part 2/3

632 45 0
                                    

🐲🐲🐲
HUQUBAR UWAR MIJINA
🐲🐲🐲
(Based on true life story) (full of sorrow)

Story Nd Written By
Khadeejaht Hydar
Young Novelist

✍✍✍✍✍✍✍✍
GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION
✍✍✍✍✍✍✍✍

❄We are bearers of soo golden a pen, we write assiduously perceive no pain so magical our creative golden pen, be hold our words, A product of our pen savour our words for it will cause u no pain❄

Dedicated to
Abdallah Ibrahim
Tnx 4 everything.

(2)&(3)
To bana zuwa ko'ina daga makarantar islamiyya se gida,niko irin bikinnan ma bana zuwa.

Toh akwia wani saurayi a layinmu mai suna Khamis,tunba yau ba yanuna yana sona amma nak'i amincewa dashi saboda maganganun danakeji akan mahaifiyarsa.

Wata rana na dawo daga islamiyya ina tafiya cikeda nutsuwa ina maimaita hadda ta,kawai sainaga mutum a gabana.

Fuska na d'aure nace"....Malam lafiya ina tafiya zakana taremin hanya, se yace"...wlh yau ko marina zakiyi sekinmin magana."

Ganin yak'i bani hanya nawuce ga hankalin mutane yafara zuwa kanmu yasa nace"....yanzu me kakeso ?,yace"....yauwa so nake kibani numbarki."

Nace"...a gaskiya banda waya,saboda lokacin banda waya Sam banda ra'ayinta,yace"...tunda bakida waya kibani izinin zuwa gunki anjuma."

Dakyar na amince masa tukun yabani hanya nawuce,ina zuwa gida nayi ayyukana na kwanta.

Se bayan la'asar na farka da sauri na s'auka naje nayo alwala nayi sallah,daganan kuma nafara karatu har magrib tazo.

Bayan isha'i muna zaune a parlour akace ana sallama dani,abin mamaki tabawa su Mama wai yaushe nafara kula samari amma basuyi maganaba.

Hijab nasaka nafito waje,yana zaune akan wani dakali a k'ofar gidanmu, da sallama na k'arasa gun na zauna d'an nesa dashi tare da gaidashi.

Bayan mungaisa yace"....wato Fatima abinda nake shirin fad'amiki ba zancen wasa bane,Fatima tun ranarda naganki naji na kamu da sonki dafatan zakiyi na'am da zancena."

A hankali nace"...nagode da nuna soyayyarka agareni amma....,bank'arasa magana ba yace".....kinason kice matsalar Mahaifiyata ko?,to wallahi ta amincemin inhar ke zan aura."

Nace".....to shikenan Allah ya tabbatar da alkhairi nace"...Amin ngd,haba Fatima ai nine da godiya."

Kud'i yabani amma fur nak'i karba saida yace"...wato kinraina abinda nabaki ko to Allah yabani nabaki masu yawa,jin haka ne yasa na karb'i kud'in namasa godiya nashige gida."

Mama kawai na tarar a parlour nan nafad'a mata yadda mukayi dashi,Mama tace"..to Allah ya tabbatar da Alkhairi kuma kici gaba da Addu'a."

D'aki na shige nayi alwala na kwanta,kamar yadda Manzon Allah (s.a.w)yace"..... Duk wanda ya kwanta da Alwala ko macece wacce batada tsarki zata iya alwala to mala'ikun Allah zasu na nema masa gafara gun Allah harse gari ya waye.

Allah yasa mu dace Amiiin.

Toh magana ta kankama tsakanina da Khamis kuma tunda muke bantaba zuwa gidansu wai gaida mahaifiyarsaba,uhm Mata kuyi hattara gun zuwa gaida iyayen miji na farko bai kamataba na biyu wani zece muje ki gaida mamata ko saboda ansaka muku rana muje kiga gidan dazaki zauna,uhm Y'ar uwa ki gujema kanki asara.

A kwai wata yarinya saurayin da ankusa d'aura musu aure yazo har gun iyayenta wai yarinyar tazo suje ganin inda ya kama,Toh iyaye ganin aii yakawo komai se suka yarje masa,da'ita da k'awarta sukaje basu San hanyar dayabi ba.

Bayan sunje har zasu tafi seyacema yarinyar wai taje ta d'akko sak'o a d'aki bata kawo komai ba tashiga,dashigarta sai ya nuna mata bindiga ta kwanta yasaka maciji yashiga yafita ajikinta.

Yasakasu a mota suka koma toh yarinyar a hanya ta rasu, Ashe ta fad'awa kawarta meya faru,Apart from that namiji na'iya yaudarraka yasanka a matsayin y'a mace yana saninki zai fasa aurenki tunda dama abinda yakeso kenan.

Toh Iyaye mata da y'emmata ayi hattara,wata rana kema uwace yanzu ilimin Addini ya yawaita mukare mutuncinmu da darajarmu

ALLHA YA KAREMU DAGA DUKKAN SHARRI.

Manya sun shiga lamarinmu har ansaka rana,wata uku aka sa,don haka tuni anfara shirye-shirye saboda zasu aurar da Y'ar su d'aya tilo.

Nikuma nafarko na'a minta da Khamis ne saboda kowa ya masa shaidar kirki a unguwar kuma nima shaidace,kuma yana da sana'arsa Masha Allah.

Ga yacemin mahaifiyarsa ta amince,kuma dama itace matsalata.


A sati sau uku yake zuwa fira saboda amfanin fira dayawa babu kyau,K'ira ga emmata Kada ki yarda mutum yana zuwa gurunki har nawani tsawon lokaci mai mike maganar aure ba kuma shi be bari kin saurari wani ba kawai yana b'ata miki lokaci a banza,daga k'arshema yak'i aurenki.

ALLAH YA KYAUTA.

To yau saura wata d'aya biki,kuma ayau aka Kawo lefe ba laifi kaya sunyi.

Kuma an musu tarba mai kyau,dukda ni ba gwanar kwalliya bace haka nad'anyi kad'an naje don gaida surukaina,Bayan mun gaisa na zauna shiru wata acikin su tace"...ah lalle amaryartamu mai kunya ce wata tace"...yo ai ta shafi Fulani."

Sallama na musu na koma ciki ina yaba kirkinsu,Toh Fatee Allah yasa hakane.

Vote.
Share.
Comment.
Like.

🐎🐎🐎🐎🐎🐎🐎🐎
Royal blood typing
🐎🐎🐎🐎🐎🐎🐎🐎

Chocolate,Milk Lover.

UQUBAR UWAR MIJINAWhere stories live. Discover now