KUNDIN QADDARATA

By huguma

1.4M 117K 19.1K

Kalmar QADDARA kalma ce dake rataye bisa wuyan kowanne bawa,haka rayuwa ta gada,tafe take da QADDARORI kala k... More

Babi na daya
Babi na biyu.
Babi na uku
Babi na hudu
Babi na biyar
Babi na shida
Babi na bakwai
Babi na takwas
kundin qaddarata
Babi na tara
Babi na goma
Babi na goma sha daya
Babi na goma sha biyu
Babi na goma sha uku
Babi na goma sha hudu
Babi na goma sha biyar
Babi na goma sha shida
Babi na goma sha bakwai
Babi na goma sha takwas
Babi na goma sha tara
Babi na ashirin
Babi na ashirin da d'aya
Babi na ashirin da biyu
Babi na ashirin da uku
Babi na ashirin da hudu
Babi na ashirin da biyar
Babi na ashirin da shida
Babi na ashirin da bakwai
Babi na ashirin da takwas
Babi na ashirin da tara
Babi na talatin
Babi na talatin da d'aya
Babi na talatin da biyu
Babi na talatin da uku
Babi na talatin da hudu
Babi na talatin da biyar
Babi na talatin da shida
Babi na talatin da bakwai
Babi na talatin da takwas
Babi na arba'in
Babi na arba'in da daya
Babi na arba'in da biyu
Babi na arba'in da uku
Babi na arba'in da hudu
Babi na arba'in da biyar
Babi na arba'in da shida
Babi na arba'in da bakwai
Babi na arba'in da takwas
Babi na arba'in da tara
Babi na hamsin
Babi na hamsin da daya
Babi na hamsin da uku
Babi na hamsin da uku
Babi na hamsin da uku
Babi na hamsin da hudu
Babi na hamsin da biyar
Babi na hamsin da shida
Babi na hamsin da bakwai
Babi na hamsin da takwas
Babi na hamsin da tara
Babi na sittin
Babi na sittin da daya
Babi na sittin da biyu
Babi na sittin da uku
Babi na sittin da hudu
Babi na sittin da biyar
Babi na sittin da shida
Babi na sittin da shida
Babi na sittin da takwas
Babi na sittin da tara
Babi na sittin da tara
Babi na saba'in
Babi na saba'in da daya
Babi na saba'in da biyu
Babi na saba'in da uku
Babi na saba'in da hudu
Babi na saba'in da biyar
Babi na saba'in da shida
Babi na saba'in da bakwai
Babi na saba'in da tara
Babi na tamanin
Babi na tamanin da daya
Babi na tamanin da biyu
Babi na tamanin da hudu
Babi na tamanin da uku
Babi na tamanin da biyar
Babi na tamanin da shida
Babi na tamanin da bakwai
Babi na tamanin da takwas
Babi na casa'in
Babi na casa'in da daya
Babi na casa'in da biyu
Babi na casa'in da uku
Babi na casa'in da hudu
Babi na casa'in da biyar
Babi na casa'in da shida
Babi na casa'in da bakwai
Babi na casa'in da takwas
Babi na casa'in da tara
Babi na d'ari
Babi na dari da d'aya
Babi na dari da biyu
Babi na d'ari da uku
Babi na dari da hudu
Babi na dari da biyar
Babi na dari da shida
Babi na dari da bakwai
kundin qaddara
KUNDIN KADDARATA

Babi na tamanin da tara

16.9K 1.4K 353
By huguma

*Bismillahir rahmanir rahim*

La haula wala quwwata illa billahil aliyyul azim

La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin

ADDU'A CE GA DUK WANDA YA SHIGE CIKIN QUNCI

_____________________________________



        Ci gaba tayi da tunkararsu ba tare data dauke idonta daga garesu ba,tamkar zuciyarta zata fito waje saboda tsananin kishi,kamar ta kurma ihu ko zata ji sauqin abinda ke sukar zuciyarta,bata taba jin bala'i irin wannan ba arayuwarta,ashe a baya duka qaryar kishi take kan almustapha?,almustaphan nata ne riqe da hannun wata haka?,sun kuma jero suna tafiya kan bigire guda?,ko a jikinsa wai an mintsini kakkausa,shi sam baiyi zaton ganinta ba ma a wannan lokaci,sai da suka qaraso dab da juna sannan ya zame hannunshi daga na sumayyan ya dubeta
"Idan kika shiga bana so ki fito,bana son yawo ki zauna waje guda,nasan duka nan za'a dawo akwai walima da zasuyi" sai ta samu kanta da narke masa cikin wani irin salo
"Ina so naje wajen umman khalipha fa,tunda nazo ban shiga ba" girarsa ya dage salon ya matuqar qayatar da shi
"Ko zakin ba yanzu ba,idan na dawo zan sanar miki" kai ta gyada tana jifanshi da wani irin qayataccen murmushi daya sake narkar da shi
"Ok,to a dawo lafiya,Allah ya tsare hanya" idanu ya lumshe addh'a ta masa dadi,qarakin murmushi ya subuce masa
"Amin,thanks" kai ta gyada tana juyawa cikin takunta na nutsuwa,baki daya idanuwa su'ad ta bita da shi,ji take kamar ta fincikota ta yarfa mata mari,ba'a tabacin fuskarta irin haka ba,a gabanta wata ke soyewa da mijinta?,ita dun da dukkan 'yammatan danginsa sunsan halinta sarai ko cikakken kallo bata so taga ka fiya masa yanzun zata ci miki mutunci?,saiga wata a gaban idanunta tana narkewa mijinta,ga sumayya kuwa sanda ta juya sai ta dinga jin wani abu na mintsininta cikin zuciya,sai taji kamar ta koma,me yasa ta barsu su biyun?,zuciyarta ta cunkushe,kallon data lura su'ad na mata bai dameta ba,qarfin gwiwar da bata taba jinsa kan kishiya ba wannan karon shi take ji,ba abinda zai sanyata taci gaba da barwa wasu matan mazanta,ta tabbata ko ba'a gaya mata ba babu zancan zaman arziqi tsakaninta da su'ad,ta santa tun ba yau ba,ta santa tun kafin miji ya hadasu,bata da kirki bata da mutunci,bata ganin girman kowa,a haka taci gaba da takawa zuciyarta dake cike da kishi na bata shawarar ta waiwaya amma ta daure zuciyarta ta hana kanta aiwatar da hakan.

      Yatsan tsakiyarsa da babban yatsanta ya hada ya murza a fuskar su'ad din wadda tabi sumayya da kallo,kishi ke sukarta,sam bata gane ma sumayyan ba,saboda ba duka wanda yayi mata qaramin sani irin wanda su'ad din tayi mata bane zai iya tantanceta ba tashi guda,idanunta da suka kada ta dauke ta maida kan almustapha,shigar jikinsa kadai ta bata mamaki,bata taba ganinsa da manyan kaya ba tunda suke sai yau din,wani qyama da takaici ya kamata,ya auri 'yar nijeria arewa ta fara zuba masa duhun kai kenan,to wallahi bazata lamunta ba,wata babbar riga harda hula sai kace wani limami,bakinta na rawa cike da tsantsar kishi tace
"Almustapha?,ashe da gaske baka sona?" Shanyayyun idanunshin nan kawai ya zuba mata yana dubanta
"Almustapha ka dubi yadda kake nuna qauna da kulawa ga wata bayan ni,dama zaka iya aikata hakan?" Ci gaba yayi kawai da dubanta,karon farko da ya soma ganin aibun irin shigar da takeyi,cikin qasarsa gidansu kuma gidan iyayensa surukai a garesu,ba shakka ta nan shine babban mai laifi,amma sam bai gane illar hakan bane sai yanzu,tunu hawaye ya soma wanke mata fuska,sai ya saki hannayenshi ya sake matsowa inda take ya kama hannayenta,ya sani qwarai kishi abu ne mai zafi cikin zuciya,abu daya ne wanda zai janyo mata ta rasa dukkan wata dama daga gareshi shine taci gaba da hauka da tashin hankali
"Enought.....daga gani na sai kuka,ya isa" wani ratsawa wadan nan taqaitattun kalaman sukayi har cikin zuciyarta,sai kawai ta fada jikinsa rungumeshi tana sake sakin kukan,hakan bai dace ba saboda suna tsakar filin gidan,kowa ma na iya ganinsu a haka,dagata yayi daga jikinsa yana fadin
"Zan wuce ne wajen daurin aure kada na makara,ki koma ciki,but ki sauya kayan jikinki kafin na dawo zuwa atamfa lace ko shadda,coz akwai maza da zasu shigo da yawa bayan dawowar tamu bana son kowa ya sake zuwa ya ganki da wannan shigar,ya kamata ta zama tsakamin ke da ni ne kawai cikin gida,understand?"mamaki ya kusa kasheta,bai taba furta mata makamanciyar wannan maganar ba sai yau,me yake son maida ta ne,irin kidahumar matarsa?,taga sarai shigar jikinta,ta nannade kanta da wani material kamar gawa ba wajen shan iska,itakam ba zata iya ba
"sai na dawo ko?" Bata saba yi masa a dawo lafiya ba ko wata addu'a tun da can ma da ake zaman dadi bare yanzu,saboda haka har ya juya ya koma wajen motarsa driver ya bude masa ya shiga suka fice tana tsaye wajen,ashariya ta lailayo ta qunduma cikin harshen nasara,tana jin nemawa kanta 'yanci ya zama dole,ba zata taba lamunta ta zauna cikin irin wannan rayuwar ba,da wannan tunanin ta tattaka cikin sassarfa ta wuce nasu bangaren.

        Wajen anty maamaa ta soma shiga ta gaidata,suja gaisa da dukka 'yan uwanta a mutunce ta musu Allah ya sanya alkhairi,cikin farinciki tare da yabawa suke amsawa,lokaci daya ta burgesu ta shiga ransh,don babu wanda su'ad ta taba duba da irin wannan sigar tsawon saninsu da ita,ta dan kashe wasu mintina masu dama kamin ta wuce wajen ummee.

         Dukka 'yammatan yau na falonta,amira uwar daba na cikinsu anata sabga,tsokanarta suka shiga yi har ta rasa na karewa,amiran tace
"Ku dubarmin wannan mata,daga dawowar miji saiki tattara ki bishi,wai ku don Allah baku gajiya da zaman hotel?" Duka kan cinyarta sumayyan ta kai mata
"Baki da kunya fa,nu yayarki ce ko kin manta?"
"Tuba nake,Allah ya ja da ran babbar yaya" dariya duka suka saka,barkwancinsu abin sha'awa ne da burgewa,ta gaisa da kowa cikin fara'a da mutuntawa,eesha dake zaune tun shigiwar sumayyan gaba daya sauran fara'ar da tayi rara a fuskarta ta bace bat,kusan a wannan bigiren tafi kishin sumayya fiye da su'ad,saboda su'ad din kusan bata da wani amfani ko tasiri mai yawa cikin zuciya da rayuwar almustapha,babban abin tashinbhankali kuwa data gano wasu sabbin sauyi da halaye da duka almustaphan ua qaro matuqar yana tare da sumayya,itama eeshan bata dameta,ita a yadda taje ji yanzu ko kishiya bazata bari ta dameta ba,balle wata wadda batasan me ya hadata da uta ba,abinda ta sani dai kawai eeshan nada izza izgilanci da jin kai,tun daga sanda tazo gidansu a kano tun bikin amira,ita kuwa a rayuwarta zata iya mu'a mala da kowa tayi haquri da shi banda mutum mai wadan nan halayen,don bata ga abinda zara nuna mata ba,mutunci da rufin asiri dai dai bakin gwargwado Allah ya basu,to kuma name zata zubda mutunctakarta ta dan adam kota yarda a zubda mata?,amiran ita ta miqe don raka sumayyan sama wajen ummee,suna haurawa saman ta dubeta
"Kinsan wajen ummee mijinki ya gaji halinshi,miskilancin tsiya rashin son hayaniya,daga wajen anty mamaa fa ta dawo wai kanta ke ciwo tana daki kwance" harara ta watsawa amira
"Eh kam su ai sun huta,ba irinku ba akun kuturu" baki amira ta riqe
"Iyeee,wai yau ya man kike tarewa?"
"To ya ranki?" Ta fada tana juya idanu,suka sanya dariya baki daya,ran amira ya mata fes,burinsu ya cika,dangantakar da suke fatan ta qullu tsakanin sumayya da almustapha bisa dukkan alamu Allah ga qulla ta cikin ruwan sanyi.

       Knocking suka yi mata ta basu umarnin shigowa,amira ke gabasai sumayya,tana zaune a dakin ita da qannenta biyu da yayarta,idanunta kan sumayya fuskarta qunshe da fara'a,yayin da kunya ta yiwa sumayya katutu,don ta tabbata tasan ba gidan suka kwana ita da almustapha ba,a ladabce ta qarasa ta duqa tana gaidasu suka amsa a sake,nabila qanwar ummee wadda itama babba ce don tana da yara samari ke tsokanar sumayya
"Har yau baku kai mana ziyara kano ba,duk da dama wannan sarkin hade gabas da yamman sai sallah sallah yake zuwa mana,saidai ki jisu suna waya da mai martaba,da alama ma baisan jikinsa ya motsa ba bai gaya masa da tuni kin ganshi ya tashi hankalin kowa" dariya suka sanya ummee tace
"So nake kafin ya koma i yayi qoqari ya kaisu baki daya ita da su'ad din,don ita dinma dudud zuwanta nawa?"
"A'ah kibar ta wannan,itakam tunda baquwa ce sai ya kaitan,idan tana da sha'awa da kanta zata ko tasa ya kaita" inji hajiya saudat yayar ummee,hira suke kadan kadan kafin su fice don komawa bangaren anty mamaa,tsabar hadin kai da fahimtar juna ya sanya duk sanda wani abu ya taso cikin gidan walau na hajiya mamaa ne kona hajiya kilishi wato ummee 'yan uwan kowaccensj basa qasa a gwiwa wajen zuwa,run daga kan matasa yammata zuwa manya,akwai hadin kai da fahintar juna mai yawa tsakaminsu,kowanne family sunsan kowanne,haka 'yamnatan kowanne vangare na mu'amala dana kowa,kasanceqar duk sha'ani za'a hadu,sai duka suka zama kamar family daya.

       "Ina almustaphan ya shiga ne?" Akunyace ta amsa mata
"Ya wuce wajen daurin aure ne"
"To masha Allah" inji ummeen dadi yaja ratsata,
"Allah ya saka da alkhairi fa amiran umman khalipha,naji dadin yadda na fara ganin sauyi wajen almustapha,bama ni ba hatta da babansu,Allah ya qara miki juriya da qwarin gwiwa,naji labarin abokiyar zaman taki tazo,ina son inja hankalinki da don Allah kada ki biye mata da duk wautar da zata zo da shi,ki dauke kanki kiyi haquri da ita,idan kika fuskabci akwai abindabtake miki na cutarwa da ba zaki iya dauka ba,ki samu mijinku cikin salama ki sanar masa ya warware muku matsalar,kada ki soma yarda ki biye mata ku dinga abinda ba dai dai ba,kada ki yarda saboda ita ku dinga bata ran mijinku kinji"
"insha Allah ummee"
"Allah yayi miki albarja,ya akbarkaceku da zuriya dayyiba" addu'ar tayi mata nauyi,amira ce ta cafe
"Amin ummee,kai Allah dai ya nuna mana ranar,ummi da ido daya zaki bacci ina jin" ta fada cikin tsokana tana qyaqyata dariya,murmushi ya subucewa ummee
"Kinci gidanku,kin maidani kakarki ko?" Ta fada tana harararta,murmushi itama sumayya tayi,gwara da zancan ya tsaya nan kada ta hanata sukuni gaban ummeen.

       Bata jima ba ta wuce bangarenta,sanda ta shiga babu kowa falon,sai ta shige dakinta ta ware lafayar dake jikinta,kitchen ta wuce kai tsaye ta soma tunanin me zata dafa mishi?,don tuni ta sani wajen ummee baicin abincin taro idan ana yi,yankewa tayi tayi masa jallop din couse,sai ta tanada masa wani abun shan,shine zata gama cikin sauri kafin su shigo,cikin qanqanin lokaci ta hada komai ta dora.

        Cikin mintina ta kammala jallop din wadda ta wadata ta kayan lambu da kuma hanta wadatacciya a ciki,kammala komai tayi waje guda ta soma hada lemo,shima bai dauketa lokaci mai tsaho ba ta gama ta kammale komai waje daya ta soma gyara wajen.

         Cikin takun isa da izza ta shigo kitchen din,ta sauya kaya kamar yadda ya umarceta,a yanzun tana sanye da fitted gown na wanu lace mai azabar kyau da tsada,saidai bata daura dankwalin ba,sam sumayyan bata ji shigowarta ba,sai takun takalmanta masu tsini wanda ke haduwa da tiles din wajen suna bada wani sauti,a hankali ta waiwayo ta dubeta,sai ta dauke kai taci gaba da aikinta ganin ta shigo mata ne ba tare da sallama ba,bata tsaya ko ina ba sai data ci birki a gaban sumayyan wadda ke wanke sink data kammala amfani da shi,wani kallon sama da qasa ta yiwa sumayyan cike da tsantsar raini wanda sumayyan bata ma san tana yi ba bare ya dameta,aikin gabanta kawai take ci gaba da yi,itakam bata hango komai tattare da ita ba banda kyau da take da shi,sai tsantsar duhun kai,idan banda haka meye hadinta da daura zani?,meye na shiga kitchen tamkar matan daa?
"Ke" ta ambata cikin gatsali,sam bata nuna ta san da ita take ba,hakan ya quleta
"You african women dake nake" nan ma tayi banza da ita taci gaba da dauraye wajen tana gogewa da qaramin towel dake hannunta,hannu ta dora kan kafadar sumayyan ta juyo da ita suna fuskantar juna,murmushi sumayyan ta saki sannan ta dora hannunta saman na su'ad din ta saukeshi daga kafadarta tana fadin
"Sallama ya kamata ki soma kafin shigarki waje a matsayinki na diyar musulmi" ta juya taci gaba da aikinta,wani abu ya tsaya mata,itama za'a koyawa abinda ya dace
"Banga dama ba kuma bazanyi na,domin bani da shamaki cikin shiga duka inda naso a cikin gidan nan,gida dai na mijina ne so mallakata ne,ba wanda ya isa hanani shiga duk inda naso a sanda naso" waiwayowa tayi ta sake saki mata murmushi,mata na baki mamaki a yawancin lokuta,wato su duka son kansu ya musu yawa ne?,babu zaman lafiya idan su suka sameka cikin gidanka kamar yadda babu zaman lafiya idan kai ka tadda su,saidai zuwa yanzu ta tsike ya kamata itama ta shiga a dama da ita
"Oh sorry fa,may be labarin shafa fatihar dake tsakanin sumayya da almustapha bai isa kunnenki ba,idan kuwa har ya isa kunnenki to ya kamata kisam cewa nima matarsa ce kamar yadda kike matarsa,so kinga kenan matsayinmu daga,babu wanda nima zaimin shamakin shiga inda nakeso,saidai ni nawa addinin ya gayamin duk inda zan shiga na nemi izinin mai mallakin wajen kafim shigar tawa,wannan kadai shi zai sanyani neman izini bawai don nima ba matar doctor mustapha bace" kalamanta sunyi matuqar qona mata rai,ita take kallon idanuwanta take gaya mata cewa itama matar almustapha ce,sai ta gyara tsaiwa fuskarta na sauya launi saboda kishi
"Anzo point din,dama abinda nazo na baki shawara kenan a kai,ina mai baki shawarar sawunki a likkafa ki fita rayuwar mustapha,ki tattara ya naki ya naki ki koma gidan ubanki tun baki gamu da tuggun kishiya ba" abun ma sai yaso baiwa sumayya dariya,ta matse towel din data gama wankewa bayan ta gama goge gogenta ta dubu su'ad
"Ina zaton ke din farin shiga ce kan tuggun kishiya ko?,to mu ba yau muka fara gani ba,zagi kuwa ban tashi naga ana yi ba,don nasan makomar wanda ya zagi iyayen wani,shawara kuwa da kike ambata ai ciwo ce,baya ga haka ma kina iya riqe abarki wataqila nan gaba zata miki amfani" daga haka ta juya kan qafafunta ta soma takawa da niyyar barin kitchen din,zage zage su'ad din ta soma yi,tana son yayuaba baqa kamar yadda aka gaya mata saidai babu cikakkar hausa,hakan ya sanya ta dinga hadin gambiza da turanci
"Idan baki wasa ba nice ajalinki" shine kalmar qarshe data shiga kunnen sumayya yayin da take niyyar fita,hakan ya sanya ta waiwayo tana sake jifanta da murmushi
"Idan numfashina a hannunki yake yau kada na kwana a duniya" ta juya ta fice abinta,sam ko a jikinta,tasan sarai zata fuskanci sama da haka ma daga wajenta,saidai ba yau farau ba balle zuciyarta ta quntaya,meye ba'a yi mata ba?,har farautar rayuwar tata anyi.

       Toilet ta fada ta sake wanka,sannan ta shirya cikin atamfa plain zani da fitted riga,ta fuskancu shigar na yawan qawatar da almustapha,yakan yawaita binta da kallo duk sanda ta yita,tana tsaka da shafa mai bayan ta sanya kayan ta jiyo sallama,hakan ne ya sanyata fitowa daga dakinta ta ratsa ta corridor dinta ta fito falon,abida ce matar hamza,cikin farinciki ta tarbeta ta jata sukayi dakinta
"Wai wannan wawuyar ta dawo ne na sameta tana zirga zirga tsakanin falo da dakinta ta kasa zama" abidan ta fada sanda take shirin zama saman doguwar kujerar dake dakin,sumayyan na saman dressing chair tana kwalliya,baki sumayyan ta tabe kana ta saki murmushi
"Gata kuwa kin ganta"
"To Allah ya kyauta,sai ki sake zage damtse ki rungumi mijinki" dariya ma ta baiwa sumayyan har sai data dara,daga nan suka shiga hirarsu,tana gaya mata ai ta dan jima ma wajensu ummee,hamzan ne ya sauketa ya wuce wajen daurin aure su da lamin,ta nan zasu dawo idan an kammala daura auren.

         Bata fi minti talatin ba ta jiyo sallamarshi cikin muryarshi mai cike da izza da kwarjini,kamar wadda aka yiwa allura ta miqe,dariya abida ta saki sumayyan ta kalleta cikin dan jin nauyi don ta tabbatar qila yadda taga tayi saurin miqewan take wa dariya
"Mene ne" kai ta kada
"A'ah babu komai jeki abinki ina nan ina jira" ta fada tana miqewa saman kujerar,feshe jikinta ta sake yi da turare sannan ta fice.

        A hankali ta tura qofan dakin baccinsa dake sama cikin nutsuwa,idanunshi cikin nata bayan muryar su'ad da ta soma dukan dodon kunnenta,shike fuskantar qofa su'ad ta juya baya,magana take cikin bacin rai harda qwallarta a idanu,yayin da ya zuba hannunshi cikin aljihun wandon shaddarsa yana dubanta,tuni ya cire babbar rigar sai 'yar sama da dogon wando,baya ta koma a hankali da niyyar komawa tunda ta fuskanci wata magana suke wadda wala'alla abune da su'ad din bazata so taji ba,a hankali ya motsa baki har yau bai daina kallonta ba,ta masa kyau matuqa,komai nata mai nutsuwa ne da shiga cikin zuciya cikin wani irin sanyi
"Zo nan" ya kirata yana ci gaba da kafeta da idanu,maganan da yayi ya sanya su'ad yin shiru daga rattabo maganar da take yi,ta waiwaya a hankali idanunta kan sumayyan,bawinciki ya sake ninka mata fiye da na dazu,har wani canjin kwalliya take,ita har a nuna mata ado,gabanshi ta qaraso,kafin tace wani abu ya bata umarni
"Rage kayan jikina ki hadakin ruwa,ina sin yin wanka" idanu ta dan fiddo,ta yaya hakan zai kasance ga su'ad wajen na tsaye,yadda ya kafeta da idanu tasan zata jama kanta wani abunne hakan ya sanya ta nufeshi ta soma balle masa botiran gaban rigarshi cikin taushi da sanyi,idanunsa ya dauke daga kan sumayyan ya mayar kan su'ad
"Uhmmmm,ci gaba ina jinki,na taho da jama'a na jira na" kai ta kada tana yunqurin danne hawayenta don kada sumayya ta ganta bare ta rainata,ta sani sarai tunda har ranshi ya baci sai ya horata,koda zata ciyo kansa to sai ya hukuntata,wanda bai iya hukunci ta dadin rai ba,idan ya maka sai kaji babu dadi
"Ka barshi kawai,idan ka dawo mayi maganar"
"Ke kika tada maganan yanzu kk?,bayan na gaya miki cewa ki barta sai na nutsu,ki qarasa kawai idan ba gaka ba daga wannan muhallin banson na sake jin komai daga gareki,idan na dawo zan ganku ne kawai baki daya ina fata kin fahimta" ita kanta tasan indai har zaman lafiya take so da mustaphan to ta bar maganan,ta yarda ya gabatar da su wa juna,idan yaso ta ruwan sanyi zata dafa yarinyar,zata ga barikanvi,zata ganar da ita rainin america ba irin na nijeria bane,zata nuna mata akwai banbanci,za kuma ta nuna mata almustapha nata ne iya daya da ita kadai ya dace.

Busy busy,need ur prayers,we shall meet tomorrow in sha Allah.

#mrs muhammad ce

Continue Reading

You'll Also Like

771K 17.2K 38
Amy is Elena Gilbert's older half sister. She left to live with her Uncle John after the accident at Wickery bridge, when her parents died. Now her U...
3.9K 73 51
Be tashi ya ga mace a gidan su ba, rayuwar su gaba ɗayan babu mata idan kaga mace a gidan to auro ga akayi har shiyasa mutanen unguwa suke musu laƙab...
35.8K 2.5K 20
'yan biyu ne masu tsananin kama ďaya masu mabambanta halaye. Maryam ta kasance miskila marar ďaukar raini, yayinda Mariya ta kasance mai son mutane d...
532K 35.1K 76
A story of a young Prince and his Mother with two sisters who have been deprived of their rights by a very heartless woman #MAGAJIYA#.......