Chapter 17

68 2 0
                                    

Kusan zan iya cewa na saba da kuka a duk lokacin da rai ya bace, balle kuma yanzu da kaddara ta sauya min mu'amala da dabi'u. Kuma ta rufe ni a cikin wani dakin da ban isa na fitar da kaina ba. Idanuwa na saka ina ta kallon yadda ake ta kai da kawo na sha'anin bikin aureni a yayinda bani da wani kuzari na magana ma balle na motsa, kamu, walima da wani event da ake yi na aure ban shirya ko daya ba, Hana ce mai kokarin ganin na yi wasu abubuwa amman ban saurareta ba domin ni kadai ya san yadda nake ji a rayuwata na auren mutumen da ba shi a lissafina.

Ana sauran kwana biyar adaura auren Hafiz ya saka a sallamomi, a lokacin na ci kuka har na sauya kalar idanuwana, sai na fito ina tafiya kamar bana son isa inda yake tsaye. Daga jikin kofar gidanmu na tsaya na rumgume hannyena kaina na kasa domin bana son kallon fuskarsa ma. Daga inda yake jingine jikin mota sanye da kananan kaya ya dago ya karaso kusa da ni kamshin turarensa na kara kusantar hancina. Wayarsa ya ciro daga aljihu ya kunna haske fitilar ya haska fuskata.

“Noor Lafiya kike kuwa?”

“Ni ban taba lafiya ba tun da kuka shigo rayuwata”

Na amsa masa ba tare da na kalleshi ba. Wayar na ga ya kashe ya saka aljihunsa.

“Daman na zo ne na tambaya me zaki yi a cikin shirye shiryen da yan mata suke yi?”

“Ba zan yi komai ba”

Na amsa a takaice.

“Okay, daman dai na zo na ji saboda na bada kudin shirye shirye idan har zaki yi, kuma Balkisu wato uwargidana kenan ta shirya Walima da Kamu, saboda na fada mata daman abu ne mai wahala ki iya shirya wani event, wannan ina fatan zaki je?”

“Ba zan je ba”

Ya tsaya kallona kamin na ji saukar ajiyar zuciyarsa. Ya gyara tsayuwarsa ya fuskance ni da kyau sannan ya kira sunana kai tsaye da siffar da be taba yi ba.

“Khadija...”

Na daga kai na kalleshi duk da kasancewar bana ganin fuskarsa da kyau saboda duhun dare.

“Ina son na yi wata magana dake, na san kina da kiriniya kina da kurciya amman duk da haka kina da hankali kuma kina da tunani irin na mutane domin ke mutum ce. Kin ga tun farko ni da ke ba mu san juna ba, ban san ki ba baki san ni ba, amman da Allah yayi nufin hada wani abu a tsakaninmu sai ya kawo dan'uwanki a gurin kasuwancin abokina, duk da haka kuma be hada ni da ke kai tsaye ba sai ya hada ki da abokina wanda shi ne silar faruwar komai a yanzu”

Yayi shiru na wasu dakiku sannan ya shiga.

“Wallahi Noor ban saka ran aure nan kusa ba, kuma ban yi tsammanin zan aureki ba, ina wani tunani da tsari ne na dabam a rayuwata game da ke ashe abun da Allah yake tsara mana dabam, kuma dai kamar wasa na amsa abun nan gashi ya zame min gaske, ban san zafin rabuwa da masoyi ba, amman na san dadin auren wanda kake so domin matata ta farko auren soyayya muka yi, sai dai ke ina hango miki wani abu a yanzu wadda na kasa gani a baya, kuma ina hangen wani rame da yake shirin fadawa da ni”

Ya gyara tsayuwarsa.

“Shiyasa yau nake son mu kai karshe da ke, Noor ko dai mu karbi kaddarar nan ko kuma mu hakura da juna, saboda ina jin tsoron abun da zai je ya dawo, ance idan gemun dan'uwanka ya kama da wuta to ka shafawa naka ruwa, Zan iya samun Mahaifinki na fada masa cewar na sanyi zancen auren nan, domin na lura san baki ra'ayi na, yadda nake tunanin zan iya juya ki kamar hakan sai gagara a gareni”

Na kalleshi da sauri ina girgiza kai hawaye na sauko min.

“Fasa aurena ba zai saka Baba ya amince na auri Zafeer ba a yanzu, kawai zai janyo min matsala ne tsakanina da shi, zai tsine zai yi fushi da ni, Kareem ya riga ya kawo ka a rayuwata kun ruguza min komai”

TA ƘI ZAMAN AURE...Where stories live. Discover now