YARINYAR CE TAYI MIN FYADE

By miss_untichlobanty

155K 10K 1.8K

WANNAN LABARI NE DA WASU BANGARE YA FARU A GASKE. BAN CANJA SHEKARUN YARINYAR BA KO ALAKA BA,AMMA NA CANJA S... More

CHAPTER 1
CHAPTER 2
CHAPTER 3
CHAPTER 4
CHAPTER 5
CHAPTER 6
CHAPTER 7
CHAPTER 8
CHAPTER 9
CHAPTER 10
CHAPTER 11
CHAPTER 12
CHAPTER 13
CHAPTER 14
CHAPTER 15
CHAPTER 16
CHAPTER 17
CHAPTER 18
CHAPTER 19
CHAPTER 21
CHAPTER 22
CHAPTER 23
CHAPTER 24
CHAPTER 25
CHAPTER 26
CHAPTER 27
CHAPTER 28
QUESTIONS AND ANSWERS
CHAPTER 29
CHAPTER 30
CHAPTER 31
CHAPTER 32
CHAPTER 33
CHAPTER 34
CHAPTER 35
CHAPTER 36
CHAPTER 37
(FINAL)CHAPTER 38
AKWAI KURA

CHAPTER 20

3.4K 227 60
By miss_untichlobanty

AishaIsmail625 , aysherahmaddanlami,  wannan shafin naku ne Allah yabar kauna

ALIYU'S POV

Bayan na fito masallati ne nayi ma luba message saboda dazu naga kiranta ina tare da ladidi kamin na shige masallati ina fitowa kiranta ya shigo ina dagawa cikin murmushi zan tsokaneta Dan na dauka ma hakuri zata bani na kuskuren sa tayi sannan tamin godiya na gyaran da nasa akayi Mata banci mutunci ta gaban ladidi ba kawai sai naji sabanin haka.

Ta inda take shiga ba tanan take fita ba Abu kamar wasa sai na bude baki zanyi magana sai naji ta daura magana. Jikina ne yayi sanyi Dan ban kyauta Mata ba amma ni ba da wata niya nayi ba banaso naci mutuncinta gaban ladidi yasa na gasata da aunty maryam tayi Mata magana ta Mata toh menene kuma na duka.

Tunani na ya datse sanda tace ta fasa auren kuma zata bawa me gadi dama a raina nace masha Allah dama nasan yarinta ke damunta.... amma dakata! Ta fasa aure na saboda me gadi? Me take nufi wato ya fini ko me ? Toh dukda banason ta saina AURETA ba ita uwar taurin kai ba? Ko me akayi in bataso ta tada bori? Toh AI in tasan wata batasan wata ba zan AURETA dan in kure taurin kan muga abinda zatayi.

Kiran wayar nayi taki ta daga daga baya ma naji switched off. Gida na shiga abina ina shirya bomb din da zan Mata Dan jira zanyi ladidi ta Dan shekara sai nasa luba ma daga ciki.

Ya Allah ka jarabce ni da rasa Mata na nayi kuma karbi kaddarata ya Allah na rokeka saboda tawakkalin da nayi kar ka kashemin wadannan kar ka rabani dasu. Shafawa nayi kamin nabar kofan masallatin.

LUBA'S POV

Ummi na samu nace Mata ummi nifa wallahi azo a sake zama na fasa auren uncle aliyu bige min baki tayi tace sannu shashasha kawai Dan yabaki haushi sai akace ki fasa aure? Haka zakiyi bayan auren da an bata miki rai kice sake ki? Zama nayi a kasa Wanda ummi tasan abinda zai biyo shine bori tace toh karma ki fara kinga yanzu SS3 kike ki rufe ido kiyi karatu kina gamawa lokacin kin kusa shekaru 17 ayi miki aurenki.

Bori na fara nifa Allah in aliyu za a aurenin yasin ko karatun bazaiyi ba. Ummi tace subhanallah yau ko uncle din babu ? Kuma da kike batun bazakiyi karatu ba wa jahilci zai kashe ? Ki auri aliyun ki a gidansa sai kiyi university ko ya kikace. Mikewa nayi nace toh ai sai muga yadda zan aureshi ni dama can nasan ba sona ake a gidannan ba. A fito a fadamin ko tsintata akayi yasa za'amin auren dole.

Bulala ummi ta dauko ta biyoni zonan yar banza in dauki cikinki wata 9 harda sati 2 awanni 13 nayi ina nakudar ki shine zakice tsintar ki akayi toh sai kin auri aliyun tukunna ma in baki aureshi ba wa zaki aura? Manna Mata nayi ta bankado labulen dakina ta shigo.... Luna wai meke damunki ne? meyasa kikeson bamu ciwon kai? Me yasa kikeson maida daddynki karamin mutum?

Maganarnan an gamata ke da kanki kikace a aura miki aliyu yanzu kice kin fasa? Ki bari idan kin huce ki sake tunani... turo baki nayi nace nide acewa abba na na fasa. Toh ai shikenan. Abinda ta fada kenan kamin ta sauke ajiyar zuciya ta fice.
Da daddare ummi ta samu daddy ta fada masa kamin ta karashe ya daga Mata hannu yace kiramin yarinyar. Kwala min Kira tayi na shigo parlourn ina wani mika da hamma daddy yace in baki warware ba zan ware ki da Mari tsam na mutsu na zauna yace wani shiririta nakeji wai kin fasa aure?

Nace nifa daddy ba aure na fasa ba uncle aliyun ne banaso! Ke dalla rufemin baki lokacin da mukayi justin duniya ki hakura burus kikayi mana kikace sai shi yanzu kuma kina wani magana da batada kan gado? Toh bari kiji gara ki sani aure ba fashi. Kuma in bakida hankali ki kawomin kasa da credit shida gidannan saina ballaki.

Mikewa nayi na koma daki ina fadin zakusha mamaki, sannan na fada kan gado na sai bacci.

Washe gari da asuba ummi ta tashi zata tasheni sallar asuba taga empty! Ban daki ko ina ta duba babu ni babu alamata sai ta dauka ko zuciya nayi na tafi gidan aunty maryam toh amma da asuba kuma? Daddy na ta fadawa aka Kira su aunty maryam sukace banzo ba.

Uncle Aliyu aka kira shima yace bai ganni ba nan cikinsu ya duri ruwa aka fara cigiya ta a unguwa amma babu alamata.

Abinda ya faru kuwa shine tun da magrib ina waya da nana nake fada Mata nifa idan aka ki yarda guduwa zanyi tace yayi mutuniyata toh amma in kin gudu ina zakije? Nace nima ban sani ba. Maama tace toh me zai hana tazo nan ba tare da sanin kowa ba sai musa ta a BQ ko ya kukace mu dinga bata su abinci daga nan.

Nace toh amma masu gadi zasu fada ai nana tace karki damu zan rufe musu baki aiko tunda daddyna bai yadda ba karfe uku nayi sneaking dama already nana ta sanar da masu gadi zuwa na Dan haka suka budemin kofa.
Inaji da safe anata cigiya na dan video call muke da  su nana ina ganin komai.

Zama aka Kira da azahar na yadda za'a soma nemana Allah sarki har sun bani tausayi amma nasha alwashin idan ba auren aka fasa ba bazan fito ba. Gidajen radio da talabijin duk an watsa amma shiru babu labarina. Ladidi ko abin ya Mata dadi amma sai ta nuna tafi kowa damuwa. Harkuka tayi anata bata hakuri ummi ma tasha kuka tace ma daddy na asanar cewa an fasa auren kila na dawo.

Yace Sam ba'ayi haka ba idan naji ba haza San dawo gida shirme nake yunwa ma kadai ya isheni ummi tace toh AI garin neman kudin abinci in na fada wani hali fa gashi dama ba hankali gareni ba? Yace a bari nan da sati sai ayi sanarwan.

Su nana kullum tsakar dare suke kawomin ziyara musha hira kuma Allah cikin ikonsa babu wadda ya taba tsammanin ina gidan kamar wasa har sati daya yayi Dan haka yau abbana suka shirya suka tafi gidan yasa labarai... basusha wahala ba aka basu Dama domin yin magana.

Daddy na yace assalamu alaikum! Nine mahaifin yarinyar nan lubabatu da akayi sanarwa satin daya gaba ta cewa ta bata... luba diyar albarka idan kina jin mu yanzu haka ki dawo gida mun janye batunnan mun fasa. Aliyu ma ya bada nasa jawabin cewa ya fasa Niko tabe baki nayi nace sai bayan kwana biyu zan fito.

Haka sukayi ta zuba ido suna neman ranta inda zan billo amm shiru. Washe gari ma haka abin ya fara daga musu hankali sosai toh kode na mutu ne? Da daddare ne su nana suka hadani da Allah cewa na fito kullum sai ummi tayi kuka kawai sai na yanke shawarar zan fito gobe.

Washe gari ummi na rashi da safe ta leka daki na yadda ta Saba dukda bata tsammaci gani na ba ta ganni nayi wannan wawar kwanciyan nawa a da kullum make ni take amma yau cikin jin dadi ta rungume ni tana sumbatar goshina. Allah sarki diyata ta dawo lubabatu na uwata in kika shiga umminki tayi kewarki.

Kureta nayi da ido Dan ta bani tausayi har ta rame nace ummi na kiyi hakuri na saki damuwa amma babu yadda na iya ne sanda nace muku banason auren kuka dage sai anyi. Tace karki damu an fasa kiyi karatun ki kinji? Toh nace mika sha kuka.

Aka fada wa su aunty maryam an sameni aiko shikenan ban karajin anyi batun auren ba har lokacin WAEC dinmu yayi. A dakin jarabawa ne naji wasu dalibai na hira ta fari tace nifa wallahi ko da aunty kaltume ta rasu naso ni aka aura wa mijin ta gaskiya aliyun nan ya hadu. Ta biyu ne tace nikam kullum sai kin mana zancen aliyunnan amma ko saninshi bamuyi ba ta fari tace aliyu mukhtar fa!  Ta uku tace wanne shi kenan? Ta biyu tace me me Ablimuk plaza ? Ta farin tace shidai.

Ta biyun tace wow gaskiya nima naji ance gayen ya hadu ta ukun tace nikam ban sanshi ba. Ta biyun tace dama ance miki shugaban kasa ne da kowa sai ya sanshi? Mtsww ta ukun tace kanku akeji toh dukda ban sanshi ba toh yamin kuma zan Nemo bayani akansa. Ta farkon tace sannu Sara me bakar tak*shi  Sato dan ubanki ya fi namu kudi shine zaki wani ce ya miki zaki kwata? Ta biyun tace ku da kuke hauka bakusan matansa 2 ba ? AI daddy naji yana cewa matansa biyu amma dayan na sirri ne. Kinsan daddy na aminin yayansa ne.

Ta farkon tace ince wancan lubar ance ta sansa? Yayar mamanta ke auren yayansa? Ta biyun tace kwarai nima naji hakan toh mu tambayeta mana. Ta uku tace yarinyar dake da shegen fi'ili ga reni cab a dawo lafiya. Wajena suka zo suka ce sannunki luba.... take na musu nace sannunku. Sukace wai da gaske kinsan Aliyu mukhtar? Nace na sanshi amma munyi fada ban kulashi Dan haka inma sako me daku bazan iya kaiwa ba.

Sukace haba yar uwa toh ko numbarshi kya bamu AI ko hannu na mika alamun abani littafi suka miko min hannunsu Niko na rubuta na cire numbar karshe nace su nemi wannan da kansu. Daidai lokacin aka kawo papers Dan haka babu halin magana.

ALIYU'S POV

Ya ABBA ne ya tisa ni a gaba yace toh aliyu ga luba fa kaga yadda ta kafe yanzu ya kake tunanin za'ayi?  Kaga de har gida ta bari akan kar ta aureka an tambayeta inda ta zauna ma tace bazata fada ba kar a kuma cewa za'ayi auren ta rasa wajen buya wadda ke nuna in aka sake takura Mata zata gudu kuma dai kasan matsayinta.

Ajiyan zuciya na sauke nace AI ya ABBA kuma kunyi gaggawa bai dace sanda takai shekara goma tace ta yarda ayi auren kuka daura a lokacin ba da kun bari ko zuwa yanzu kunga ko ta fasa ba matsala. Uncle ABBA yace toh ka saketa mana tunda bata ma San da auren ba! Nace kai gaskiya bazan iya ba ni bansan yadda zanyi da ita in tazo gidan sai in sanar da ita.  Ya ABBA yace toh kadai yi a hankali kasan kamar me aljanu kar mu sake nemanta mu rasa!

😳TOH FA NAJI WANI LABARI KO KUNNE NA NE?💃🏻💃🏻 TOH BARI NA TAKA RAWA ASHE LUBAR MU MATAR ALIYUN CE MA TOH YANZU DE YA ZA AYI TA YARDA TAJE GIDAN?

KU BIYONI A NEXT CHAPTER DANJIN YADDA ZA'A KAI LUBA A DABARA, SHI IN ANKAITA ZATA ZAUNA KO ZATA ARCE?

IN KUNYI COMMENTS DAYAWA IN BAKU UPDATE IN NAJI SHIRU KUWA TOH SHIKENAN NIMA ZAKUJI SHIRU😉

TAKUCE KARAMARSU BABBARSU WATO

Miss untichlobanty 💕

23rd June,2020.

Continue Reading

You'll Also Like

104K 4.4K 30
Labari ne akan 'yan mata 3 wad'anda suka sha gwagwarmayar duniya suka ga bala'i a rayuwar su kala-kala, labarin ya gino ne akan makirci, yaudara, cin...
2.8M 185K 89
What will happen when an innocent girl gets trapped in the clutches of a devil mafia? This is the story of Rishabh and Anokhi. Anokhi's life is as...
3.4M 143K 60
The story of Abeer Singh Rathore and Chandni Sharma continue.............. when Destiny bond two strangers in holy bond accidentally ❣️ Cover credit...
1.1M 27.5K 45
When young Diovanna is framed for something she didn't do and is sent off to a "boarding school" she feels abandoned and betrayed. But one thing was...