Shiru Mum tayi zuciyar ta a wuya take tuk'in har suka zo k'ofar gidan su Rauda Mama ta fita daga motar tana kallon gidan ta tabbatar nan ne inda aka binciko mata ta nufi zuwa cikin gidan, juyowa tayi taga Mum bata fito ba ganin tana kallon ta ya saka ta fitowa suka shiga cikin gidan.

K'ofa biyu suka gani suka tsaya suna kallon k'ofar cikin tunanin waccw zasu bi a ciki, bud'e d'aya akayi aka fito hakan ya saka suka kalli wacce ta bud'e k'ofar ta kalle su tace, "Bayin Allah daga ina?" Inna ta fad'a tana kallon su. Mum ta kawar da kanta gefe da alama baza ta bada amsa hakan ya saka Mama tace, "Muna neman wajan su Rauda."

"Gashi nan" ta fad'a tana nuna musu d'aya k'ofar suka wuce ba tare da sun kuma kallon ta ba. Da sallama suka bud'e k'ofar sai gasu a falo Rauda na zaune ita da Umma da kuma Yaya Ummi suka amsa suna kallon su, ido Rauda suka had'a da Mum ta bita da kallo kana tace, "tofa kice shugabar y'an daba ce da kanta ta kuma dawowa, to yau kuma da me kika zo mana...? zauna ki bamu labari" ta fad'a tana kallon Mum cikin sigar rashin mutunci.

         Mama ta zauna ta d'age nikaq d'in fuskar ta ta kalli Umma tace, "Sannu ya jikin?." Umma tace, "lafiya lau Alhamdulillah. Amma ban sanki ba." Mama ta murmusa tace, "Sunana Fulani Rabi'atu mata a wajan sarki katagum ya a wajan sarkin Kano, jika wajan sarkin Kano, uwa a wajan sarkin Katagum mai jiran gado" ta fad'a tana kallon su. Yaya Ummi tace, "Allah sarki! To sannu." Mama ta kalli Rauda tace, "wajan ki nazo." Rauda da mamaki ta kalle ta tace, "gani ai kin ganni."

Mama tazo wuya jin amsar da ta bata amma ta jure tace, "d'ana Asad ya furta kalmar so a gare ki a lokacin da ban shiryawa hakan ba, ya nuna ke yake yi kuma na riga da nayi masa mata tun ba yanzu ba, gidan sarauta gida ne na rikita-rikita kanki bazai d'auki abinda yake faruwa a cikin sa ba koda an baki labari, duk inda kike tunanin abun ya wuce haka gwara ki zauna a gefe hakan zaifi miki alkhairi. Nasan halin mahaifin sa tunda yace amsar ki ake jira ita ake jira indai kika amsa zance ya k'are in kuma kika yi akasin haka za'a fasa shiyasa nazo na shawarce ki akan karki kai kanki ga halaka matsayin da kike k'okarin takawa yafi k'arfin ki akwai mata sosai a gaban ki." Kallon Umma tayi kana tace, "Ke uwa ce baza kiso ki rasa d'iyar ki ba ki bata shawarar kar ta amsa batun Asad domin kuwa tana niyar shiga wuta ne da k'afar ta."

Umma tace, "banda abin ki kinji ance y'ar mu zata auri d'anki ne?." Mama ta tab'e baki tace, "ko d'aya nasan baza tak'i tayin ba ai shiyasa nake fad'a mata gaskiya."
"Ai kuwa sai muce a kai kasuwa domin kuwa tana da wanda yafi Asad d'in" Yaya Ummi ta fad'a tana kallon ta. Kyakykyawan murmushi Mama tayi tace, "tana da daidai ita dai amma bawai wanda yafi Asad ba ko yarinya..? Ta samawa kanta lafiya da kuma zaman lafiya."

Rauda da take gefe tace, "in kuma na amince masa fa?." Mama ta kalle ta tace, "abinda ma bazai yu ba kenan, keda shi sai dai taimako amma yafi k'arfin ya zama mijin ki har Allah ya tashi duniya, Rauda sunan ki ko?" Ta fad'a tana kallon ta cikin k'ask'anci da rainin hankali Rauda tayi dariya tace, "kodai nafi k'arfin sa ba tunda shine yake jiran amsa ta bani nake jiran tasa ba, shi ya gani ya mato yace yana so har kika kasa dakatar dashi kinga kenan nice nafi k'arfin sa bashi yafi k'arfi na ba. Ki rike d'anki daman bana sha'awar auren kuramen maza ni."

"Ke yarinya ki iya bakin ki! Ki san da wacce kike magana" Mum ta fad'a a fusace tana kallon ta Rauda tace, "in kuma nak'i fa akwai abinda za'ayi min ne?." Mama tace, "Naga alama kanki yana rawa sosai kina ji da y'an matanci, ki saita harshen ki tun kafin ya kai ki ya baro ki" ta fad'a tana nuna ta da yatsa. Umma tace, "Rauda ya isa haka." Mama tace, "ya kamata dai kija mata kunne ta san da wacce take magana."
Rauda tace, "Ke kika tako k'afar ki kika zo har inda muke dan haka baki isa ki fad'a mana maganar da batayi mana ba kuma nayi miki shiru ba."

Mama tayi k'wafa tace, "Ba wannan ne a gabana ba abinda na fad'a miki shi ya kamata kiyi, maganar auren Asad ki d'auka a mafarki kika tab'a ji ba a gaske ba" ta fad'a a kausashe. Rauda ta tab'e baki tace, "Umarni ne ko shawara?."
"Umarni ne!" Ta fad'a a fusace tana kallon ta.
"Dalili?" Rauda ta fad'a tana binta da kallon raini. Mama tace, "ke banzo wajan nan dan na fad'a ki fad'a ba, ina so kisan badan Jan kunnen da zan miki ba uban ki ma bai isa na fad'a ya fada ba balle ke y'ar k'aramar tsakuwa. naga alama baza kiji maganar a nutse ba sai an fad'a miki da yaren da talaka yafi ganewa wato duka. Ki samarwa kanki lafiya ki bar Asad in baso kike wani abun ya same ki ba."

KWANTAN ƁAUNAWhere stories live. Discover now