DAN MINISTER

939 22 0
                                    

👝👝👝👝👝👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠👠👠👠👠
👝👝👝👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠👠👠
👝👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠
👝👝👝👝
👠👠👠
👝👝
   👠

💄💅 *DAN MINISTER* 💅💄
           🦚🦚


Written by *Husba'ahfama*

*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*

Follow me on Wattpad *@ Real Husba'ahfama*









                       9-10





MINISTER  yace baffah kayi hakuri wlh tsohuwar ce bata da mutunci Dan Haka nake ajje komai agefe nake kulata yanzufa kaji me tace Wai MINISTER take Kira da Miss miss Wai mukamin Miss Miss aka bani Dan Allah Kar ta Kara kwanar Mana agida ta koma inda  ta fito har jikar tata

Baffah yace Ni dai azamana na mahaifinka ka dena shiga harkar yarannan kayi kokarin hada kansu ba Wai kana hura wutaba Kana nuna bakaso tin daga jiya Allah yafara nuna maka ishara Akan auransu tashin farko anfasa maka goshi yau baya gaba in ka kuma shiga har karsu bakasan me ze faruba karabu da iya Kar ka daka ta halinta kaso shatuwa kamar yanda kake san nabil gaba bakasan wana alheri zata za me mukaba azuriarka gaba zakaji kunyar abinda ka aikata  infa kaji nasihata in Kuma bakajiba to Allah yaba da sa,a tashi ka tafi

Bayan minister yafita

Baffah yace Fatima Allah yaimiki albarka Allah yabaki hakurin Kula da yarannan nasan daga ke har Amina Baku da matsala yanzu Dan Allah kiga me yarannan sukayi yau kowa acikinsu Yana Ji da danyan Kai ita rikwan Kaka uwa ba kwaba shikuma rikwan namiji uba bakwaba ga nabil da shegiyar zuciya da zafin Rai ga shatuwa da tsokana da taurin Kai shi ma Kuma nabil din akwai taurin Kai in Abu yafi karfinki atsakanunsu kina kirana ki sanar da Ni zan zo Dan sani ba ze musu fada na tsakani da Allah ba se yasa San zuciya aciki nashi ze so ita Kuma iya dole yau na jata mubar gidannan yakin badar din da akayima jiya da yau ya isa haka ai in har akabar iya agidannan bazamu iya gyara ko maiba yanzu kije kisa akai mata abinda takeso taci se mu tafi du abinda yashige Miki duhu Akan abinda na fada miki kiki rani kijin Allah yabamu sa,a Akan niyarmu ta alheri Kan yarannan

Tace ameeen baffah Ni yanzu damuwata yanda nabil da shatuwa zasu na kwana waje Daya wlh abinda kamar wuya Dan bakaga rigimar da mukayi dshi Akan su iya sun kwanar Masa adaki cewa yayi yabar bangaransa gaba Daya Kuma baya San komai na wajan shi sabo ze canja se da nacimai mutunci sannan yahakura Kuma kasan alhaji bayansa ze goya

Shawara baffah yai tabawa hajiya Fatima sannan yadada samun minister yadada jamasa kunne sosai Amina itama yafada Mata gudunmawar da yakeso tayi atsakanin nabil da shatuwa

Iya ankai ruwa Rana da ita sosai Kan ta yarda ta koma mazagai ta rabu da shatuwa bakara min kuka iya tashaba na rabuwa da jikarta har tausayi tabawa su baffah ana haka nabil yashigo falan yasamu iya tana kuka Baki yatabe yaja tsaki kawai se gani sukayi iya tatashi tsaye tabi ta bayan nabil babu zato babu sammani Dan Babu Wanda yakawo me zatayi tatakarkara ta dimawa nabil dundu a gadan baya se da yagantsare Dan abin yashige shi beyi zatoba se saukar hannunta yaji

Iya tace Dan kwal uba ai ga Wanda du yaja komai Nan yarabani da jikata muna zaman zaman mu Kuma Zan tafi saura ka Kuma karyamin ita Kuma har yanzu ban huceba se nayi zaman Yan bori akanka ko yaushene me zubin karfafa me shigar Mata dandudu kawai yau Kuma irin shigar da akayi kenan kuma ubanka nagani yaki ya hanaka Dan miss miss din uwa kawai takalli hajiya Fatima yarnan bakiya Saar Daba da mijiba du Basu da mutunci ke Kuma gaki saliha me kirki Amma auran Dole aikai Miki da uban Dan daudun Nan ko Dan Baku dace da junaba

DAN MINISTERWhere stories live. Discover now