Page 5

245 18 0
                                    

KOWA YA GA ZABUWA...
   (DA ZANEN TA YA GANTA)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.            
         (Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
And Now
*Kowa Ya ga zabuwa..*

                      *PAGE 5*

*FREE BOOK*

Ba ƙaramin tashi hankalin Abba yayi ba, nema har police station ta ya ze fara cewa Allah ya kasa riƙe alkawarin da ya ɗauka na riƙon marainiyar nan har karshen rayuwarta? Cikin haka ya ga call da sabon layi kaman ba ze ɗaga ba se kuma ya ɗauka.

"Alhaji kana magana ne da mahaifin Ummi kawar ƴar wajenka Hidayat ce kawai muka gansu bayan an tashi gashi har yanzu ta ƙi yarda a maida ta gida"

Ajiyar zuciya ya sauke kan ya tambayi kwatancen gidan, nan ya faɗa mishi unguwan da kyar ya iya cewa drivern "mu je dorayi malam isa"

Bayan sun isa mahaifin Ummi ya musu iso zuwa cikin gidan, karamin gida ne na masu rufin asirin Allah machine ɗinshi na Parke daga gefe, har parlor suka shiga ya saka ummansu ummi ta kira mishi su, hidayat na ganin Abba ta fara hawaye, itama ummi na tayata riƙe hannunta tayi tace
"bana so a dakeki Hidayat amma ya zan yi?"

Haka suna gani Abba ya janye ta suka tafi, a mota cikin karaya da ganin yadda take hawaye yace
"Hidayat! Tunda kika fara wayau Na taɓa tauye miki wani hakki na uba akan ƴarsa?"

Kai ta girgiza cikin sanyi yace
"to menene? Gayamin yanzu me yasa bakya son komawa gida?"

Cikin kuka tace
"Abba Umma zata kasheni in na faɗa maka"

Idanu ya kura mata na lokaci kaɗan kan yace
"in shaa Allahu babu abunda zata miki, ba zan bari ba gayamin kin ji?"

Kai ta gyaɗa kan tace
"Abba bani jin daaɗi ban yiwa Surayya assignment nata ba nima ummi ce ta min sbd takardar a wurinta ya kwana, teacher ɗin beat for the assignment na san in na koma umma ma dukana zata yi"

Driver ya girgiza kai, yace
"kayi hakuri Alhj amma zan bada sheda don akwai ranar ma da bata yi mata assignment ba aka dake ta a gabana hajiya ta zane yarinyar nan hidayat, wani abu dake ci min tuwo a ƙwarya shine yadda suke hana yarinyar nan zama a kujera gashi bani da halin magana, nayi sau ɗaya hajiya tace in tsaya matsayi na ko in rasa aiki na"

Abba cikin wani yanayi yace
"menene shi da yake ci maka tuwo a ƙwarya?"

Driver yace
"Alhj Hidayat bata isa ta zauna akan seat na kujeran ba, a inda kafafun ka suke ɗin nan wurin tsugununta kenan a kullum sannan bata da kulan makaranta"

Da sauri Abba ya kalli inda kafafunshi suke ya juya ya kalli hidayat hawaye ya cika idanunshi yace
"hidayat me kuma take miki? Ki gayamin kinji?"

Abubuwan da ake mata ta bashi labarin wasu, he was totally speechless har suka isa gida be iya ya ce komai ba, sashenshi yayi da Hidayat abincin da aka yi don shi ya bata ta ci ya dinga saka mata namomin har ta cinye, shi yaje har ɗakin su ya ɗauko mata kaya ya saka ta tayi wanka a toilet ɗinshi ta sauya, shi ya wanke mata uniform ɗinta Kal ya shanya.

A lokacin daya dawo ya samu tayi bacci nan kasa ya ɗaga ta ya maida ta kan gado haka ya zuba mata idanu yana kallo, yanzu har yarinyar nan tayi girman da za'a iya zalunta? Umma bata tsoron wani abu ya samu wannan ƴar batalikar Allahn? Fisabilillahi this loving soul kyakyawar yarinya na nunawa sa'a.

Babu irin Tunanin da be yi ba akan matakin da ze ɗauka, har Tunanin ƙara aure Seda yayi daga karshe ya yanke hukuncin da zuciyarshi ta fi bashi ita ce daidai.

KOWA YA GA ZABUWA...Where stories live. Discover now