chapter 1

2.6K 98 3
                                    

A KASAR LONDON.
Yarima Mustapha zaune a dinning area yana jiran matarshi Fatima dake kitchen tana hada mishi karin kumallo. Qarar ringing din wayar shi ce ta katse shi daga duniyar tunani daya shiga. Dubawa yayi a fuskar wayaran saka "my mom".  "Hello,hajiya ya gida?

"Lafiya kalau. Dama jikin mai martaba ne ya tashi, shine nace bari in sanar dakai"
"

Innalillahi hajiya me ya sa meshi kuma ynxu?
"Ciwon shine na diabetes ne ya tashi dan jiya ma bamuyi bacci ba a asibiti muka kwana"

"Insha Allah a cikin satin nan zan siya ticket in dawo domin duba jikin mai martaba"cewar yarima.
"Dama waziri ne dazu yake cewa zai sanar da kai shine nace ya bari zan sanar maka da kaina".
"Nagode sosai hajiya. Ki gaidamin mai martaba. Insha Allah nan da sati me zuwa zan wa Nigeria tsinke"
"Toh Allah ya kaimu kuma ya kawo ka lafiya. Ka gaida min da jikokina da ita fatiman"
"Zasu ji insha Allah"
  Haka ya gama waya da hajiya wacce take maman shi. A duniya yarima Mustapha na bala'in son matarshi dan a cewar shi tayi mishi komai a rayuwa. Domin hajiya ita ce silar farin cikin shi. Da taimakon ta ya auri Fatima,yanzu gashi har Fatima ta haifa mishi yara biyu. Tsintar maganar Fatima yayi da take kokarin fitowa daga kitchen
"Honey,kashiga duniyar tunani I hope komai lafiya. Daxu naji kana waya da hajiya I pray nothing happened"
"Kira na tayi take sanar Dani jikin mai martaba ba dadi dan jiya a asibiti suka kwana"
"Innalillahi,Allah ya bashi lafiya yasa kaffara ne"
Mika mishi spoon tayi dan ya fara cin abincin da ta dafa mishi.
"Honey favorite food dinka na dafa maka amman naga gaba daya hankalin ka ba a nan yake ba kashiga duniyar tunani and I'm worried"
"Wlh dukk rashin lafiyar mai martaba ne ya daga min hankali Amman don't worry yourself  kinsan bana son wani abu ya Sami baby na" ya fada yana kallon cikin jikinta daya taso alamar cikin ya kai wata hudu.
"Dama in ka gama cin abincin ina so muyi wata magana"fatima ta fada tana kallon yarima da yake cin abinci.
"Ok"yace mata a takaice.
   Ya gama cin abinci suka koma parlour domin kallon wani TV show da suke following. Yau gidan shiru da yake Abubakar da Aisha sun tafi summer lesson. Chan Fatima ta nisa sannan tace "hmm honey are you ready to hear what i want to tell u?
"Yes I'm all ears" yace mata.
Fatima tai Kiran Mustapha shima ya zuba mata manyan oily eyes dinsa yana son jin me zata ce don yasan maganar bazata wuce na zata bishi Nigeria ba. Katseshi daga tunani tayi take cewa"dama zancen zuwan mu Nigeria ne ni da yara". Kaduba yau shekarar mu shida da aure baka taba kaini gidanku ba, baka taba nunamin dangin ka ba. Kullum idan nayi maka korafi zancen ka daya Wai GIDAN SARAUTA akwai gulma, GIDAN SARAUTA ya fiye munafunci, GIDAN SARAUTA bashi da dadi, ba zamu sake ba ni da yara na a GIDAN SARAUTA ba.
Toh menene a GIDAN SARAUTA
         Readers ku biyoni kuji tashin hankalin dake GIDAN SARAUTA da Mustapha baya son Fatima da yayanshi su fuskanta.
VOTE🤗
COMMENT 🤗
LIKE🤗

GIDAN SARAUTA 👑Where stories live. Discover now