Page 6

268 21 1
                                    

KOWA YA GA ZABUWA...
   (DA ZANEN TA YA GANTA)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.            
         (Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
And Now
*Kowa Ya ga zabuwa..*

                      *PAGE 6*

*FREE BOOK*

"Hidayat! Ni kuwa zan so sanin wannan labari ko zan amfana da wani darasi na zamantekwar rayuwa"
Zata yi magana suka Haɗa idanu da Yusuf dake bautar ƙasa yanzu, irin kallon da yake aika mata yasa tayi saurin wucewa Dukda be taɓa dukanta ba sede ta san yana da manufa me girman gaske a kanta.

Hamza na ta aikin kiranta sede ko waiwaye bata yi ba, Yusuf ya kalla na seconds kan ya juya ya tafi.

Bayan ta dawo daga islamiyya tana shirin shiga gida Kenan taji an fisgo hannunta, a tsorace take Kallonshi har ya isa sashesu da ita a jikin gini ya bugata har Seda ta runtse idanu, manneta yayi sossai ba tare da ya damu da haramcin hakan ba yace

"ki buɗe kunnuwanki da kyau ki saurareni, ya zuwa yanzu kalar muguntar Umma da su khausar kawai kika sani baki san ni ba, amma idan kina so ki fara sani in kara ganinki da kowanni kalar namiji ki gani!"

Kai ta gyaɗa banda hawaye babu abunda ke zuba daga fuskanta sbd yana maganan ne yana tattaɓa jikinta, bayan ya saketa ta fice da gudu cikin kuka Abba be yi dacen mata da ƴaƴa ba, taya mutum me karamci irin shi ze samu ƴaƴa da mata irin umma da su Yusuf?

Ko da ta shiga gida bata dawo daidai ba khausar da duk suka ajiye islamiyya tunda Abba yayi tafiya tace ta yi mata custard a babban jug sbd shi suke son sha yanzu yanzu, ko jaka bata ajiye ba ta shiga kitchen har lokacin jikinta rawa yake na abunda Yusuf yayi mata hawaye kuwa wani na bin wani a fuskanta, ta gwammaci abunda su khausar ke mata sau dubu da abunda yusuf yayi mata yau ta ja Allah ya isa ya fi abinda ya fi a ranta.

Saboda yadda take a ruɗe garin dama custard abu kam yayi gudaje, Sam bata ma kula ba ta ɗauko ta kawo musu dayake haɗewa take da madara da sugar da garin, tana kawowa ta ajiye ta juya har ta ɗaura hannu kan handle na kofansu taji Fahariyya ta saki ashariya, a razane ta juyo gabanta na dukan uku uku.

"Aunty khausi kina ganin irin Gudajen dake cikin custard ɗin nan!"
Aunty khausi da Surayya har rige rigen karɓan cokalin suke, suna gani kuwa suka kirata ta dawo.

"Ɗauka ki shanye!"
Wara idanu tayi a duniya babu abunda bata iya sha irin custard, amai yake sakata hakuri take shirin basu, Khausar ta tsinka mata mari tace
"dauka nace!"

Dauka tayi sede ta kasa kaiwa baki, mikewa suka yi suka danneta suka ɗura mata shi cikin tsantsar mugunta, Surayya bata saki hancinta ba seda custard nan ya kare tas, mikewa tayi zata fice da gudu umma dake zaune tun ɗazu bata ce komai ba se yanzu tace
"dawo ki zauna, kika kuskura kika amayar min da madara da sugar na wlh se na lahira ya ciki jin daaɗi tunda ba guminki bane"

Zama tayi sede bata da wani iko da amanta, duk yadda tayi son dannewa kasawa tayi ta yunkura zata mike Salamatu ta saka mata ƙafa anan ta faɗi a kan hannunta, aman da take dannewa ya kwace mata ta sake shi anan.

Duk mikewa suka yi suna zazzare idanu sbd tas a jikin mus'ab ta kwararo shi, yana mikewa ya sake mata wani bahagon mari da Seda jini ya balle a hancinta, kasa magana yayi ya juya ya fice.

Umma bata barta ba seda ta kwashe aman tas ta wanke wurin da omo ta saka turaren wuta da room freshener kan ta samu ta shiga kitchen ta dinga zuba ruwan sanyi a kanta har haɓon ya tsaya, hannunta da take ji kaman ya samu matsala ta tallafe tana zub da hawaye, a haka ta ɗaura musu abincin dare cikin taka tsantsan don in tayi kuskure kashin ta ya gama bushewa.

KOWA YA GA ZABUWA...Where stories live. Discover now