KUNDIN QADDARATA

By huguma

1.4M 117K 19.1K

Kalmar QADDARA kalma ce dake rataye bisa wuyan kowanne bawa,haka rayuwa ta gada,tafe take da QADDARORI kala k... More

Babi na daya
Babi na biyu.
Babi na uku
Babi na hudu
Babi na biyar
Babi na shida
Babi na bakwai
Babi na takwas
kundin qaddarata
Babi na tara
Babi na goma
Babi na goma sha daya
Babi na goma sha biyu
Babi na goma sha uku
Babi na goma sha hudu
Babi na goma sha biyar
Babi na goma sha shida
Babi na goma sha bakwai
Babi na goma sha takwas
Babi na goma sha tara
Babi na ashirin
Babi na ashirin da d'aya
Babi na ashirin da biyu
Babi na ashirin da uku
Babi na ashirin da hudu
Babi na ashirin da biyar
Babi na ashirin da shida
Babi na ashirin da bakwai
Babi na ashirin da takwas
Babi na ashirin da tara
Babi na talatin
Babi na talatin da d'aya
Babi na talatin da biyu
Babi na talatin da uku
Babi na talatin da hudu
Babi na talatin da biyar
Babi na talatin da shida
Babi na talatin da bakwai
Babi na talatin da takwas
Babi na arba'in
Babi na arba'in da daya
Babi na arba'in da biyu
Babi na arba'in da uku
Babi na arba'in da hudu
Babi na arba'in da shida
Babi na arba'in da bakwai
Babi na arba'in da takwas
Babi na arba'in da tara
Babi na hamsin
Babi na hamsin da daya
Babi na hamsin da uku
Babi na hamsin da uku
Babi na hamsin da uku
Babi na hamsin da hudu
Babi na hamsin da biyar
Babi na hamsin da shida
Babi na hamsin da bakwai
Babi na hamsin da takwas
Babi na hamsin da tara
Babi na sittin
Babi na sittin da daya
Babi na sittin da biyu
Babi na sittin da uku
Babi na sittin da hudu
Babi na sittin da biyar
Babi na sittin da shida
Babi na sittin da shida
Babi na sittin da takwas
Babi na sittin da tara
Babi na sittin da tara
Babi na saba'in
Babi na saba'in da daya
Babi na saba'in da biyu
Babi na saba'in da uku
Babi na saba'in da hudu
Babi na saba'in da biyar
Babi na saba'in da shida
Babi na saba'in da bakwai
Babi na saba'in da tara
Babi na tamanin
Babi na tamanin da daya
Babi na tamanin da biyu
Babi na tamanin da hudu
Babi na tamanin da uku
Babi na tamanin da biyar
Babi na tamanin da shida
Babi na tamanin da bakwai
Babi na tamanin da takwas
Babi na tamanin da tara
Babi na casa'in
Babi na casa'in da daya
Babi na casa'in da biyu
Babi na casa'in da uku
Babi na casa'in da hudu
Babi na casa'in da biyar
Babi na casa'in da shida
Babi na casa'in da bakwai
Babi na casa'in da takwas
Babi na casa'in da tara
Babi na d'ari
Babi na dari da d'aya
Babi na dari da biyu
Babi na d'ari da uku
Babi na dari da hudu
Babi na dari da biyar
Babi na dari da shida
Babi na dari da bakwai
kundin qaddara
KUNDIN KADDARATA

Babi na arba'in da biyar

8.6K 902 53
By huguma

*Bismillahir rahmanir rahim*

*wa asa an takrahu shai'an wa huwa khairul lakum,wa'asa an tuhibbu shai'an wa huwa sharrul lakum,wallahu ya'alamu wa antum la ta'alamun*

*_SAU DA YAWA ZAKU QI ABU AMMA ALKHAIRI NE A GURINKU,SAU DA YAWA ZAKU SO ABU AMMA SHARRI NE A GURINKU,HAQIQA ALLAH SHINE YA SANI AMMA KU BAKU SANI BA_*

______________________________

*ZAINAB*

Kamar yadda suka tsara ita da zinatu hakan ce ta kasance,qarfe goma na safiyar washe gari a gidan malam ta yi musu,duk da dan uban ciwon da jikinta ke mata amma sam bata kula ba,burinta kawai ta ganta gaban malam din,da yake safiya ce bata taras da mutane da yawa ba a gidan mutum daya ne ya fito suka shiga.

Kamar ko yaushe mutumin da suke kira da malam ya kuma shiga rigar malamai yayi bake bake yana zaune kan buzu,yaci babbar riga da rawani gefe litattafan addini jere wadanda ko zaka kasheshi layi guda bazai iya karantawa ba balle har ya iya gane me ya karanta din.

"Zainabu abu,ina fata buqata ta biya don na ina nan ina ta kewarki,ban manta daren mu ba na......"
"Dakata dalla malam,ni zaka yaudara?,kayimin aikin banza lalataccen aiki da tunda na fara yawon bin malamai ba'a taba min matsiyacin aiki irinsa ba,to wallahi da sake bazai yiwu ba"turbune fuska yayi ainun yana dubanta
" ke kisan fa agaban wa kike,bana son tsiya"sake harzuqa tayi tana cewa
"Eh dole mana ka fadi haka,bayan ka gama amfana da albakatun jikina ko?"
"Ke sha shashasha,ai ba kanki farau ba,kuma ke kika kawo kanki,dama tunda kika rabu da Allah babu irin qazantar da ba zaki fada ba,kinga ki fadamin abinda ke tafe dake kada ki batamin lokaci customers na tafe a hanya kada ki bata min aiki" cikin masifa ta sake takowa gabansa tana dubansa
"Amma malam bansan kai ba qaramin dan akuya bane sai yau,to wallahi baka isa kaci bulus ba,ni babu wanda ya isa ya takani wallahi na qyaleshi ban dau fansa ba ko uban waye kuwa" dariya ya barke da ita ya dinga qyaqyatawa har suka saki baki suna kallonsa
"Saidai cin bulus na gaba,bulus kuma ai na gama cinta tunda na hadaki da CUTA MAI KARYA GARKUWAR JIKI?" wata saukar guduma sukaji bisa kawunansu,ba zainab kadai ba hatta da zinatu
"Cuta mai karya garkuwar jiki!" Zainab ta tambayeshi cikin qaraji,dariyarsa ya ci gaba da yi yana kada kai
"Qwarai kuwa,wannan tsaraba ce da muke baiwa dukkan macen data bijirewa Allah,ta zabi biyan buqatar duniyarta akan ta lahira" sulalewa kawai tayi a gun,zinatu ta fasa kuka tayi kanta,ganin suna neman tara masa jama'a ya sanyashi samo mai adaidata sahu ya dorasu ya saita musu hanyar asibiti.

*MUKHTAR*

Tun ranar da sirrin ya yaye masa baki daya ya sauya,tamkar ba mukhtar ba,hatta da abdallah sai da ya samu sauyi da naqasu wajen kulawar da yake samu,ya kusa wata bai zuwa ko ina yana gida,sai abdallah ya matsa da rigima yake fita waje ya dan tattaka da shi a qafa ya dawo,babu abinda ke bijiro masa sai tausayin sumayya da tunanin da wanne ido zai kalleta?,ko wane minti daya tana dawo masa ne da irin abubuwan da ya aikatawa sumayyan,tun daga auren zainab zuwa ranar rabuwarsu,wasu abubuwan gani yake tamkar a mafarki suka faru ba a zahiri ba,kuka kam ya yishi sau babu adadi,baisan iyaka ba,yana so yaje ya warwarewa su malam komai amma yana jin wata 'yar banzan kunya da nauyinsu wadda a da bai jita ba,kusan ya mance kwanansa nawa rabonshi da gidan,saidai ya zame masa dole yaje gidan don sauke nauyin dake kansa.

**** ****** *****

Zaune take gefan gado sanye da hijabinta tana ci gaba da sharce hawaye,tsahon kwana biyu da faruwar lamarin amma ta kasa tsaida hawaye a idanuwanta wanda ita kanta ta rasa dalilin haka,kukan nata ya dadu ne tun bayan gama wayarsu da anty dije wadda kejin tamkar a kanta hakan ya faru.

Halima ce ta shigo dakin
"Yaya sumayya kije inji malam" jikinta ya qara sanyi a zatonta magana a kanta ne bata qare ba,duk da cewa babu abinda ya fada face yi mata addu'a bayan ya gama saurarar rayuwarta a gidan mukhtar,fada daya yayi mata na rashin neman taimako daga wanda tasan ya fita gogewa da sani kan irin wadan nan lamuran,al'amura ne da kake buqatar addu'a koda daga wajen iyayenka ne daga bakunansu,tunda addu'ar tasu karbabbiya ce a wajen ubangiji.

Cikin sassanyar murya tayi sallama a falon nasa,da abdallah idanunta suka soma tozali,ko kadan batayi tsammanin ganinsa a lokacin ba shi ko mahaifinsa,ai da gudu ya baro jikin mukhtar din ya iso inda take tsaye ya riqeta yana kiran amma na,jikinta da zuciyarta baki daya a raunane suke,hakan ya sanyata zubewa shima ya fado jikinta,sai ta rungumeshi a jikinta tayi qas da kanta hawaye ya balle mata a boye,cikin dabara take shareshi.

"Sumayya" taji malam ya kirata
"Na'am" ta amsa murya a sarqe
"Ga mukhtar nan yazo neman gafararki kan abunda ya faru tsakaninki da shi a baya,wanda mu nasan ya riga da ya wuce a gunmu saidai tsakaninku dai" ya fada yana miqe ya fice ya turo halima ta zauna da su tunda ya sani a lokacin bai halatta ya barsu su kebe ba,har a sannan tana matsayin matar lukman har zuwa sanda ta kammala idda.

Dauke idanunsa yayi da sauri daga kanta saboda tunawa da yayi matar wani ce,rabonsa da ya sanyata a idanunsa ya mance,tun kafin aurenta.
"Sumayya,nazo gareki a matsayina na mutum mai tarin laifi,a matsayina na mutumin da yafi kowa laifi duk duniya a gurinki,nasan cewa kalmomina basu isa su haqurqurtar da ke kan abinda na aikata a gareki ba cikin jahilci,gaggawa da yanke hukunci cikin rashin bincike,tun ranar da na san gaskiyar lamarin naso neman gafararki amma hakan bazai yiwu ba saboda kina gidan wani,yanzun ma mama da malam mazo sanarwa ya gayan kina kusa,don girman Allah sumayya na roqeki ki yafemin,koda kuwa wannan ne alfarma na qarshe da zakiyimin,babu shakka zainab ta zalunce ni ta zalunceki ta kuma zalunci danmu,kimin afuwa don Allah" tsam ta miqe ba tare da tace komai ba ta dauki abdallah ta fice daga falon,sai yayi qasa da kansa zuciyarsa na masa zafi,yayin da nauyi ya kama halima,sai ta miqe tabi bayan sumayya itama.

Ranar bacci barawo ne kawai ya dauketa,zafi goma da ashirin ke bugun zuciyarta,ta duba ta laluba kaf rayuwar aurenta babu wanda ya ruguza farincikinta sai mata 'yan uwanta,babu abinda ta aikata musu don kawai sun hada miji?,me yasa kishiya ta zame mata qalubale cikin rayuwarta baki daya?.

Sannu kwanaki suka dinga hada satittika,satittika suka hadu suka bada watanni,ta miqawa Allah dukkan lamarinta baki daya,ta yadda babu bawan da ya isa ya gujewa qaddararsa,watanni uku cif cif iddarta ta cika,ta godewa Allah bisa baiwa da ni'inar lafiya da ya bata,ta watsar da dukkan wani abu ta rungumi rayuwarta,riqon Abdallah ya dawo wajenta,hakanan taci gaba da makarantarta na koyon sana'o'i,wanda zuwa lokacin ta qware sosai wajen iya humra kwalakca da turaren daki na kaya da na tsuguno,ya abbakar shi ya bata jari ta soma gwadawa,Allah kuwa ya sanyawa abun albarka don ciniki take sosai,don kana shigowa gidansu zakasan ana saida humra balle kuma jikinta,nutsuwa sosai ta sake zuwa mata,wani girma da hankali na musamman ya soma gameta,mukhtar kuwa har yau bata yarda ta sake ganinsa ba ma bare ya dagula mata lissafi.

**** ***** ****** *****

Qarfe bakwai na bayan sallar magariba ta gangaro cikin layinsu abdallah na sabe a kafadarta,tun daga makaranta ta wuce gidan anty maryam qanwar mama sai gab da magariba ta fito.

Tana gab da gidan nasu ta kula da motar wadda ko daga bacci ta tashi zata iya ganeta,motar mukhtar ce,sai ta dauke kai tana qoqarin wucewa cikin gidan,saidai abdallah dake kafadarta wanda ya soma zillo ganin babansa yaqi bada hadin kai,tilas taja tunga ta saukeshi da niyyar ta wuce ta barshi a gun,saidai tana dagowa daga durquson da tayi ta tsinci mukhtar din tsaye a gabanta
"Zan wuce malam" ta fada ranta a hade
"Kiyi haquri malama" ya fada da irin salon muryarta,kicin kicin tayi ganin yadda yake son maida lamarin wasa
"Ka bani hanya da Allah kana batamin lokaci bana son shirme" tsit yayi yana kallonta,ita kanta sai taji kalma ta mata nauyi,don haka ta basar ta hanyar gyara hannun hijabinta
"Sumayya" ya kirata da wani irin salo wanda ada can yake kiranta da shi,kira ke da idan yayi mata take jinsa har cikin jikinta
"Ki yafemim sumayya,a kullum tsahon wata biyar kenan cikin neman yafiyarki nake,idan na kira baki dauka,idan nayi miki saqo baki reply,kiyi haquri ki yafemin,na yadda nayi babban kuskure a rayuwata amma na girbe abinda na shuka ai,na rasaki na tsahon wasu shekaru,ban taba tunani a baya akwai abin zai rabani da ke ba idan ba mutuwa ba,tunda na rabu da ke sumayya ban taba samun nutsuwa ta minti guda ba,Allah ya hukuntani tunda har kin shiga gidan wani sumayya,ki zama mai afuwa da yafiya kamar yadda na sanki nasam halinki a baya,mukhtar dinki ne sumayya bazan daina neman yafiyarki ba matuqar baki yafemim ba har sai ranar da numfashina ya bar gangar jikina...."da sauri ta katseshi don yana neman karya mata zuciya
" don Allah ka bani hanya,na gaji da jin kalaman bakinka"murmushi ya saka yana kada kai
"Shikenam sumayya,idan kinso ma ba zaki sake gani na ba tunda haka kika buqata,amma bazan daina neman afuwarki ba,na barki lafiya"ya fada yana juyawa ya danqawa Abdallah wani dan madaidaicin kwali ya wuce motarsa,sai ta samu kanta da tsayawa cak a gun ta kasa tafiya har ya bar layin,tausayinsa nason rinjayar zuciyarta,tuna wahalhalun da tasha shi ya bijiro mata ya taurarar da zuciyarta,kama hannun abdallah tayi suka shige ciki.

***** ****** ******

Tunda ya bar gidan yaso tilastawa kansa cireta daga zuciyarsa saidai ya gaza hakan,wata sabuwar soyayya da qaunarta ke yawo ko ina cikin jinin jikinsa fiye da irin qaunarta da yake ji a da,sai ya soma komawa wani iri,ko da yaushe cikin tunani,ga wani matsanancin ciwon kai dake matsanta masa wanda ke kwantar da shi,yana mamakin yadda ya kasa haqura da ita,ji yake tamkar idan ya haqura da ita din zai rasa numfashinsa,hakan ya sanya ya shirya da kansa wani dare bayan ya yiwa abbakar waya ya sanar masa ya gayawa malam zaizo zasu tattauna,idan da hali abubakar din ma ya zauna.

Qarfe takwas yana sitring room din malam din dake qofar gidansu,hakan ne ya sanya babu wanda yasan da zuwansa a cikin gidan.

*mrs muhammad ce*

Continue Reading

You'll Also Like

12.9K 433 56
labari ne data kafu aka kadara🙇🙇 Kubiyoni ku ji yanda LabariDr. Essha Ahmad zata Kaya da Young Tycoon Namji Mai ji dankashi Aliyu Umar Tycooon 💃...
250K 20.3K 61
"Tun ina yarinya kike zagin mahaifiyata, tun bansan menene maanar kalmomin wulakanci da muzgunawa ba nakejin kina fadarsu ga mahaifiyata, ina cikin w...
9.6K 306 57
I'm bored so...bakudeku bs
58.6K 4.4K 78
Najib yaron littafin bai dda buri da aaddu'a sai ta Allah yaya bashi mace ta gari mai ilimi Sumaiyya Yarinya ce yar karya wacce ba abinda ta iya sai...