Yau ya tashi baya jin daaɗi hakan ya sa yace da ya tsaya zuwa jeji dibowa dabbobin abinci gwara ya korasu suje su ci tunda ya kan fitar dasu, fita dasu yayi zuwa chan wajen gari se ya kaɗa su ya samu wuri ya kwanta tun jiya da rana be ci komai ba yunwa yake ji ga zazzaɓi dake damunshi wadda damuwa da yake ciki ne ya haddasa mishi.. Mutanen gari sun maida shi wani soko,gaula wasu har kallon marar cikakken hankali suke mishi hakan yasa yake iya yinshi wurin gujewa mutane.

Yannenshi ko kusa dasu be isa zuwa ba daga me hanbari se me duka, yadikkonanshi babu wacce ta taɓa faɗan abun arziki a kanshi duk bautar da yake musu haka nan uban da ya haifeshi be san zafinshi ba.

Kuka yayi sossai a wurin yayi ta jan numfashi daga karshe ya tashi ya kaɗa shanayen suka koma gida, ba tare da ya san a kiwon da suka yi da wasu shanayen akwai wani ciwo dake jikin waenchan wadda suka sakawa nashi ba.

Dare shanaye basu barshi ya rintsa ba kan safe wasu abubuwa kaman bulalai suka fiffito musu a kafafu nan take biyu suka cika, hmm misalta irin halin da ya shiga ɓata lokaci ne..

Duka shanayen suka kamu ko da hantsi yayi lokacin da Babanshi ya zo duba shanayen kaman yadda ya saba abunda ya gani ne ya kusa sumar dashi.. Kasa magana yayi yasa aka kira likitan su yazo yayiwa sauran shanayen Allura Sede ana gamawa uku suka sake mutuwa Wayyoooo zubewa kawai Bukar yayi a sume aka fita dashi..

Badi'ah dake kallon yadda Raed ke numfashi da kyar yana fusga ne tace
"Wallahi ka shiga uku Raed idan babanka ya dawo ya sameka a gidan nan, ka ga yadda ka kashe shanayen nan haka ze kashe ka, dama jiya ya gama gayamin ya tsaneka tsanar da be taɓa yiwa kowa ba baka da anfani a gareshi, ko kallon ka baya son yi yanzu kaga se ya kashe ka da hujja..."

A tsorace yake kallonta.. Suka yi dariya suka tafa da Naja.. Naja tace
"yau fa shikenan kwanan wani ya kare kaman yadda mamanka ta tafi har Abada"

Mikewa yayi a tsorace ya rabe su ya fice sbd magana shine abu na karshe da zaka ji daga gareshi..

Tunda ya fita yake ta tafiya in yaga mutane se ya raɓe ya wuce idan kuwa namiji ne se ya dauka Babanshi ne ya fara ihu yana cewa yayi haƙuri baze sake ba.. Mutane dayawa sede su ce Allah sarki Allah ya baka lafiya yaro.

Gidan David ya tafi duk uban nisan dake tsakaninsu, ya same su da Philip sede ya kasa karasawa se kuka,idan sun matso se ya matsa gabaɗaya ya rikice barin ma in ya tuna yadda aka fita da Babanshi ai in ya warke ya dawo shi ba a sume za'a fita dashi ba sede a mace.

Philip da ze wuce Kano ne yace
"Pastor I think I will be going with this boy, can't u see he's depressed and he's seriously sick.. Daga ka ganshi zaka san panic attack na damunshi idan uban shi baya sonshi ni ina son shi I will take him with me"

Duk yadda David ya so ƙi Philip ma nacewa yayi yace idan yaron ya girma ya dawo da kanshi amma yanzu ba ze bari ya koma ba.

Sanadiyar fitan shi Mambila kenan suka tafi Kano sun ɗan kwana biyu Seda Visa ɗinshi da komai nashi ya fita kan suka wuce US anan Philip yake rayuwa da matarshi da kuma ƴarshi mace wadda shekara huɗu Raed ya bata.

First jinya ya fara yi sbd yadda ko cikin dare numfashi se ya sarƙe mishi ga mafarke mafarke, ga yawan tsorata rashin son mutane in kuwa ya ga baƙin fata nan take se ya ruɗe.

Yana jinyar yana samun sauki a hankali Philip ya sa shi school sede be son boko Sam, da kyar ya gama grade 5 yace shi kam ya gama karatu da Philip ya tambayeshi abunda yake so yace ball.

Nan yayi enrolling ɗinshi ya samu trainee wani irin baiwar kwallo yake dashi, nan take ya fara fita wasanni in kana son farin cikinshi ka mishi hiran kwallo, abu guda ɗaya da be bari ba sallah, ya kan Haɗa salloli biyar da dare yayi Dukda be ga kowa nayi ba a gidan.

KOWA YA GA ZABUWA...Where stories live. Discover now