Kallonta kawai yake she's now a grown up woman ba kaman sadda ya Santa ba, tana magana da hankali da kuma natsuwa, Sam maganan ta be dame shi ba yace
"na sani and I will help u with all my strength idan bukatar hakan ta taso har ki cimma Burin ki, I just want ur love nd care Hidayat..!"

Ya kira sunan a hankali, ajiyar zuciya ta sauke tace
"zan yi shawara akan hakan na gode"

Kai ya gyaɗa yace
"I would like to see Junior and Aisha gashi flight ɗin yamma zan bi na koma Nigeria"

Ko karen hauka ne ya cije ta bazata kaishi gidan Raed ba, a hankali tace
"eyyaa next time in shaa Allah"

Murmushi kawai yayi sun ɗan taɓa hira suka yi sallama, kuɗi ya bata ta ƙi karɓa se da yayi da gaske kan ta amsa ta Mishi godiya ta shige school..

Bayan ta dawo ta hau ayyukan ta kan yaran su dawo, tana cikin kitchen take ta jin ringing na landline ɗinsu wanke hannayenta tayi ta fito ta zo ta ɗauka ta saka a kunne se tace
"Assalamu Alaikum warahmatullah"

Shiru aka ɗan yi kan taji muryar wata dattijuwa tace
"Wa'alaikumussalam warahmatullah yau sallama ake min daga gidan Raed?"

Muryar wata dattijuwa ya ratsa kunnuwanta, a natse tace
"Ina yini hajiya!"

Matar na hawaye har muryarta ya bayyana hakan tace
"lafiya ƙalau Alhamdulillah ƴan nan wacece ke?"

Hidaya na mamakin halin da matar ta shiga kawai daga jin hausa da kuma sallama a gidan na Raed tace
"Sunana hidayat, ni ce sabuwar nanny ɗin su Norah"

Kuka kawai matar ta saki sossai tana cewa
"Alhamdulillah adu'ata da na jima ina yi ne Allah ya amsa mini, ke ɗin kaman haske ce don Allah Don Annabi ki taimaki rayuwar waennan bayin na Allah, rayuwar su ya gama tabarbarewa bani da yadda zan yi ne nake Kallonsu a haka... Hidayat ki min alkawari zaki cecesu ki fitar dasu daga cikin baƙin duhun da suke ciki"

Hidayat tace
"kiyi hakuri hajiya ki dena kukan nan, in Shaa Allah zan yi miki duk abunda kike bukata in har be fita a musulunci ba"

Godiya tayi ta mata kaman zata fito ta wayan ta duƙa mata, hakan ya taɓa zuciyar hidayat sossai a hankali matar tace
"sunana Hafsah amma ƴaƴana da jikokina suna kirana Daadida"

Kwarai ta taɓa jin sunan na Daadida eh ta taɓa ji wurin Raed, itace kullum yake yiwa masifa cikin waya..

"Nice na haifi mahaifin Raed"

Shiru hidayat tayi tana sauraran ta, ashe suna da dangi da ƴan uwa kuma musulmai shine suke rayuwa cikin ɓata?

"Rayuwar Raed abun a tausayawa ne kwarai da gaske, sbd be taso cikin farin ciki kaman kowanni yaro ba, ya rasa mahaifiyarshi tun yana shekara uku banda azaba da baƙar rayuwa be san komai ba a wurin yadikkonanshi da Mahaifinshi karan kanshi... Labarin Raed labari ne me tsawo da ba ze yiwu a waya ba sede abunda na sani baƙar Gaaba ce me tsanani tsakanin shi da Mahaifinshi hakanan be san komai ba game da addini, gashi yayi auren wuri da yara suma mahaifiyarsu ba musulma bace ƴar marikinshi ne ya aura kuma ta mutu ta bar mishi yaran babu addini.."

Tayi shiru tana fyace majina tace
"Kiyi mini alkawari za kiyi wannan aikin jihadin? Wlh Allah ne kaɗai ya san sakamakonki in kika taimaki rayuwar waennan Bayin Allahn"

Ajiyar zuciya me karfi hidayat ta sauke, no wonder rayuwarsu yake a haka, ashe akwai binnannen abu a ƙasa cikin sanyin murya tace
"in shaa Allahu zan yi iya kokarina wurin ganin na taimakesu saboda Allah"

Godiya sossai Daadida ta mata suka yi sallama akan zata ke kiranta irin wannan lokacin a landline ɗin gidan..

Kitchen ta koma ta cigaba da aiki cike da tunanuka iri iri, tana cikin shirya dining yaran suka shigo Norah da Aisha suka mata sannu yayinda Farrah ta shige ɗakinta ba tare da ta kula ta ba, Norah da yanzu ta kan ɗan taimaka mata da wani abu ne ta shiga ta taya Farrah wanka yayinda Aisha tayi da kanta suka zo suka fara cin abinci..

Ita dae hidayat Tunanin ta yadda zata fara shiga rayuwar Raed har ta sauya shi take, mutumin da idan tana ganganshi jininta kaman tsinkewa yake, idan taji muryarshi gabanta har faɗuwa yake idan kuwa ya tsura mata waennan idanun nashi masu yanayi da na snake se taji kaman fitsari ze kufce mata shine tayi alkawarin sauyawa! Ta ina zata fara kuma ta yaya?

Bayan sun gama cin abincin ta tattare ta saka Aisha da Norah Alwala suka zo suka yi sallah, bacci suka yi se bayan la'asar suka fara lessons nasu na Qur'ani da ta saba musu.

Bayan sun gama suna zaune a parlorn na sama ya shigo babu sallama, a gajiya yake tilis har layi yake sbd zazzafar wasar da suka yi yau ya haɗu kuma da ƴar damuwar da yake dankare chan kasan ranshi wadda ya kasa cisgewa, da ita suka fara Haɗa idanu Norah tace

"laaaaa dad u didn't say salam"

Ɗan kallon yarinyar yayi cikin rashin fahimta, tana kallon hidayat tace
"Miss hidayat ina kin ce dole ne musulmi yayiwa ɗan uwanshi musulmi sallama idan ze shiga wuri kuma na ciki ma dole ne su amsa?"

Hidayat ba tare da ta kalleshi ba tace
"kwarai kuwa Norah kuma akwai lada a cikin sallama"

Aisha tace
"eh ai kuma idan baka da lada dayawa bazaka shiga aljanna ba"

Norah ta gyaɗa kai, duk be kallesu ba se ita ne ya zubewa gajiyayyun idanunshi yace
"idan mutum ya mance fa?"

Husky musculine Muryarshi ya dake ta, a hankali ta ɗaura idanunta a kanshi cikin kankan da murya tace
"se ya koma da baya yayo in an amsa se ya shigo"

Juyawa yayi ya fice se ya dawo yace
"Assalamu Alaikum"

Duka suka amsa Mishi suna murmurshi..

Norah da Aisha suka ce
"welcome daad"

Kai ya gyaɗa kawai ya shige room ɗinshi, ajiyar zuciya me karfi hidayat ta sauke bata taɓa zaton ze koma ya sake sallama ba, idan ko hakane zata yi anfani da yaran sossai wurin ganin ta sauya shi..

Tana cikin Tunaninta Farrah da ta bishi ɗakin ta fito da gudu tace

"Daadddy is throwing up"

Dukkansu mikewa suka yi Norah tace
"is he sick?"

Hidayat da tunda ta kalleshi take Tunanin wani abun na damunshi ta wuce ɗakin ba tare da Tunanin komai ba.

Duƙe yake gaban washing hand base se amai yake kwararawa a wahalace, a gefen shi ta tsaya tace
"sannu!"

Kai ya gyaɗa mata har ya gama, ruwa ta saka mishi a hannu ya wanke fuskanshi da bakinshi yace

"I wanna take shower"

Fita tayi gabaɗaya a ɗakin taje wurin miss Mary ta sakata kiran family doctor ɗinsu don daga gani dauriya kawai yake, ko da ta dawo a tsaye ta samu Su Norah duk suna cikin damuwa, Norah ta tura ta duba ko ya gama shiryawa ta dawo tace mata ya kwanta ya rufe da blanket yana ta rawar ɗari..

Cikin mintuna likitan ya zo ya hau dubashi nan ya hada allura ya mishi ya ba Paul takarda ya sayo magani, bayan ya fito ya cewa hidayat a tabbatar ya sha tea kan ya hadiye maganin don da yunwa a tare dashi..

Bayan Paul ya dawo ya bata maganin, kitchen ta shiga gabanta na faɗuwa ta Haɗa tea ɗin ta ɗauko ta nufi ɗakin, da sallama ta tura kofan ɗakin...

#Vote
#share
#comment


                      🖤Gureenjoh🖤

KOWA YA GA ZABUWA...Où les histoires vivent. Découvrez maintenant